Skip to content

Chapter 69

Chapter 69

Zazzafar Kauna Book One Complete Hausa Novels 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

k'arfe 10 ya isa Hotel d'in yayi parking motar sa sannan ya sauka kae tsaye ya wuce d'akin, a nutse ya saka mukullin hannun sa ya bud'e sannan ya tura k'ofar d'akin kana ya tura jikin sa cikin d'akin, acan tsakiyar gadon ya hango ta ta lullu6e jikin ta da bargo kan ta akan gwuiwar ta tayi shiru idanun ta akan k'ofar, ganin sa da tayi ya sanya zuciyar ta saurin karyewa bata san sanda wasu hawaye masu d'umi suka fara sintiri akan kuncin ta ba lokaci d'aya kuma tana cusa kan ta cikin k'afafun ta, runtse idanun sa yayi yana jin wani irin tausayin ta na ratsa shi, cike da sassarfa ya k'arasa cikin d'akin, kae tsaye ya haye kan gadon beyi wata wata ba ya jata cikin jikin sa yayi mata wata kyakykyawar runguma, dae_dae lokacin data fashe da kuka kenan me cin rae tana sake jin wani irin rauni a tare da ita, sake rungume ta yayi yana jin yadda bugun zuciyar ta ke fita da sauri da sauri, a hankali ya d'ora kan sa akan ta dake kan k'irjin sa sannan ya shiga shafa bayan ta a hankali lokaci d'aya wani tausayin ta na sake lullu6e shi, sosae take yin kuka wanda ke fita tun daga k'asan zuciyar ta, shi kuma be hana ta ba se dae har lokacin be dena shafa bayan nata ba, a hankali cikin rarrashi ya furta sanda ya kae bakin sa cikin kunnen ta "Kukan ya isa haka plsss.." ya k'arasa yana jan k'arshen maganar tare da hura mata iska a cikin kunnen na ta lokaci d'aya kuma yana sake shigar da ita cikin jikin sa, a hankali ta shiga rage sautin kukan na ta, har zuwa sanda ta koma sauke ajiyar zuciya, se a lokacin ya saki k'atuwar ajiyar zuciya sannan yace a hankali "Am sorry, am deeply sorry pls.." ba tace komae ba har lokacin kuma be sake ta ba dan sosae yake jin nutsuwa da take cikin jikin na sa "Plss Babe.." ya sake fad'a nan ma dae a hankali kamar me rad'a, kamar jira take suma kuma hawayen kamar jira suke se suka zubo kan fuskar ta sannan ta fara maganar cikin raunanniyar murya "Don Allah kada ka sake tafiya ka bar ni anan kaaji?" tausayin ta ne ya sake kama shi, shi kan sa baya son barin ta amma babu yadda zeyi dole se dae ya raba kwanan ko da d'ad'd'aya ne, yau idan ya kwana anan gobe ya kwana acan "Toh In Sha Allah" ya fad'a sannan ya d'ora da "Nan d'in ne bakya so?" "Tsoro nake ji ni dae, bana son nan gaba d'aya" tayi maganar tana k'ok'arin tashi daga jikin na sa, kamar kada ya sake ta amma seya sake ta d'in a hankali, se kuma a lokacin ya fahimci yanda ilahirin jikin sa yayi wani mugun sanyi, wata iriyar kasala ta gama rufe shi kamar kada ya motsa daga inda yake "Shikenan.. Zan fita na samo gidan da zamu zauna kafin komae ya daedaeta.." da sauri ta d'aga narkakkun idanun ta ta kalle shi jin da tayi yayi zancen fita, ya fahimci abinda ya sanya ta kallan na sa ba tare da ta shirya ba dan haka ya d'an yi murmushi kana yace "Kar ki damu da rana zan fita, dama Abbu na nema na, sena biya ta wajen su Abba ma mu gaesa" "Don Allah zan bi ka.." ta fad'a da sauri bayan ta rik'o hannun sa, hannun nasu yabi da kallo saboda yanda ya sake jin tsigar jikin sa ta tashi, ganin inda yake kalla ya sanya itama ta kalla, da sauri ta saki