Skip to content

Chapter 52

Chapter 52

Zazzafar Kauna Book One Complete Hausa Novels 1,207 words 0 views Progress saved
Download Book

masa kyau akan fuskar sa "Lafiya k'alau Alhamdulillah, da alama dae wannan ce sirikar tamu?" ta fad'a tana kallan Ayrahn, da kallan farko ta mata ta hango zallar kyan da take dashi, wani kallo Ayrah ta d'aga narkakkun idanun ta ta watsawa Hameeda, ita kan ta Hameedan seta gaza gane wane irin kallo ne wannan? Murmushin yak'e yayi dan baya so su sake 6allo masa wani aekin yace yana mik'ewa "Amm Madam.. Pls ga sister nan zata d'an yi wanka ta shirya pls, zuwa anjima zan zo na d'auke ta" duka kallan sa suke yi cike da mamaki, Yaseer yayi k'arfin halin fad'in "Bangane ba?" lumshe idanun sa yayi yana fesar da iska daga bakin sa sannan ya bud'e idanun nasa yana kallan Yaseer yace "Plsss idan na dawo zamu yi maganar, Abbu na jira na" ya fad'a yana fara yin gaba, mik'ewa tayi itama dae_dae lokacin da hawayen da suka dad'e cikin idanun ta suka samu damar zubowa akan fuskar ta, lura da hakan ya sanya shi d'an dakatawa kana yace a hankali yana kallan ta "Ki shirya, ina dawowa se mu wuce.." ya fad'a cikin taushi, ita dae ba tace komae ba se sake share hawayen da tayi yayin da shi kuma ya fice daga d'akin cike da fatan kada ta tubure masa, Yaseer da Hameeda suka kalli junan su cike da mamakin wannan abu, sauke numfashi Yaseer yayi kana yabi bayan Rk daya fita "Malam nifa bangane abinda kake nufi ba, ya zaka tafi kuma ka barmu cikin duhu? Ka fara warware mana wacece waccan d'in kafin ka bar gidan nan" numfashi ya sake fesarwa daga bakin sa sannan yace "Sorry Friend, zance ne me tsayi amma ina gamawa da Abbu nan zan dawo pls" yayi maganar sanda ya bud'e murfin driver seat "Shikenan karka d'au lokaci pls" "In Sha Allah" Rk ya fad'a yana shigewa cikin motar "Ammm pls kada a barta taje ko'ina kamin na dawo" Rk ya fad'a yana kallan Yaseer, yanzu kam kan Yaseer ya sake kullewa da al'amarin abokin nasa, dan haka bece komae ba ya bishi da kallo kawae, shi kuma Rk tunda yasan Yaseer d'in yaji abinda ya fad'a d'in ya sanya shi jan motar, bin sa da kallo Yaseer ya sake yi har ya fice daga cikin layin sannan ya sauke ajiyar zuciya yana komawa cikin gidan, "lallae akwae wani abun" ya fad'a a k'asan ran sa. ... Kae tsaye gida ya wuce zuciyar sa cike da sak'e_sak'e kala_kala, ya k'arasa yayi parking motar sa sannan ya fita ya shige cikin gidan, parlourn Abbu ya wuce da sallama d'auke a bakin sa ya shiga, Abbun na zaune akan kujera yana shan lemo gefe guda kuma yana kallo cikin k'atuwar T.Vn dake manne a jikin bango, seda ya d'auki remote ya rage volume d'in T.Vn sannan ya amsa sallamar Rk daya k'arasa shigowa cikin d'akin, murmushi ne ya su6uce akan fuskar Abbu sanda Rk yace "Barka da wannan lokacin Abbu" "Barka dae likita ya kamata ka samu bacci haka nan" jinjina kae Rk yayi yana yin d'an murmushin kana yace "In Sha Allah Abbu" gyara zama Abbu yayi daga inda yake zaune sannan yace bayan yayi gyaran murya "Wato maganar da nake so nayi da kae ita kan ta tana buk'atar nutsuwa, dan haka da zarar ka gama samun baccin da baka samu ba seka fara shirye_shirye saboda rashin ishashshen lokaci" Abbu ya fad'a yana d'an dakatawa, duk da Rk be fahimci maganar Abbun ba amma hakan be sanya shi cewa komae ba, yayi shiru yana cigaba da saurarar Abbun dan yasan ze warware masa komae ne "Dama magana ce akan auren ka da Muneerah da za'a gabatar dashi nan da sati d'aya" Mhiz Innocent.....