Chapter 63
Chapter 63
hankali, kae tsaye ta ta6a k'ofar fita se ta ji ta a rufe, dan haka ba tare data kalle shi ba ta furta "Ka bud'e min na fita" shiru yayi yana bin ta da kallo duk da baya iya hangen fuskar ta "Don Allah ki tsaya ki saurare ni" kamar jira take seta juyo tana kallan sa, kafin ta fara magana fuskar nan ta ta tayi jajur haka zalika sassanyar muryar ta ta sake rusuna "Babu abinda zaka fad'a min Raj, ka bud'e min na koma gidan mu, kaje kayi rayuwa da wadda kake so nima yanzu bana son ka.." ta fad'a tana jin wani irin zafi da bata ta6a jin sa ba cikin zuciyar ta, zazzafar iska ya fesar daga bakin sa kana ya d'an lumshe idanun sa yace "Ayrah, wallahi Abbu ne ya aura min ita, akwae maganar auren dama tun kafin sake had'uwar mu, don Allah kiyi shiru ki dena wannan kukan wallahi yana nakasta min zuciya" hannu ta saka ta toshe kunnuwan ta, tana ji a ran ta kamar wad'annan d'in kalaman yaudara ne kawae yake fad'a mata, meyasa zeyi mata haka? Meyasa ta yadda dashi shi kuma yaci amanar ta? Meyasa ze had'a ta da wata bayan ita tunda take bata ta6a had'a shi da wani ba, tana cigaba da tare sabon kukan daya taho mata ta furta "Ni ka bud'e min k'ofa na fita.." yanzu kam babu musu ya bud'e mata k'ofar, da sauri ta saka hannu ta bud'e murfin motar sannan ta fad'a cikin gidan nasu, a tsakar gida ta taradda Umma babu 6ata lokaci ta fad'a jikin Umman tana sake sakin wani sabon kukan "Subhanallahi Ayrah.. Meya faru?" Umma ta fad'a tana rik'o Ayrahn dake cigaba da kuka kamar wadda akama mutuwa, bata iya cewa komae ba saboda yanda zuciyar ta ke cigaba da tafasa, haushi da kuma takaeci suna sake cika ta, seda ta gama kukan tsaf sannan ta d'ago tana kallan Umma da zuwa lokacin ta gama rud'ewa da yanda taga d'iyar ta ta na kuka haka "Umma wae aure yaje yayi! Umma ya yaudare ni bansan yadda zanyi ba zuciya ta na dab da bugawa" ta fad'a tama manta Umman ta take fad'awa maganar, da mamaki Umma take kallan Ayrahn kafin cikin k'arfin hali ta furta "Ay..." sallamar da Abba yayi cikin gidan itace ta katsewa Umma maganar da take k'ok'arin fad'a, seta d'aga kae ta kalli Abban, ga mamakin ta seta gan shi sun shigo tare da Rk, maganar sa da Ayrah ta jiyo ne ya sanya ta shirin mik'ewa a fusace tana shirin shigewa cikin d'aki Umma ta rik'o ta "Ki tsaya tukunnah" ba dan taso ba haka ta zauna d'in har lokacin kan ta na kan cinyar Umma kuma har zuwa lokacin zafin da zuciyar ta ke mata be ragu ba, haka zalika ji take kamar tayi ta kukan kar ta dena, sam bata san kuma meya shigo dashi cikin gidan ba, me yake nufin zece mata ta yadda dashi? "Ina jin ka Allah yasa lafiya" Abba ya fad'a bayan ya zauna akan tabarmar dake shimfid'e a tsakar gidan, seda ya d'an yi shiru kad'an kana ya saci kallan inda Ayrah ke zaune sannan yace "Abba dama akan maganar aure ne da nayi yau d'in nan, naso na yiwa Ayrah bayani se dae tak'i fahimta ta, Abbu be san da maganar aure na da ita ba shiyasa, kuma dama tun farko yana da burin aura min ita kasancewar er k'anin sa ce, se kuma yanzu Allah yayi za'a yi auren amma sam bani da laefi Abba" ya k'are maganar a maraeraece dan yana da tabbacin Ayrahn na jin