Chapter 36
Chapter 36
Abbu ya fad'a yana bud'a hannun sa, Rk ya k'arasa yayi hugging mahaefin nasa sannan yace "Barka da wannan lokacin Abbu" "Barka dae Raj, ka dawo ashe? Mu wuce masallaci dae tukunna" babu 6ata lokaci suka wuce masallacin dake jikin gidan su, ana Sallahr Isha'i Rk ya koma gida saboda yadda yake so ya watsa ruwa a jikin sa yayin da ya bar Abbun a masallaci. Cigaban nan wajen yana page 1, yanzu haka mun ji TUSHEN LABARIN MU dan haka zamu d'ora ne da CIGABAN LABARI.... ... "Shin yanzu kin san wanene Raj d'in da kike magana a kan sa? Waye mahaefin sa? Meya aekatawa rayuwar ku? Mahaefin ku ya amince masa ya bashi amanar da be ta6a bawa wani ba amma daga k'arshe ya wulak'antashi ya tozarta shi yayi wancakali da duk wannan amanar, mahaefin ki ya d'auko shi daga rana ya sanya shi a inuwa amma daya tashi dame ya saka mishi? Seya d'auki mahaefin ki ya jefa shi cikin ranar shi kuma ya cigaba da rayuwar sa ba tare da tunanin halin da zamu iya shiga mu dukan mu ba, Yanzu haka Sadeeq na kwance ne a d'aki sakamakon karayar daya samu ana buk'atar a masa aeki amma babu kud'in aekin, mahaefin Raj ya cuci Abban ku, ya raba shi da dukiyar sa, takaddun sa masu muhimmanci, uwa uba kuma shine silar shigar mu cikin kowanne hali, silar abinda ya aekatawa mahaefin ku ne ya janyo masa hawan jini, ya cuce mu mu kan mu akan son zuciyar sa, ta yaya zan miki wannan bayanin a wancan lokacin ki fahimta? Ina k'wak'walwar ki take ta k'arfin fahimtar wannan zancen?" Umma ta k'arashe maganar tana kallan Ayrah da tunda ta fara maganar ba tace komae ba, idanun ta gaba d'aya Umma suke kalla har lokacin tana cigaba da tuno maganar Umman cikin kunnuwan ta wanda take jin su kamar amsa kuwwa suke mata a kunnen ta, dan kuwa duk da Umman tayi shiru hakan be hana ta cigaba da jiyo sautin muryar Umman a kunnen ta ba, kunnen nata ya mata wani duumm kamar wadda ta kurumce banda sautin muryar Umman babu abinda take ji har yanzun, bata ma sani ba ko Umman ta cigaba da fad'a mata magana ko tayi shiru ne ita dae bata sani ba, abinda kawae ta sani maganganun nan da suka sanya ta cikin sani irin shock da kuma hutun da k'wak'walwar ta ta tafi na wucin gadi su kad'ae keta dawo mata, jikin ta wani irin rawa yake yi kamar me jin sanyi, duk da idanun ta ba'a rufe suke ba amma se take so ta sake bud'e su tarr ko dan ta cigaba da kallan Umman da yanzun take ganin ta dishi dishi, gaba d'aya ta kasa koda bud'e bakin ta ne ballantana ta furta wani abun, koda yake idan ta bud'e d'in ma menene za tace?? Mhiz Innocent......✍️ https://chat.whatsapp.com/DH0EIIWNPnSICxsGgh2DSd *♡☆ZAZZAFAR KAUNA☆♡* *FREE BOOK* *CHAPTER ONE* ✨ *TITAN'S OF TALENT* ✨ Page 027_028 ___Ganin da Umma tayi har lokacin Ayrah ta gaza furta komae ya sanya ta sanya hannu ta share idanun ta itama da k'wallar ta gama tarar mata, kawae seta juya a hankali ta fice daga d'akin dan ta bar Ayrahn ta dawo daga shock d'in data shiga, ta san dole abin ya ta6a ta aenun, bata ta6a zata ba ba kuma ta ta6a tsammani ba se gashi rana tsaka taji dalilin rabuwar Abba da Abbun Raj. Ko d'aga ido ta kalli Umman ta kasa yi sanda Umman ta fice daga d'akin, ita bama ta lura ta fita ba dan kuwa har zuwa lokacin