Chapter 58
Chapter 58
lokacin ba wani k'arfi gare shi ba amma saboda wadatar zuci da kuma tausayi irin na sa ya taemaka masa, be tsaya iya nan ba ya taemakawa Abbun sa amma ace abinda Abbun sa yayi kenan? Ya zama dole ya bincika. .. Babu wanda yace uffan a cikin su sanda Yah Sadeeq d'in ya gama bada labarin, Ayrah na taya shi har lokacin tana share k'walla a idanun ta, Abba gaba d'aya bashi da abin cewa shiyasa ma yayi shiru yayin da Umma kuma mamaki gami da takaeci sune suka taru suka mata yawa yasa ta kasa cewa komae, a hankali ta shiga goge hawayen dake ta saukowa daga kan fuskar ta tana girgiza kae, se yanzu ta sake gane kuskuren da suka aekata na yankewa Ayrahn hukunci ba tare da sun yi bincike ba, hannu Umma ta mik'awa Ayrah bayan ta d'aga fuskar ta ta kalle ta, sannan ta mata alama da ta taho da kan ta, babu 6ata lokaci Ayrah ta k'arasa da sauri ta fad'a jikin Umman tana sakin wani irin kuka, itama Umma bata hana kan ta kukan ba ta rungume d'iyar ta ta sosae tana jin yadda ilahirin jikin Ayrahn ke rawa "Kiyi hak'uri Ayrah, don Allah ki yafe min, nice na fara d'arsawa Abban ku zargin guduwa kikayi daga gidan nan bayan tabbatar da ba zamu aura miki Raj ba, kiyi min afuwa Ayrah!" ta k'arasa fad'a tana sake jin wani irin takaeci, se da Ayrah ta sauke sheshshek'a sannan tace "Umma ni ba abinda kuka min, wannan dalilin ne ma yasa nake ta sauri in dawo gida dan nasan za'a iya tunanin hakan, Umma ba kuyi laefi ba dan kun yi tunanin hakan musamman daya kasance a washe garin ranar da kuka hanani auren sa ne kuka neme ni kuka rasa.. Umma ni baku min komae ba, nice ma zan baku hak'uri.." "Kuull..ki bar fad'in mu miki hak'uri Auta, babu abinda kika mana mu ma" Umma ta fad'a tana sakin Ayrahn, bata sake cewa komae ba se k'arasawa da tayi inda Abba ke zaune har lokacin, tsugunawa tayi tana kallan sa, dae_dae lokacin daya d'auke kae yana jin zuciyar sa na karyewa "Abba..!" ta fad'a har lokacin tana kallan sa "Ayrah je ki huta bazan iya cewa komae ba, kiyi hak'uri kawae.." Abban ya fad'a, wani irin sanyi taji yana ratsa kafatanin jikin ta, ko ba komae yau d'in gata ga iyayen ta kuma da alama sun yafe mata, gashi ma har neman yafiyar ta suke yi "Abba ni zan nemi yafiyar ku don Allah.." Abba be iya cewa komae ba se girgiza kae kawae da yake yana ajje numfashi a hankali, Yah Sadeeq kuwa da yake gefe murmushi ne kawae ke fita daga kan fuskar sa, tana shirin mik'ewa dan komawa d'aki Abba ya juyo kamar wanda ya tuna wani abu "Ayrah!" seta juyo a hankali tace "Na'am Abba.." "Kin san mutumin daya saka aka d'auke ki?" tsayawa tayi tayi shiru tana hasaso fuskar Alhaji Mato, kwata kwata ba zata iya cewa ga fuskar sa ba dan haka ta girgiza kae kamin tace "A'ah Abba bansan shi ba.." "Idan kika gan shi zaki gane shi?" shiru tayi tana nazari, ko da ta san shi ma bata tunanin zata iya gane shi ballantana bata san shi ba dan haka a nutse ta furta "A'ah Abba.." "Tashi kije Allah yayi miki albarka" lumshe idanu tayi kamin ta mik'e tare suka wuce cikin d'akin ta ita da Umma, shiru Abba yayi bayan barin su wajen yana nazari, ya zama dole ya gano mutumin daya d'auke masa yarinya ya kae ta wani