Skip to content

Chapter 27

Chapter 27

Zazzafar Kauna Book One Complete Hausa Novels 1,204 words 0 views Progress saved
Download Book

yayi yabi kowa ya kar6a paper sa, wasu duk suka baada yayin da wasu k'alilan basu bayar ba saboda basu gama ba, Monitorn bebi ta kansu ba ya had'a paper hannun sa yabi bayan Rk daya fice daga cikin ajin har zuwa motar sa, ya bud'e ya shige motar sannan Monitorn ya ajje masa papers d'in a front seat, dae_dae sanda yake tada motar su 3 suka fito, Ayrah se wata er ajin tasu Fateema, sannan wani su kad'ae ne basu bayar ba, Monitor ya kalle su sannan ya kalli Rk yace a hankali "Sir.. Pls wad'anda basu bayar ba!" da mamaki Rk ya kalle shi kamar ba zece komae ba se kuma yace "Saboda raeni?" da sauri ya girgiza kae lokaci d'aya yana furta "No sir, ina sauri ne ban kar6i ta sun ba saboda kada dukan mu mu rasa, Sorry sir" "Leave them, next tym zasu yi saurin baka.." yayi maganar sanda yake maeda kan sa kan driving d'in daze soma "Pls Sir, ayi musu hak'uri ba dan halin su ba" yayi d'an shiru sannan yace bayan ya fesar da iska daga bakin sa "Su wakilta mutum d'aya a kae min office" ya fad'a yana yin gaba "Thank u so much Sir" Monitorn ya fad'a yana mik'ewa tsaye zuwa bakin class d'in, daga inda take ta runtse idanun ta tana ganin kamar tun yanzu tayi failing course d'in tunda gashi ta rasa C.A, tana shirin komawa cikin ajin hannun ta akan fuskar ta tana ji kamar ta fashe da kuka ta jiyo muryar Monitorn nasu na fad'in "Ayrah.." seta dakata lokaci d'aya tana juyowa, ya kalli yanda fararen idanun ta suka sauya kala sannan yace bayan yayi murmurshi "Doctor yace a cikin wad'anda ba kuyi submitting Paper ku ba ku wakilta mutum d'aya ya kae masa" lumshe idanun ta tayi tana jin wani irin dad'i na ratsa ta, seta kalli Fatima dake gefen ta itama rik'e da tata Paper a hannun ta tace tana kallan namijin da shima be bada ba, bata san sunan sa ba dan ita harkar matan ajin nasu ma bata kowa take shiga ba ballantana ta mazan ajin nasu "Gashi zaka kae masa?" ta k'are maganar tana kallan sa, Monitor ya kalle ta yace "kin san yadda za'ayi? Ki kar6i Paper su ki had'a ki kae masa" da mamaki ta kalle shi jin furucin sa kafin tace komae ya sake jinjina kae, da sauri ta girgiza kae sannan tace da sauri tun kafin ma ya sake cewa komae "A'ah ba zan iya ba.." tayi maganar da dukkan gaskiyar ta, dan a yadda take ji koda za'a ce sun rasa exam ne ba C.A ba ba zata iya zuwa wajen mutumin ba, cikin maraeraecewa Fateema tace "Don Allah Ayrah kije ki kae kin ji?" "Toh ke waya hana ki zuwa?" ta fad'i abinda take sak'awa cikin ran ta, kafin duk suce komae ta sake fad'in "Babu inda zan je ni" tayi maganar kamar zata saka kuka, hannu Monitor ya saka ya kar6i takaddun hannun su duka har ta Ayrah sannan yace "Zo muje mu kae masa" tunda taga ya kar6a se kawae ta bishi a baya kamar wata doluwa, a haka har suka k'arasa Office d'in Rk, seya kalle ta bayan sun dakata daga tafiyar yace "Kinga abinda yasa nace ki kae masa da kan ki, su Fateema sun fiya kaud'i, kuma kin san halin doctor.. kada suzo su janyo muku shiyasa nace ke kije, yanzu dae kije ki kae kada lokaci ya k'ure yace baze kar6a ba" hannu ta sanya ta kar6a fuskar ta a cunkushe, sannan ta runtse idanu tana