✍️ https://chat.whatsapp.com/DH0EIIWNPnSICxsGgh2DSd *CHAPTER TWO* *♡☆ZAZZAFAR KAUNA☆♡* *FREE BOOK* Page 034 ___Seda ya d'au wajen minti 1 bece komae ba yana ta kokawa da zuciyar sa akan zafin da take masa kada kuma 6acin rae yasa ya furta abinda be dace ba sannan a hankali ya d'aga idanun sa da suka sauya kala ya kalli Abbu "Abbu aure ka nemar min hadda tsaeda rana ba tare da sani na ba?" ya fad'a ba tare dama yana sanin abinda ke fita daga bakin sa ba saboda tsananin 6acin rae, da mamaki Abbu ya kalle shi na tsawon sakanni, sosae yayi mamakin jin abinda ke fitowa daga bakin Rk d'in amma seya sake gyara zama sannan yace har lokacin yana kallan sa "Toh ko ban isa bane?" se a lokacin Rk ya tuna abinda ya fad'a d'in a hankali ya d'an lumshe idanun sa sannan ya bud'e a nutse kuma a hankali ya furta "Abbu ka isa.." daga haka ya mik'e cike da sassarfa ya fice daga d'akin, bin sa da kallo Abbu yayi har zuwa lokacin daya gama ficewa daga d'akin sannan ya dawo da duban sa cikin d'akin yana jinjina kae. ... A hankali ya nemi waje ya zauna akan gadon sa idanun sa a lumshe, a karo na barkatae ya sake fidda iska daga bakin sa, hannu ya kae ya dafe kan sa daya cigaba da sara masa, ya kae wajen minti 5 a hakan yana sauke numfashi a jere a jere saboda yanda zuciyar sa ke cigaba da tafasa sannan ya mik'e kamar me tunanin wani abun se kuma ya koma ya zauna, tabbas Abbu na neman sakawa zuciyar sa ta buga, ta yaya ze iya kallan wata matar a matsayin matar sa bayan Ayrah? Be san ta yaya hakan ze kasance ba, son da yakewa Ayrah yana da yawa baya tunanin ko da ya auri wata ze iya adalci a tsakanin ku, toh ta yaya ma ze auri wata? Koda be auri Ayrah ba baya tunanin ze iya auren wata matar ballantana kuma yanzun daya same ta, se dae ga Abbu na neman saka shi auren wata bayan ita, baya so kuma ya d'auki zunubi akan hakan, amma ta yaya ze kalli Abbun ya fad'a masa baya son Muneerah saboda yana da wata matar daya aura ba tare da sanin su ba? Hannun sa ya kae ya cusa cikin kwantacciyar sumar kan sa nan take kuwa ta hargitse seya koma ya kwanta kawae cikin rashin sanin abinyi. ... A 6angaren Ayrah kuwa sanda Rk ya fita daga cikin d'akin seta cigaba kawae da kallan k'ofar kamar me tunani "Muje na kae ki d'akin koh?" Hameedah ta fad'a tana murmushi, kamar ta mata banza se kuma taga gwara kawae ayi komae a yanzu a gama a wuce wajen, dan haka se kawae tayi gaba ta fara tafiya a hankali, Hameedahn seta wuce ta ta k'arasa zuwa bakin wani d'aki tace tana kallan ta "Ki shiga kiyi wankan zan kawo miki kaya seki saka" se a lokacin ta iya bud'e baki tace "Toh" sannan ta shige cikin d'akin, madaedaecin d'aki ne me d'auke da gado, wardrobe da kuma toilet, bata tsaya tabi ta kan d'akin ba kawae ta fad'a toilet d'in, anan d'in ma ba wani dad'ewa tayi ba dan haka ko minti 15 ba tayi ba ta fito sanye da hijab d'in, se a lokacin ta tsaya tana k'arewa d'akin kallo kafin ta d'auke kan ta ta maeda shi zuwa k'ofar d'akin da aka turo, Hameedah ce ta shigo yanzu hannun ta d'auke da riga

Table of Contents

Chapters

70 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70