hannun nasa tana tura k'aramin cute lips d'in ta, nan ma seya sake bin bakin nata da kallo lokaci d'aya yana lumshe lumsassun idanun sa, ya kae wajen second 30 a haka sannan ya bud'e yana kokawa da zuciyar sa yace "Muje kici abinci" "Na ci kafin ka shigo!" ta fad'a ba tare da ta kalle shi ba "Kin ci?" ya fad'a yana kallan ta sosae, seta jinjina kae kawae tana sake kaucewa kallan daya ke bin ta da shi, jin bece komae ba ya sanya ta sake fad'in "Allah kuwa kuma ka duba ka gani idan ban ci ba" ta fad'a tana nuna masa abincin da ke ajje, seda yabi wajen da kallo sannan ya dawo da duban sa kan ta yace "Matso kiyi bacci kafin na dawo.." yayi maganar yana kishingid'a akan gadon lokaci d'aya yana mik'a mata hannun sa d'aya, tura bakin ta gaba tayi kafin tace "A'ah.." ta fad'a tana d'ora kan ta akan kafad'ar ta, tilas abinda tayi d'in ya sanya shi lumshe idanun sa yana sakin murmushi, hannun sa ya kae kawae ya janyo ta se gata cikin jikin sa, ya gyara kwanciyar sa sannan itama ya gyara mata ta ta kwanciyar cikin jikin sa duk da yanda take ta neman k'wacewa daga jikin nasa, wanda hakan ya bawa ma6allan rigar jikin sa na sama damar 6allewa, hakan ne ya bawa kyakykyawar farar fatar sa me d'auke da bak'a sid'ik d'in gargasa bayyana, ba tare daya lura ba ya sake manna ta da k'irjin sa, hakan ne ya bawa kan ta damar kwanciya akan zallahr fatar sa dake ta tashin wani sassanyan k'amshi, k'atuwar ajiyar zuciya ya sauke sanda hakan ya faru, ya lumshe idanun sa bugun zuciyar sa na k'aruwa "Kiyi bacci" yayi k'ok'arin lalubo kalmomin biyu ya had'a ya fad'e su, ita kan ta sosae zuciyar ta ke bugawa musamman ma jikin ta dake ta rawa kamar mazari, amma duk da haka be sake ta ba, ganin bashi da alamar sakin ta ne ya sanya ta hak'ura ta runtse idanun ta tana jiran zuwan bacci, cikin ikon Allah kuma babu dad'ewa baccin ya d'auke ta seta koma tana sauke numfashi akan k'irjin sa, wanda hakan ya sanya shi saurin lumshe idanu gami da janye ta daga jikin sa a hankali yana jin yanda bugun zuciyar sa ke cigaba da k'aruwa fiye da d'azun, ba zeso wani abun ya shiga tsakanin sa da Ayrahn a Hotel ba, ba dan haka ba yau yadda yake jin sa babu abinda ze hana shi bin abinda zuciyar sa ke raya masa duk da yadda ita kan ta Ayrahn har yanzu bata koma asalin Ayrahn ta ba. Seda ya shiga toilet ya watsa ruwa sannan ya fito har lokacin tana baccin ta a nutse babu hayaniya, da alama dama baccin jiyan be wani wadace ta ba, hakan ne ya sanya shi saurin shiryawa ya fice yana fatan har ya dawo bata farka daga baccin ba, kafin nan ya samo musu mafita. ... Sanda ya isa gidan kae tsaye parlourn Abbu ya wuce dan yana da tabbacin yana nan, da sallama ya shiga d'akin, Abbu dake zaune kan kujera hannun sa d'auke da laptop yana aeki ya amsa sallamar har lokacin be d'auke idanun sa daga kan laptop d'in ba, a nutse ya k'arasa cikin parlourn ya zauna a k'asan had'ad'd'en carpet d'in dake malale a tsakiyar d'akin "Barka da safiya.." ya fad'a yana kallan Abbun, se a lokacin Abbu ya sauke ajiyar zuciya sannan ya rufe laptop d'in ya ajje ta gefe kana yace "Barka dae doctor ya Muneerahn?" "Alhamdulillah.." ya fad'a a

Table of Contents

Chapters

70 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70