Chapter 20
Chapter 20
da "Kana ganin idan naje wajen mahaefin ta a yanzu banyi gaggawa ba?" girgiza kae Muttala ya shiga yi ya d'an yi murmushi kana yace "A'ah ranka ya dad'e ka bari tukunna, kada su fahimci dalilin hidimar ka tun yanzu, zefi kyau mubi komae daki_daki.." "Gaskiya a haka ma nayi k'ok'ari wallahi, bari dae zan bar ta ta gabatar da first semester kawae zuwa lokacin zan je wajen baban nata" ya fad'a yana girgiza kae shima "Toh hakan ma babu laefi" Inji Muttala.. .... Tana sanye cikin doguwar rigar atamfa da hijab kasancewar sa favourite nata, sosae kyakykyawar fuskar ta tayi fayau kamar mara lafiya, fararen manyan idanun ta sunyi ja, hannun ta cikin na Umma tana kallan ta da idanun nata da suka sake yin rau rau, Umma tayi murmushi dan tana so ne ta kwantar mata da hankali tace "Ya isa haka shalele, kada ki 6ata fuskar nan taki yanzun nan mana Uhmm?" Umma ta fad'a tana sanya hannu ta d'auke k'wallar dake zuba akan kuncin ta "Umma ta zanyi kewar ki" ta fad'a tana kwantawa a jikin Umman, hannu Umma ta saka ta rik'o ta bayan tayi murmushi tace "Banda abin ki Ayrah ae ba dad'ewa zaki dinga yi ba, ko kin manta zaki dinga dawo mana hutu?" seta jinjina kae kawae "Toh idan kin gama kukan seki taho mu tafi" Yah Sadeeq daya shigo ya fad'a, seta d'aga kae tana kallan sa gami da murgud'a mitsitsin bakin ta "Iyeee.. Lallae ne yarinyar nan" Yah Sadeeq ya fad'a yana rik'e ha6a. Har k'ofar gida Umma ta rako su inda motar da zata kaesu Zarian take, seda taga tashin motar tasu sannan ta koma cikin gidan tana matse k'walla, dan kuwa tun tasowar Ayrahn baza tace ga ranar da suka ta6a rabuwa ba, dan tun tana yarinyar ta mayyar Umman ce, ko yadda da mutane ba wani sosae take ba ballantana ace taje ta kwana. ... "Ki maeda hankali kiyi karatu, sati d'ayan nan da aka wuce ki ki samu wata ta koya miki, banda yin k'awar da zaki zauna kina fad'a mata cikin ki duk da dae nasan halin ki amma dae gwara na tisa miki" Yah Sadeeq ya fad'a sanda suke tsaye a wani ke6antaccen waje, seta jinjina kae kawae dan bata tunanin zata iya magana, idan kuwa tace zatayi maganar toh tabbas kuka zata saka, Abba daya fahimci haka se yayi murmushi dan shi kansa har ya fara kewar Autar tasa, ya matsa kusa da ita yace "Ayi karatu sosae koh?" nan ma dae seta jinjina kan tana kae hannun ta idanun ta ta goge hawayen daya sauko akan fuskar ta, hannu Yah Sadeeq ya sanya cikin aljihun sa ya zaro wata k'aramar waya yace yana kallan k'anwar tasa "Yau dae ga alk'awarin mu.." seta kalli hannun nasa sannan ta kalle shi, bata san sanda murmushi ya su6uce a kyakykyawar fuskar ta ba, ta saka hannu ta kar6a cike da farin ciki kana ta d'an jujjuya ta sannan tace lokacin da wasu kyawawan hawaye suka samu damar zubowa akan kuncin ta "Amma nagode sosae Yah Sadeeq, Allah ya k'ara arzik'i" "Ameen" dukan su suka amsa da hakan cikin jin dad'in yadda ta d'an saki jiki.. seda suka d'an dad'e suna sallamar zuwa lokacin ta saki jiki suna ta d'an hira, se kuma daga baya tayi kukan ta ta godewa Allah, sannan su Abban suka tafi bayan sun kwantar mata da hankali... ... A hankali ta tura k'ofar d'akin hannun ta jaye da er trolley d'in ta da aka kar6o mata a wajen k'anwar Umma da itama zama ya dawo dasu cikin