karanto addu'ar da duk tazo bakin ta kana ta fara takawa zuwa bakin Office d'in, da sallama d'auke akan la66an ta ta shiga cikin Office d'in, ba tare data kalli kowa ba ta zube akan k'afafun ta, wani irin sassanyan k'amshi ke tashi cikin Office d'in, wanda ya had'e da k'amshin turaren sa da kuma shi kan sa na Office d'in ga kuma sanyin A.C hakan ba k'aramin k'arawa yanayin Office d'in dad'in shak'a yayi ba. Da mamaki Muneerah dake zaune kan kujera ta kalle ta, seta saka hannu ta zame k'aramin glass d'in dake fuskar ta ta cigaba da kallan ta "Malama menene zaki shigowa mutane waje without even taking excuse?" taji maganar daga gefen ta, idan kujerar da Muneerahn ke kae ta d'ago ta kalle ta toh Ayrah ma ta kalle ta, seta d'aga kae a hankali ta kalli inda yake zaune kan kujera yayi shiru hannayen sa rik'e da ha6ar sa kamar me tunani "Sir.." karo na farko kenan data ta6a yi masa magana, ita bata so ma hakan ta faru ba, so tayi har ta gama makarantar wata magana ba zata ta6a had'a ta da shi ba, idanun sa masu kaefi ya d'aga ya kalli Muneerah dake sake fad'in cikin kufula "Kamar dake nake koh?" lumshe idanun ta Ayrah tayi ba tare data juya ta kalli Muneerah ba tace "Sir test d'in mu na kawo.." tayi maganar tana mik'ewa daga zaunen da take ta ajje masa kan bench d'in dake gaban sa, jin bece komae bane ya sanya ta mik'ewa tana jin k'irjin ta na bugawa lokaci d'aya kuma tana fatan Allah yasa kada yace wani abun, ya kar6a kenan "Don't ever try dis mistake again.." ta jiyo daddad'ar muryar sa yana fad'in hakan kuma a hankali kamar wanda akawa dole, ba tare data kalle shi ba ballantana bugun zuciyar ta ya k'aru tace "In Sha Allah" tana shirin fita ta jiyo muryar Muneerah na fad'in "Kin ci sa'a yau an miki uzuri, saboda haka se ki kiyaye" ta fad'a ita a lallae dole se an gane wata ce ita a wajen Rk d'in, kallan ta kawae Ayrah tayi tana jin wani irin takaeci da haushi na musamman na zuwa suka tirnik'e ta, dan haka yanzu ma ba tace komae ba se sake d'auke kan ta da tayi, daga haka ta sanya k'afa ta fice daga Office d'in, galala Muneerah ta bita da kallo sanda ta gama ficewa daga Office d'in sannan ta dawo da duban ta kan Rk tace "Baby wannan d'alibar ka ce?" kallan Muneerah yayi kallo irin na cikin ido wanda ya sanya ta kauda kan ta gefe se dae har lokacin bata ji yace komae ba dan haka ta sake furta "Baka tunanin shirun da ka mata bayan abinda tamin kamar ze janyo min raeni ne" "Meye had'in ki da ita?" yayi maganar cikin basarwa, se tayi shiru kawae tana mamakin wannan mutumin, yaja Papers d'in data kawo ya had'a su da ragowar sannan ya mik'e yana zura wayar sa cikin aljihu yace "Zan fita" "Da wuri haka Baby? Ina zaka je?" yamutsa fuska yayi ba tare da ya bawa tambayar ta ta muhimmaci ba yace "Zaki tafi ne?" a shagwa6e ta furta "Haba haba kae kuwa Yaya na, ni fa hira nazo na taya ka" kansa ya d'an dafe dan shi yana jin kamar ciwon kae take k'ok'arin saka masa, a yayin da ita a 6angaren ta tana yin komae ne dan saboda ta burge shi, jin da tayi bece komae bane ya sanya ta fad'in "Ohk muje na raka ka" ta fad'a tana murmushi "No babu buk'ata" ya fad'a yana d'aukar key d'in

Table of Contents

Chapters

70 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70