sa, ajiye numfashi Abba yayi sannan yace "Ikon Allah, dama namiji ba dan mace d'aya akayi shi ba, kuma hakan ya sake nuna min kae d'in yaro ne me biyayya, dan haka ka tashi kaje Allah yayi maka albarka.. Ke kuma Ayrah ki tashi ki bi mijin ki dan banga amfanin zaman naki cikin gida bayan da auren ki ba" ya k'are maganar yana kallan Ayrah, da sauri ta d'aga narkakkun idanun ta ta sauke su kan Abban da yayi magana, ita kan ta Umma tayi mamakin maganar Abban, amma shi kam da yayi maganar da alama ko a jikin sa "Abban su.." Umma ta fad'a tana cigaba da kallan sa "Babu damuwa, ta tashi ta bishi d'in" shine abinda Abban ya sake fad'a, ajiyar zuciya Umma ta sauke sannan ta kalli Ayrah dake girgiza kae kamar k'adangaruwa cikin kuka tace "Abba don Allah ka bar ni a gidan nan kaaji" dama saboda hakan Abban yace tabi mijin ta, dan kuwa yasan idan ba yanzun ba nan gaba ma se gwagwarmayar tafi hakan dan haka ya kalle ta yace "Babu komae kinji, ki tashi kije.. Zamu yi komae daga baya" ita sam ba fahimtar Abban take yi ba dan kuwa kishi ya riga ya gama rufe mata ido, duk kuwa da irin bayanin da yayi ita har yanzun bata gamsu ba, kawae ji take yi kamar yaudarar ta yayi. Umma ce ta mik'e ta fad'a cikin d'aki ta shiga had'awa Autar ta ta kayan da tasan zata yi amfani dasu ko kuma ta buk'ata kafin komae ya daedaeta sannan ta fito har ran ta tana jin babu dad'i, a yadda ta bar ta a tsakar gidan a haka ta same ta, zaune ta d'ora kan ta akan k'afar ta tana sheshshek'ar kuka, seda ta fito d'in sannan Abba ya kalli Rk "Ku tashi kuje Allah yayi muku albarka, In Sha Allah zan neme ka ko ta layin Sadeeq ne" sosae yaji dad'in abinda Abban yayi dan haka yace "Nagode sosae Abba, Allah ya k'ara girma" "Ameen" d'ago da fuskar Ayrah Umma tayi tana kallan yanda fuskar ta tayi kace_kace da hawaye, seta girgiza kae tana jin tun yanzu har kewa ta fara kama ta "Kukan ya isa haka Ayrah, ki tashi kije zamu yi waya Uhmm?" Umma ta fad'a cikin rarrashi, tausayin Ayrahn na kamata yanda take yarinya da ita amma yanzu haka tana da kishiya wadda za'a kira da Amaryar mijin ta, d'aga ido tayi ta kalli Umma, tana shirin fara magana Umma ta girgiza kae tana murmushin yak'e "Ya isa haka ki tashi ki je kin ji?" sam bata so wani 6acin ran ya sake shiga tsakanin ta da iyayen nata dan haka ta mik'e tana jin jiri na d'ibar ta "Allah ya tsare Auta" shine abinda Abba ya fad'a sanda take shirin gifta inda yake zaune, bata iya amsawa ba dan ita kad'ae tasan yadda take ji a cikin zuciyar ta, shine ya d'auki kayan sannan yayi gaba ita kuma ta rufa masa baya, suna fita kuwa Umma ta mik'e da sauri ta shige cikin d'aki saboda kukan da taji ya taho mata, bin ta da kallo Abba yayi sannan ya dawo da kallan sa tsakar gidan da murmushi kan fuskar sa gami da girgiza kae. A hankali take takawa kamar mara laka zuwa wajen motar tasa, shi ya saka hannu ya bud'e mata, yanzu kam babu musu ta shiga sannan ya zagaya driver seat ya shiga ya zauna, kallan ta yayi yanda yaga tana ta curewa waje d'aya kamar me jin sanyi lokaci d'aya kuma tana matsar k'walla, lumshe idanun sa yayi a ran
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70