Skip to content

Chapter 14

Chapter 14

Zazzafar Kauna Book One Complete Hausa Novels 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

Mato a wayar sa, ya kalli wayar na tsawon sakanni sannan ya d'aga ya kara ta a kunnen sa, daga can 6angaren Alhaji Mato yace "Haji Ibraheem na jika shiru kwana 2 yasa nace bari na ta6o ka" d'an numfashi kad'an Abba ya sauke sannan yace "Wallahi kuwa, nima ina ta k'ok'arin kiran ka se kuma na sha'afa, dama zuwa anjima nake so nazo wajen naka, ina so ka sake min kwantance" "Toh toh Madallah.." Alhaji Maton ya fad'a yana d'orawa da yiwa Abban kwatance, Umma ta kalle shi sanda ya gama wayar tace a nutse "Yanzu ya za'ayi da shi kenan?" seda Abba ya sauke ajiyar zuciya sannan yace "Zan fad'a masa gaskiya ne, idan ya yadda da k'addara shikenan idan kuma be amince ba yace sena biya shi kud'in sa se nasan yadda za'ayi.." "Toh Allah Ubangiji yasa ma shima ya kar6i wannan k'addarar" "Ameen" Abba ya fad'a ba dan yana da tabbacin hakan ba, dan shi sheda ne akan son kud'i irin na Alhaji Maton. .. Shiru Alhaji Maton yayi har Abba ya gama masa bayanin abinda ya faru, se yayi murmushi yana girgiza kae kana ya d'aga kae ya kalli Abba yace "Haji Khaleel ni fa gani nake ko menene ya faru kae ka jawa kanka, ba sau d'aya ba ba sau biyu ba na fad'a maka na kuma baka shawara ka rabu da matar ka, farar k'afa gare ta, an kore ka daga banki, kazo ka fara teaching an dakatar da kae ka fara kasuwanci wani ya gudu da kud'in wannan kad'ae be ishe ka ka gane.." "Malam ya ishe ni haka!" Abba ya fad'a yana d'aga masa hannu idanun sa akan sa cike da zallahr 6acin rae "Aou aou toh hakane abin, wato har yanzu kae ka kasa gane Annabi ya faku koh?, toh cigaba da zama da ita, ina ga ba zaka fahimci abinda nake fad'a maka ba se ranar da kayan sakawa ma ya gagare ka sakawa.." Abba ya runtse idanun sa zafin zuciyar da yanzun ya zame masa jiki se k'aruwa yake yi, a nutse ya mik'e tsaye sannan cikin kaurin murya ya furta "Kana buk'atar kud'in ka ne ko kuwa?" "A'ah se kuma in k'i buk'ata, ina jiran kud'i na a cikin satin nan kawae" Alhaji Mato ya fad'a shima yana mik'ewa ya bar wajen, da kallo Abba ya bishi yana mamakin wannan banzan hali irin na Alhaji Maton, shikenan kuma a matsayin ka na bawa musulmi Allah baze jarabce ka ba? Da wannan tunanin ya koma gida yana sak'a da warwarar yadda ze biya Alhaji Maton kud'in sa. Sanda ya koma gidan bayan yaci abinci Umma ta tambaye shi yadda suka yi da Alhaji Maton, duk se yaji tausayin ta ya kama shi yadda wani ke ik'rarin duk dalilin tane abubuwa ke faruwa dashi, abinda shi kuma baze ta6a yadda ba kenan, dan kuwa shi musulmi ne daya yadda da k'addara me kyau da kuma mara kyau, gyara zama yayi yana kallan ta "Kada ki damu, zan san yadda zanyi in biya shi kud'in sa.." cike da mamaki Umma tace "Aou yace se an biya shi?" "K'warae kuwa" Abba ya fad'a "Ikon Allah.." Umma ta fad'a tana girgiza kae... Abba beyi k'asa a gwuiwa ba wajen d'akko motar sa ya siyar da ita ba, saboda matsalolin da take dasu yasa ba tayi wani daraja ba gata kuma dama ba babbar mota bace, seya d'auki kud'in Alhaji Mato ya bashi sannan ya rik'e ragowar a hannun sa dan amfanin yau da gobe, abinda ya tsaya masa a rae yanzun kawae shine yadda zeyi ya samu sana'a ko dan ya sanya 'ya'yan nasa a