kano, dukkan su suka d'aga kae suka kalle ta sanda tayi sallama da kyakykyawar siririyar muryar ta data sake sirancewa saboda kukan da tayi, su 3 ne zaune a cikin d'akin, d'aya na daga gefe tana danna waya yayin da biyun ke zaune kusa da juna suna hira "Wa'alaeki Assalam" suka amsa dukan su suna bin bak'uwar fuskar da suka gani da kallo "Wow, tubarkallah Masha Allah" d'aya daga cikin su ta fad'a a ranta lokaci d'aya kuma tana mik'ewa tsaye ta k'arasa inda Ayrah take tace tana d'an yin murmushi "Anan d'akin kike?" tayi maganar tana kallan idanun ta da suka yi ja alamar kuka tayi, seta k'ak'alo murmushi ta wanzar akan fuskar ta wanda kana gani kasan beje ko'ina ba tana jinjina kae "U're highly welcome.." ta fad'a tana d'aukar bagcon data gani a gefen Ayrah tayi gaba, babu musu Ayrahn tabi bayan ta a hankali "Ruks ki tashi me waje tazo fa" wadda ta kar6i jakar Ayrahn ta fad'a tana kallan wadda ke zaune kan gado tana danna waya, wadda aka kira da Ruks d'in ce ta mik'e tana kallan Ayrah itama tayi murmushi tace "Barka da zuwa bak'uwa" "Umhum" Ayrah ta fad'a kawae tana jefa mata kalar murmurshin data yiwa Jidda, seta k'arasa ta zauna akan gadon tana jin ta gaba d'aya a wani irin takure, musamman yadda taga su duk lokaci d'aya suna neman sakin jiki da ita, seda Jidda ta ajje mata kayan ta gefe guda sannan ta dawo ta zauna kusa dasu Ruks ta zauna, Bahijja da tun d'azun ba tace komae ba se kallan Ayrah da take tace "Bak'uwa ya sunan ki?" a hankali ta bud'e bakin ta daya mata nauyi tace "Ayrah.." "Awwwn, sunan en gayu, suna me dad'i.." kusan a tare suka fad'i hakan, har seda hakan ya sanya ta tayi murmushi "Toh barkan ki da zuwa" Bahijja ta fad'a... Suna nan zaune d'akin har bayan isha'i suna hirar su, hirar da kusan duk akan abu d'aya suke yin ta, ita dae tana zaune a gefe guda se dae ta bisu da ido kawae, so take ta ke6e ita kad'ae tayi kukan ta ko zata ji sauk'in kewar gida data fara damun ta tun yanzun. "Ruks ki tashi ki d'ora mana ko Indomie ce pls, kinga bak'uwa ma ba taci komae ba" Jidda ta fad'a, Ruks ta kalli Ayrah tace "Ayrah kina jin yunwa ne?" seta girgiza kae kawae tana yabawa da kulawar mutanen da bata ta6a ganin su ba se yau "A'ah a k'oshe nake" ta fad'a tana kallan Ruks d'in "Toh dae kin ji, mu duk bama jin yunwa muma, a bar shi kawae pls" "Shikenan ae" Jidda ta fad'a "Kuuu, kun san k'arfe nawa kuwa?" Bahijja ta fad'a tana d'an waro eyes d'in ta "Wani abun ya faru?" Ruks da Jidda suka tambaya lokaci d'aya "Ni kam seda safen ku wallahi, kwanciya zanyi ko dan na tashi da wuri, gobe fa Doctor RK ne a farko, ko kun manta abinda yayi last Monday?" ta k'arasa maganar tana hayewa kan gadon ta "Nima kam seda safen ku" Ruks ta fad'a tana mik'ewa, harara Jidda ta jefa mata sannan tace "Toh ni me zan zauna jira hajiya? Ayrah seda safe" tayi maganar itama tana hayewa gadon ta.. Bin su tayi da kallo su duka lokacin da d'akin yayi shiru, se taji tsoro ya fara shigar ta, dan haka taja jikin ta ta maeda shi kan gadon ta kwanta, ta lullu6e kafatanin jikin ta da hijab d'in ta wani sanyi na ratsa ta, a hankali ta lumshe idanun ta wasu hawaye masu d'umi na sakkowa akan fuskar ta, wayar data tuna da ita ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70