Skip to content

Chapter 35

Chapter 35

Zazzafar Kauna Book One Complete Hausa Novels 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

Bahijja ta fad'a dan tana ganin kamar duk tafi su takaeci da abinda Ayrahn ta aekata musu, ta shammace su, tayi wasa da hankalin su, ta kuma nuna musu yawan shekaru ba shine wayo ba. .. Da sallama ya shiga d'akin yana sanye cikin wasu k'ananan kaya masu kyau da taushi, kan sa d'auke da facing cap data matuk'ar k'awata shigar sa ya fito yayi kyau abin sa, cikin sa'a seya samu Mummy har ma da Daddy a d'akin, ba k'aramin dad'in ganin hakan yayi ba, dan haka ya k'arasa ya zauna k'asan Carpet yace "Barkan ku da warhaka" "Barka kadae" suka had'a baki wajen fad'in hakan "Daddy dama inaso ne na shaeda maka yau zan koma Kano" "Kano kuma Likita? Wani abu ne ya faru?" seya girgiza kae kawae yana d'an lumshe idanun sa kad'an bece komae ba har zuwa sanda Mummy tace "Haba kae kuwa Raj, gaggawar ta me ce?" "A'ah Mummy.." shine abinda kawae ya fad'a, Daddy yace "Ko dae akwae abinda zaka yi ne acan d'in?" tambayar Daddyn ta matuk'ar yi masa dad'i dan haka da sauri ya furta "Ehh Daddy, akwae wani abu me muhimmanci da zan gabatar acan d'in.." "Toh shikenan babu damuwa, akwae maganar ma dama da zaku yi da Abbun naka.." be bawa zancen muhimmanci ba dan haka kawae abinda yace shine "Tohm" "Allah yayi maka albarka kaji Doctor, Allah kuma ya sanya albarka" shine abinda Mummy tace "Ameen" kawae yace duk da ita kan ta be gane akan maganar da take magana ba, ya dae fi tunanin itama taji labarin ajiye aekin da zeyi ne yasa take magana fatan alkhaeri, seya mik'e hannun sa d'aya cikin aljihun sa yace bayan yayi murmushi "Daddy bari naje na sake shiryawa" "Toh Raj, seka fito" daga haka ya fice daga d'akin. .. Ko jakar ta bata iya d'auka ba ta fad'a cikin gidan nasu da gudu tana kwad'a sallama da siririyar muryar ta, wani sanyi Umma taji ya ratsa ta jin muryar shalelen er tata, kafin ma ta kae ga k'arasowa Umman ta fito daga cikin d'akin ta, aekuwa tana shigowa ba tayi wata wata ba ta fad'a jikin Umman tana sakin dariya lokaci d'aya tana furta "Nayi kewar ki sosae Umma ta" murmushi Umma tayi ita kan ta tasan tayi kewar d'iyar ta ta sosae, dan haka itana ta rungume ta tana fad'in "Yanzu ae gani gaki koh?" seta jinjina kae har lokacin tana jikin Umma, sun kae wajen minti 1 a haka sannan Ayrah ta saki Umma tana fad'in "Umma ina Yah Sadeeq?" "Yana d'aki bacci yake" Umma ta fad'a tana kallan d'iyar ta ta "Umma wallahi yanzu Yah Sadeeq ya zama malalaci, kullum cikin bacci" ta fad'a lokacin data shiga d'akin nasa, seta hange shi kwance kan gadon idanun sa a rufe ya lullu6e rabin jikin sa da bargo, se tayi murmushi tana jin dad'in ganin sa sannan ta k'arasa ciki tana fad'in "Yah Sadeeq ka tashi, na dawo" kamar daga sama ya jiyo muryar lilin ta sa, dan haka a hankali ya bud'e idanun sa se kuwa ya sauke su a kan ta, murmushi suka sakarwa junan su sannan Yah Sadeeq yace "Yanzu kuka shigo?" "Ehh Yah Sadeeq nayi kewar ka wallahi" ta fad'a tana 6ata fuska, dariya yayi yana jin dad'in ganin k'anwar ta sa dan shi kan sa yayi kewar ta irin sosae d'in nan "Nayi kewar rigimar nan taki Auta" ya fad'a har lokacin yana murmushi "Kae Yah Sadeeq rigima kuma?" ta fad'a har lokacin dae tana 6ata fuska gami da tura baki "Toh shikenan dae ya hanya?" ya fad'a yana k'ok'arin tashi zaune, shi kan sa baya so ta gane karaya