makaranta, abinda ya k'ara masa k'aemi ma akan saka su a makarantar shine.. Rannan suna zaune a cikin parlourn dukan su suna kallan Al jazeera inda Abba ke kallan labarae, Ayrah na zaune gefen Abban itama tana kallan T.Vn kamar me fuskantar abinda ake nunawa a ciki, daga k'arshe a cikin labaran aka nuno wasu d'alibae da Uniform d'in su, se kuwa tayi zumbur ta tashi zaune tana kallan Abba tace "Abba mun dena zuwa makaranta?" kallan ta Abba yayi cikin mamakin jin furucin ta, se yayi murmushi sannan yace yana shafa doguwar sumar kanta dake a bud'e "A'ah za'a sanya ku mana" "Abba yaushe?" ta sake tambayar sa, seya d'an yi shiru kana yace "Nan bada dad'ewa ba Uhmm?" "Hadda Raj koh?" ta fad'a tana murmurshi, zancen kenan dan kullum idan ba tayi maganar Raj ba toh ba Ayrahn bace "Ehh" Abba ya fad'a yana maeda duban sa kan T.V. .... Sosae Umma ta takurawa Abba akan zuwa asibiti saboda rashin baccin da yake samu, shima kansa rashin baccin na damun sa dan haka a wannan karon da tazo masa da k'orafi be musa mata ba ya shirya ya tafi asibitin, gwajin hawan jini aka fara masa, kuma tashin farko su kaga yanda jinin sa ya hau, sosae suka bashi shawarwari akan hakan da kuma magunguna, hakan ba k'aramin kuma tayar masa da hankali yayi ba, amma gudun kada hankalin Umma ya tashi yasa be sanar da ita ba, kawae yace mata an gwada shi amma basu fad'a masa aenahin abinda ke damun sa ba se result d'in ya fito, haka ta yadda da abinda ya fad'a mata d'in, yayin da shi kuma ya cigaba da shan magungunan sa ba tare daya bari Umman ta sani ba. A lokacin ne ya cigaba da fama da rashin bacci da kuma tunanin daya zame masa jiki, se kuma bugun zuciya da shima baya rabo dashi, haka wataran ze kwana a zaune, se dae da yake baya bari lokacin ya tafi masa a banza se hakan yake sakawa baya wani damuwa sosae, dan kuwa k'arin lokacin karatun Qur'an ya samu, idan dae ya fahimci bacci baze zo masa ba seya fito tsakar gidan nasu ya shimfid'a dadduma yayi ta karatu har zuwa asuba, ranar da kuma ya samu baccin se yayi baccin sosae, sau da dama Umma kan farka ta same shi yana karatu, dalilin kenan daya sanya bata damu da rashin baccin nasa ba, saboda ta riga data saba da ganin sa cikin dare yana tashi karatu, se dae tasan ya k'ara lokacin karatun, amma duk da haka bata kawo rashin samun bacci ne ya sanya shi k'ara lokacin karatun ba, tafi ta'allak'a hakan da yanayin rayuwa kawae.. Sanda Umman ta gano ciwon dake tattare da Abban ba k'aramin tashin hankali ta shiga ba, dan har kuka seda tayi, Abba ya fesar da iska daga bakin sa yana kallan ta yace "Kiyi hak'uri kiyi shiru, kada kisa nima nawa hankalin ya tashi mana" "Amma Abban su meyasa ka 6oye min?" "Toh yanzu ba gashi kin sani ba?" ya fad'a yana kallan ta, seta share hawayen fuskar ta sannan tace "Duk da kullum cikin yi maka addu'a nake, amma ko ba komae zan dage da maka addu'a akan ciwon koh?" "Toh shikenan nayi laefi amin afuwa" ya fad'a yana kallan ta da tattausan murmushi akan fuskar sa, itama murmurshin tayi duk da yadda can k'asan zuciyar ta ke cunkushe da tausayin Abban. .. Sosae Abba ya dage wajen neman sana'ar da zata rufa musu asiri, se dae har zuwa lokacin be samu ba, gaba d'aya yanzu burin sa be

Table of Contents

Chapters

70 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70