Chapter 5
Chapter 5
saba ganin sa kamar koda yaushe yana zaune yanzun idanun sa kan wata takadda yana kalla, a hankali ta fara takawa zuwa inda yake zaunen idanun ta a kansa "Ayrah..er carafke fa muma yau zamu yi" wata k'awar ta da itama ba zata wuce sa'ar ta ba ta fad'a da maganar ta me cike da tsamin baki, bata ma jita ba dan gaba d'aya hankalin ta yayi kansa, har zuwa sanda wata a cikin k'awayen nata ta dafa ta tana fad'in "A'ah ki taho enter zamu yi" ta fad'a tana dariya, hannu Ayrah ta saka ta zame hannun k'awar ta ta dake kan kafad'ar ta sannan tace "Ke ni ba zanyi ba.." daga haka tayi gaba, su kuma yaran duk basu bi ta kanta ba suka cigaba da wasan su, seda ta isa inda yake d'in sannan ta tsaya tana cigaba da kallan sa da kuma kayan dake jikin sa, a k'alla zeyi shekaru 12 ne, fari ne sosae kyakykyawa ajin farko, me manyan idanu da dogon hanci, ga wata bak'ar suma dake kwance akansa sedae daga gani kasan bata samun yadda take so dan haka ta d'an cukurkud'e kad'an, kayan jikin sa ma haka kana ganin su kasan sunji jiki amma da alama shi duk wad'annan basu dame shi ba dan kuwa har lokacin idanun sa na kan takaddar hannun sa ne "Kae!!" Ayrah ta fad'a tana kallan sa, da sauri ya d'aga manyan idanun sa ya sauke su akan Ayrahn, bece komae ba seya maeda kansa kan takaddar sa "Kae!!" ta sake fad'a a karo na, d'an lumshe idanun sa yayi sannan ya ninke takaddar a hannun sa ya mik'e, yana k'ok'arin barin wajen Ayrah tace "Kawo na koya maka.." seya d'an dakata kad'an kafin ya juyo yana kallan ta, hannu ta mik'a ta kar6i takaddar hannun sa tana kallan abinda ke ciki, ta karanta da karatun data iya sannan ta kalle shi yadda shima ita d'in yake kalla, seta saka dariya kawae hadda toshe baki kamar wata babba, dama fuskar tasa babu annuri yanzu kuma da yaga tana masa dariya seya sake tsuke ta ya sanya hannu ya kar6i takaddar hannun ta ya juya da nufin barin wajen, hannun ta ta saka ta rik'o nasa hannun, manyan idanun ta sun cika da k'walla tace "Yi hak'uri, gani nayi kae babba ne fa.." ta fad'a abinda take ganin shine ya dace ta fad'a "Allah kuwa idan kana so zan fad'awa Yah Sadeeq ya dinga kowa maka karatu.." seya juyo gaba d'ayan sa yana kallan ta lokaci d'aya murmushi na su6ucewa akan fuskar sa yace "Da gaske?" karo na farko kenan da yayi magana, seta jinjina kae kawae tana d'an murmushi... Ku sani wannan book d'in ina yin sa ne based on experience, zan iya cewa wani abun ma true ne wlh nake had'a muku dashi duk dan labarin ya k'ara armashi kuma ku fahimci sak'on da nake son isarwa, Allah yasa mu dace.. *ZARAH BINT YUSUF (Mhiz Innocent)*✍️ https://chat.whatsapp.com/DH0EIIWNPnSICxsGgh2DSd *♡☆ZAZZAFAR KAUNA☆♡* *FREE BOOK* *CHAPTER ONE* ✨ *TITAN'S OF TALENT* ✨ Page_003 ___"Ke Ayrah!!" Yah Sadeeq ya fad'a yana k'arasowa wajen, dukkan su suka d'aga kae suka kalli inda yake, bata motsa daga inda take ba sedae ta cigaba da kallan sa har ya k'araso wajen, ya kalli inda yaron nan ke tsaye na tsawon sakanni sannan ya maeda kan Ayrah, kama hannun ta yayi ba tare da yace komae ba suka bar wajen, yayin da shi kuma ya bisu da ido har suka bar wajen, seda suka isa bakin ajin su sannan ya tsaya ya kalle ta fuskar sa a had'e yace "Meya kae ki can?" rau rau tayi