ce a k'afar sa dan ya riga yasan halin ta yanzun nan zata fishi shiga damuwa, se akayi sa'a ma tace "Yah Sadeeq kayi baccin toh, idan ka tashi se muyi hirar" ta fad'a tana kallan sa, seya koma ya kwanta ba dan yana tunanin ze iya baccin ba sannan yace "Toh shikenan Auta.." "Yawwah Yah Sadeeq" ta fad'a tana ficewa daga d'akin tana fad'in "Umma kin ga lalacin Yah Sadeeq d'in koh? Ya sake komawa baccin" ta fad'a tana k'arasawa tsakar gidan, dae_dae lokacin da Umma take fad'in "Za dae a tantance malalacin" turo d'an k'aramin bakin ta tayi sannan tace "Kae Umma" dariya Umma tayi tana fad'in "Toh shikenan, ina Abban?" "Aou" ta fad'a bayan ta kae hannun ta kan bakin ta sannan tace "Allah sarki Umma k'anwar Zaenab ce ta rasu shine ya tafi za'a kae ta" "Innalillahi wa inna ilaehi rajiun, ashe ta rasu? Toh Allah ya ji k'an ta, ashe ba mazauniya bace" Umma ta fad'a tana tuna yarinyar data rasun wadda ba tafi wata 5 da haehuwa ba, k'arasowa Ayrah tayi ta zauna kan tabarmar da Umma ta shimfid'a, seda Umma ta zauna sannan ta d'ora kan ta akan cinyar Umman tace "Umma nazo muku da wani albishir, amma bazan fad'a ba se Abba ya dawo" "Wane albishir ne wannan?" "A'ah Umma se Abba da ya dawo" Ayrahn ta fad'a tana sake gyara kwanciyar ta kan cinyar Umma "Toh shikenan, ya exam ya karatun?" "Umma komae Alhamdulillah fa" ta fad'a tana murmushi, daga haka suka cigaba da hira, Umma nata jin labaran da Ayrahn ke ta bata, wani tayi dariya wani ta girgiza kae cike da ganin wautar Ayrahn, se dae lokaci lokaci ta kan yi shiru ta saki murmushi me k'ayatarwa idan ta tuna Rk, Umman na lura da ita amma har lokacin tak'i fad'awa Umma komae game da albishir d'in da tace zata yi musu, dan haka itama ta mata shiru kawae tana cigaba da saurarar hirar da take mata. ... A 6angaren Rk kuwa dab da maghrib ya isa gidan nasu cikin motar sa, k'atuwar harabar gida dake d'auke da manya manyan motoci a gefe guda, shuke shuke da sauran abubuwa na burgewa, kae tsaye parking lot d'in ya wuce da motar sa yayi parking nata dae_dae lokacin da wani ya k'araso da sauri yana fad'in "Barka da dawowa yalla6ae" ya fad'a yana duk'awa "Barka, a shigar min da kaya ciki" shine abinda Rk ya fad'a yana wucewa cikin tafiyar nan tasa ta nutsuwa hannun sa d'aya cikin aljihun sa, tafiya me tsayi ce yayi kafin ta sada shi da aenahin inda d'aku nan masu gidan yake, yayi murmushi sanda ya ganshi a k'ofar Parlourn Ummeen sa, babu 6ata lokaci ya sanya k'afar sa cikin k'aton hamshak'in Parlourn da sallama, Ummee na zaune kan kujera hannun ta d'auke da remote tana shirin chanja channel yayi sallama, seta ajje remote d'in akan kujera tana kallan sa sanda wani k'awataccen murmushi ya su6uce a fuskar ta tace tana k'arasawa inda yake "Oyoyo Oyoyo.." k'arasawa yayi inda take yayi hugging nata sannan ya zauna a k'asan kujerar yace cikin girmamawa "Ummee barka da wannan lokacin" "Barka dae ya hanya?" "Hanya Alhamdulillah" ya fad'a dae_dae sanda aka k'walla kiran Sallah a masallacin su dake jikin gidan nasu, se yayi saurin mik'ewa yana fad'in "Ummee bari naje" "Toh Raj seka dawo" ta fad'a tana bin sa da kallo har lokacin da murmushi kan fuskar ta. A harabar gidan suka yi kaci6us da Abbu dake sanye cikin wata dakakkiyar bluen shadda d'inkin babbar riga data matuk'ar yi masa kwarjini "Welcome my Son"

Table of Contents

Chapters

70 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70