Chapter 42
Chapter 42
ta6a ganin Ayrah ta fita babu izinin wani a cikin mu? Abban su yau nayi nadama.." "Ya isa haka Ruk'ayyah" Abba ya fad'a yana d'aga mata hannu "Bar ta taje, in dae bijirewa umarnin iyaye ne taje gata ga duniyar, kada muyi mata baki saboda ni uba ne ke kuma uwa ce kada ya kama ta, amma ni kae na yau Ayrah ta wulak'antani a rayuwa.." kallan su kawae Yah Sadeeq yake yi ya kasa cewa komae, ya kasa koda bud'e bakin sa ne ya furta wani abu, dan maganar ta shige shi, bashi da bakin da ze iya k'arya ta wannan maganar ko kuma ya musa, toh idan ya musa d'in mene hujjar sa ta yin hakan? Meze kawo a matsayin hujjar sa? Amma meyasa Ayrah zata yi haka? Meyasa zata za6i d'a namiji akan iyayen su? Iyayen da suka d'auke ta tun ciki har tazo duniya suna d'awaeniya da ita har kawo yanzun basu gaji ba? Duk wani tunanin su akan ta ne, duk wani burin su akan ta, meyasa zata saka musu ta hanyar za6ar wanda ta had'u dashi rana tsaka a rayuwar ta? Ta fifita d'a namiji akan su??. ... Yana cikin motar har lokacin idanun sa na kan gidan yana tunanin yadda zeyi ya shiga cikin gidan, idan ya tuna maza ne har biyu suka d'auki Ayrahn suka shigar da ita cikin gida se yaji wani sabon tuk'uk'i da kuma wani zafi na cigaba da azalzalar sa cikin zuciya, seya bud'e murfin motar a hankali ya zuro k'afar sa dake cikin wani had'ad'd'en takalmi hannun sa akan goshin sa yana d'an murzawa, daga ganin mutanen da suka d'auke ta kasan sanya su akayi, kuma gidan da suka kawo ta babu alamar akwae mutum a ciki, kenan idan haka ne ogan nasu ze zo kuma ze nemi a bud'e masa k'ofar dan shiga gidan "Exactly" ya fad'a yana sake bud'e idanun sa, seda ya fesar da wata zazzafar iska daga bakin sa sannan ya cigaba da zama cikin motar har lokacin gaba d'aya hankalin sa na kan gidan gefe guda kuma yana jiran yaga ta inda wani ze 6ullo. ... Zubewa yayi a gaban me garin yana d'aga hannun sa alamar girmamawa "Allah ya taemake ka yalla6ae" wani matashi da zeyi 25 years ya fad'a kan sa a k'asa, me garin bece komae ba ya cigaba da kallan Mubarak yana jiran jin abinda ze fad'a "Yalla6ae acan gidan Alhaji Mato naga wasu bak'in fuska sun shiga gidan, ban ta6a ganin su ba kuma naga kamar basu da gaskiya" Mubarak ya fad'a har lokacin kan sa na a k'asa, seda me gari ya d'an numfasa sannan yace "Gidan Alhaji Mato?" Me gari ya fad'a, Mubarak ya sake jinjina kae kana yace "K'warae kuwa yalla6ae nima nayi mamaki" d'an shiru Me garin yayi sannan yace "Aje a zo min dasu" ya fad'a a nutse "An gama ranka ya dad'e" Mubarak ya fad'a yana mik'ewa ya bar wajen. ... Suna zaune a tsakar gidan Muttala ya kalli wanda suke tare yace "Kodae mu fito da ita, kada zafi ya mata illah" "A'ah mu k'yale ta, mu dae ba aekin da aka saka mu ba kenan? Ina ruwan mu? Gwara kawae mu jira yazo shi yasan yadda za'ayi da ita" jinjina kae Muttala yayi kana yace "Hakane kuma" babu wanda ya k'ara cewa komae a cikin su har zuwa sanda suka ji ana knocking k'ofar, da mamaki dukan su suka yi shiru suna saurarar knocking d'in sa ake dan tabbatarwa "Wallahi da gaske k'wank'wasawa akeyi, waye kenan?" "Ko dae Alhajin ne ya iso?" mutumin ya tambaya yana kallan Muttala, girgiza kae Muttala yayi kafin yace "No bana tunanin haka gaskiya, idan shine ae akwae mukulli a hannun sa" Muttala yayi maganar yana mik'ewa a hankali ya k'arasa dab da gate d'in sannan yace "Wanene?" Mubarak ne yace "Daga gidan Me gari ne, me gidan yana nan?" se Muttala ya sauke ajiyar zuciya sannan yace "A'ah be iso ba tukun" "Toh Me gari na neman ku" Mubarak ya sake fad'a, kallan juna Muttala suka yi shida mutumin nan sannan Muttala ya d'aga kafad'a kafin a hankali ya furta "Babu wata matsala fa" jin abinda ya fad'a ne ya sanya mutumin k'arasawa ya bud'e gate d'in sannan suka fara k'ok'arin fitowa daga cikin gidan "Ku kad'ae ne a cikin gidan?" Mubarak ya sake tambaya, mutumin nan na shirin cewa "Ehh" Muttala ya girgiza kae da sauri kana yace "A'ah akwae matar Oga amma bacci take" "A taso ta itama ta fito, Me gari ke neman ku ku duka" had'iye yawu Muttala yayi kana ya koma cikin gidan ya k'arasa ya bud'e motar cikin tunanin yadda za'ayi ta farka saboda abinda suka shak'a mata, cikin sa'a seya hango wani ruwa wanda d'azun ya sha ya ajje ragowar, da sauri ya janyo kana ya bud'e ya fara zuba mata a fuska, seda ya kusa juye mata ruwan sannan ta fara bud'e dara daran idanun ta da suka sake komawa ciki saboda wahala, a hankali ta dinga bud'e su har ta gama ware su tarr cikin motar, idanun ta suka sauka akan Muttala, da sauri ta mik'e ta fara komawa baya tana shirin sakin k'ara Muttala ya girgiza mata kae da sauri yana d'ora hannun sa akan bakin sa sannan yace a hankali ganin yadda ta gama rikicewa gaba d'aya "Kada kice komae, kiyi shiru taemakon ki zan yi" yayi maganar har lokacin yana kallan ta, cigaba da girgiza kae tayi hannun ta d'ore akan bakin ta hawaye se sintiri suke akan fuskar ta "Ki dena kukan taemakon ki zan yi fa" ya sake fad'a ganin kamar bata ji abinda ya fad'a da farko ba "Kiyi shiru kada ki nuna a tsorace kike kin ji, ko me kuma za'a ce miki kada kice komae, komae kika ji an fad'a ke dae ki bisu a haka" ya fad'a a nutse dan gudun kada ta tona musu asiri a gaban jama'a, haka kawae taji tayi na'am da zancen mutumin dan haka seta jinjina kae sannan yace "Fito muje" babu musu ta sanya k'afa ta fito se dae har lokacin k'irjin ta be bar bugawa ba haka zalika tana mamakin ko nan d'in ina ne? Waye ya kawo ta? Yaushe suka zo? Ya akayi suka zo nan d'in? Su waye su? Meyasa suka kawo ta nan d'in? Amma koma dae menene tunda wannan mutumin ze taemaka mata bari ta zubawa sarautar Allah ido, seta sake bud'e idanun ta tana kallan gidan sanda Muttala ke fad'in "Yawwah ga ta" Mubarak ya kalle ta sannan yace "Toh ku wuce muje" babu musu duka suka fito daga gidan sannan suka kulle, tafiya take a hankali kamar wata mara laka tana cigaba da kallan garin da be mata kama da birni ba, ji take kamar ta saka kuka amma idan ta tuna abinda mutumin ya fad'a seta d'an lumshe idanun ta ta had'iye hawayen. Tunda suka fito idanun sa ke kan su, seya saki wata k'atuwar ajiyar sanda ya hange ta ta fito daga cikin gidan tana tafiya cikin k'oshin lafiya "Thank god" ya fad'a yana fitowa daga cikin motar gaba d'aya, seda suka kusa zuwa gidan Me garin yana hango su sannan yabi bayan su cike da tunanin inda zasu je
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70