ta kasa gasgata duk maganganun nan da Umma take fad'a ba mafarki bane "Abbun Raj fa" shine abinda ta dinga maemaetawa a cikin ran ta tana so ta hasaso fuskar sa amma ta kasa dan shekarun nada yawa, ga kuma yanayin shekarun ta a lokacin, amma tabbas idan har bata manta ba mutumin ya zo wa Abban ta a matsayin mutumin kirki, bata san menene ya had'a su ba se gashi yau Umma ta bankad'a mata komae taji dalilin Abba na cewa ba zata auri Raj ba, tabbas in dae kuwa haka ne dalilin Abban yana da gaskiya, a hankali ta shiga sauke ajiyar zuciya tana jin wani irin zafi a cikin zuciyar ta, sosae zuciyar ta ke zafi wanda har ta numfashin ta seda ya koma fita da zafi, se a lokacin taji wani kuka ya taho mata, bata hana fitowar kukan ba se kawae ta jefar da jikin ta kan gadon ta fashe da wani irin kuka, a hankali take dukan kan ta akan pillown kan gadon tana jin wata iriyar nadama da danasani na lullu6e ta, kunyar abinda ta fad'awa Abba d'azu na sake k'arawa yanayin da take ciki k'aemi, wani irin kuka take wanda ke fitowa daga can k'asan ran ta, kukan nadama, kukan danasani, kukan rashin sanin mafita, a yau d'aya taji tayi danasanin sanin Rk a rayuwar ta, meyasa ma ta san shi? Meyasa tayi silar zuwan sa wajen Abba? Meyasa ta zamo silar da Abba ya janyo mahaefin sa cikin jikin sa? Yanzu kenan itace silar komae? Itace ta janyo komae? Meyasa tayi hakan? Gani take kamar komae ya faru itace me laefi tunda ita ta kawo Rk d'in "Nice silar komae!" ta fad'a sanda take sake sakin wani kukan me cin rae "Tabbas nice sila, dan da ban san Raj ba Abba baze ta6a sanin Abbun sa ba, ni na janyo Abba ya jawo Abbu a jikin sa har me faruwa ta faru, nayi danasanin sanin ka a rayuwa ta Raj!" ta k'arashe maganar tana cigaba da kukan da har muryar ta ta fara dashewa, yau mamaki na neman kashe ta, wae Abbu ne ya cuci Abba, Abbu ne sanadiyyar tarwatsewar farin cikin su, Abbu ne sanadiyyar saka damuwa a zukatan iyayen ta, Abbu ne sanadiyyar abubuwa da dama da suka faru a rayuwar su, shi kam yanzu menene zece musu su yafe masa? A hankali ta sake komawa ta kwanta har lokacin ta kasa tsaeda kukan da take, haka zalika zafin da zuciyar ta yake yak'i raguwa sema k'aruwa da yake yi, ta rasa yadda za tayi, ji take dama zata iya janyo abinda ya faru ada ta goge komae akan alak'ar ta da Rk, da kuma ana iya tariyo baya data hana kan ta had'uwa da Rk, Yah Sadeeq ne ya fad'o mata, se taji wata sabuwar k'walla ta zubo mata, ta sanya hannu ta d'auke ta lokaci d'aya tana lumshe idanun ta, bata da k'arfin da zata iya tashi yanzu haka taje ta duba jikin sa, amma ita kad'ae tasan abinda take ji a cikin jiki rae da kuma zuciyar ta. ... "Don Allah Alhaji kayi hak'uri ka bari ko zuwa gobe ne, kaga ko hutawa ba kayi ba" Muttala ya fad'a yana kallan Alhajin daya fito daga d'akin sa cikin wata bugaggiyar shadda d'inkin babbar riga, juyawa yayi ya kalli Muttala sannan yace har lokacin be tsaya ba "Wallahi bazan iya hak'ura se gobe ba, gwara ma ka k'yale ni kawae" yayi maganar sanda ya isa motar sa, ya bud'e ya shiga sannan ya kalli Muttala yace "Zaka raka ni ne ko kuma in nemi wani?" seya girgiza kae sannan ya k'arasa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70