waje dan a d'aura musu aure, idan kuma ya tuna da maganar auren Raj dake kan er tasa se ya sake jin jikin sa yayi sanyi, a yanzu be san wanene Raj d'in ba be san ko halin su d'aya da mahaefin sa ba, be san yadda za'ayi su kasance sirikae tsakanin sa da Kabeeru ba, abinda be ta6a tunanin ze kasance a rayuwar su ba, abinda ya guda tun farko, se dae gashi Allah yayi ikon sa akan su ta hanyar da basu ta6a zata ba, seya koma ya jingina bayan sa da jikin bango yana cigaba da sak'a da warwara. ... Da sallama ya shigo cikin d'akin hannun sa d'auke da envelope, Mummy dake zaune kan kujera ta mik'e tana fad'in "Alhaji sannu da zuwa" "Yawwah sannu kadae, ina Muneerahn? Na gan ki ke d'aya?" murmushi Umma tayi sannan tace "Toh Alhaji ae dole ka ganni ni d'aya a kwanakin nan, kasan sha'anin amarya fa yanzu haka tana wajen gyaran jiki" "Toh madallah, ga kati dae ya iso" ya fad'a yana mik'a mata envelope d'in hannun sa, da sauri ta sanya hannu ta kar6a da murmushi kan fuskar ta take fad'in "Kae toh Masha Allah.." ta fad'a tana k'arasawa ta zauna kan kujera ta fara fito da katinan masu kyau da k'ayatarwa, girgiza kae Daddy yayi yana murmushi ganin yadda Mummyn ta shagala da kallan kati, ko bi ta kansa ba tayi ba hakan ne ya sanya shi jan k'afafun sa ya bar d'akin. Be dad'e da fita ba Muneerah ta shigo cikin d'akin cikin hijab har k'asa hannun ta d'auke da jaka da had'ad'd'iyar wayar ta, k'arasawa tayi da sauri kan kujerar tana kallan Mummy kamin ta saka hannu ta tu6e hijab d'in jikin ta, nan take shigar dake jikin ta ta bayyana, gajeran wando tiet ne a jikin ta da vest irin me bin jikin nan hakan ne ya bayyana yanda ta cika daga sama ba kamar da ba wanda ke nuni da siyo shi ba natural bane, haka zalika hips d'in ta ma sun k'aru ba kamar da ba dake kamar 1, kan ta babu d'an kwali se dae kamar ko yaushe a kitse yake da kitson attachment daya zuba a gadon bayan ta, ta k'ara wani irin mahaukacin fari bauu, fatar nan ta sake d'ashewa, da alama ba mae ta shafa ba se dae ko k'waya ko kuma allura "Kin dawo?" "Ehh Mummy, na gaji wallahi" "Toh sannun ki, gashi nan kati ya iso" farr tayi da idanun ta kafin ta kalli katinan, seta saka hannu ta d'auki guda d'aya ta kalla ta shiga karantawa, sunan ta ne gashi nan ya fito 6aro 6aro dana Rk, wani murmushi ya k'wace mata tana jin ita kam burin ta ya gama cika daga lokacin data auri Rk d'in, ajiye katin tayi seta d'auki wayar data ajje a gefen ta kamar koda yaushe ta danno number sa, amsar d'aya ce dae kamar kullum baya kusa, bata gaji ba ta sake kira amma har ta katse be d'aga ba, a karo na 3 ta sake gwada kiran na sa cikin sa'a kuwa ya d'aga wayar se dae bece komae ba, daga inda take ta maraeraece fuska kamar za tayi kuka "Haba Baby, ina ta kiran ka amma kak'i d'agawa, na maka magana ta whatsApp kak'i kula ni, ya kake so nayi? Auren mu saura kwanaki amma kak'i tsayawa muyi magana ko da akan shirye_shiryen bikin ne" tsaki ya saki akan la66an sa, ya kasa gane wannan dalilin na had'a auren sa da Muneerah, idan so suke zumuncin su ya d'ore ae ba dole seta hakan zasu biyo ba, shi abinda ma yake
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70