da idanun ta, tana ta6e d'an k'aramin bakin ta kamar zata yi kuka "Ba nace miki ba'a wasa da maza ba?" jinjina kae kawae tayi, yace "Bari na sake ganin ki da wani!" ya fad'a yana sake had'e rae dan ta fahimci da gasken yake "Ya hak'uri Yah Sadeeq.." ta fad'a tana share k'wallar idanun ta, seya d'an yi murmushi kana yace "Yawwah..toh maza ki koma aji.." daga haka ta shige class d'in su shima ya tafi nasu ajin. .. Washe gari ma haka ta sake ganin yaron nan yana lek'e ta window, koda aka fita break seta ajjiye basket d'in ta a cikin ajin sannan ta fita zuwa inda ta ganshi a bayan ajin nasu yau sa6anin da da yake zama a gaban ajin nasu, yana zaune yau ma kamar jiyan yana karanta wata takadda dake hannun sa, seta k'arasa ta zauna tace "Wae kae ba'a saka a makaranta ba?" tayi maganar cike da sakarci, da sauri ya juyo yana kallan ta dan besan da zuwan ta wajen ba maganar ta kawae yaji, ganin ta ya sanya shi sakin ajiyar zuciya sannan ya jinjina kae "Kawo na koya maka toh" ta fad'a tana kallan sa, seya lumshe manyan idanun sa sannan ya mik'a mata takaddar hannun nasa, ta kalla abinda ke cikin takaddar, abinda aka koya musu yau ne seta dinga fad'a masa yadda ta fahimci aekin, shi kuma yana biye mata yana jin abinda take koya masan, kasancewar k'wak'walwar tasu ba d'aya bace kuma karatun su Ayrahn na yara ne yasa cikin k'ank'anin lokaci tana masa yake ganewa, tunda ta fara bece komae ba yayi shiru yana saurarar ta yana kallan ta yadda take maganar duk da ba wani iya magana tayi ba amma yana ganewa, wani abun ne dae sedae idan ta fad'a ya gyara da kanshi, idan ya fahimci bata san yadda zata fad'a ya gane ba, tana ji an kad'a k'ararrawa alamar an koma break seta yarda takaddar hannun ta ta mik'e tana waro idanun ta "Na tafi.." ta fad'a tana shirin wucewa yace "Nagode..ya sunan ki?" seta juyo ta zuba masa manyan idanun ta sannan tace bayan tayi murmushi "Ayrah.." ta fad'a tana juyawa, kamar wadda ta tuno wani abun seta juyo da sauri tace "Kae fa?" murmushi ne ya su6uce a kyakykyawar fuskar sa sannan yace "Suraj..." "Suraj!!" ta maemaeta sunan a la66an ta sannan ta wuce ba tare da ta sake cewa komae ba ta koma ajin su. ... Abba na sauke su a inda ya saba sauke su se suka tafi gida, kamar kullum da sallama suka shiga gidan nasu, Umma na zaune kan dadduma da alama sallah ta idar, tayi musu sannu da zuwa tana rik'e Ayrah data rungume ta "Tashi ki kae basket d'in kitchen.." Umma ta fad'a tana kallan Ayrah "Umma akwae abinci a ciki fa" da mamaki Umma ta kalle ta kana tace "Baki cinye ba?" girgiza kae Ayrah tayi tace "A'ah banci ba fa" mik'ewa Umma tayi rik'e da Ayrahn a hannun ta tace bayan ta zauna "Baki da lafiya ne ko a k'oshe kike?" "Ehh" Ayrahn ta fad'a tana cire hannun ta daga cikin na Umma ta wuce d'aki, Umma ta bita da kallo tana girgiza kae sannan ta dawo dashi ga Sadeeq dake tsaye tace "Meya hana ta cin abincin?" girgiza kae Yah Sadeeq yayi sannan yace "Wallahi Umma bansani ba, kuma amma banga alamar rashin lafiya a tattare da ita ba ballantana ace koh?" "Ehh hakane, may be ko yau a k'oshe take, ko kuma kana so ka koya mata halin ka" Umma ta fad'a tana kallan sa, murmushi Sadeeq yayi yana
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70