Skip to content

Chapter 30

Chapter 30

Zazzafar Kauna Book One Complete Hausa Novels 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

dae ba taga alama ba dan kuwa hirar su suke kamar yadda suka saba kullum se sunyi ta kamar farilla, se juyi take kawae akan gadon tana tuna kyakykyawar fuskar sa, ada sanda yake a Doctor Rk bata ta6a tsayawa ta k'are masa kallo ba ballantana har ta gano wannan kyan na musamman da matan ajin nasu kan kod'a shi akan sa ba, se yau ta kalle shi ta tabbatar da hakan, ta kuma ga zalla kuma aenahin kyau daga Raj d'in. .. Sanda ya koma gida kae tsaye d'akin sa ya wuce yau ko sashen Mummy be je ba, dan so yake kawae ya gama abinda yake ya kira ta yaji abubuwa da dama daga wajen ta, toilet ya fad'a ya watsa ruwa a jikin sa sannan ya fito ya shirya cikin wata brown d'in had'ad'd'iyar jallabiyya, ya zauna yayi karatun qur'an kamar yadda ya saba sannan yayi addu'o'i ya mik'e daga kan abin sallah, yana shirin ninkewa yaji ana knocking k'afar d'akin, d'an tsaki yaja sam be san wani ya kula da shigowar sa cikin gidan ba, kamar ba zeje ya bud'e ba se kuma ya ajje daddumar kan gado sannan ya fito parlourn ya k'arasa ya bud'e k'ofar, kawae seta sanya kae cikin d'akin ta shigo hannun ta d'auke da warmers d'in abinci guda 2 ta ajje a tsakiyar parlourn, sanye take cikin doguwar rigar shadda wadda tasha aeki ta fito tayi kyau da ita, fuskar nan kamar koda yaushe ta k'ara fari, tsaki ne ya su6uce masa akan bakin sa yana lumshe ido, ya akae tasan ya shigo gidan? "Baby yau baka shigo kaci abinci ba, yasa nace bari na kawo maka d'aki, ina fatan ban yi laefi ba?" tayi maganar tana matsowa kusa dashi, bece komae ba ya k'arasa ya zauna kan kujera sannan yace har lokacin be kalle ta ba "Sannun ki" seta saki murmushi tana dawowa itama ta zauna kan kujera tana shak'ar k'amshin turaren jikin sa daya cakud'e dana sassanyan k'amshin sabulun sa, ko second 5 ba tayi kan kujerar ba ta zame zuwa k'asa tana fad'in "Bari nayi serving naka" shi bema jita ba dan gaba d'aya hankalin sa ya tafi kan Ayrah ne, tunda ya baro makarantar ya kasa dena tuno kyakykyawar fuskar ta, gaba d'aya ta chanja, duk da dama tun tana yarinya kyakykyawa ce amma yanzu ta k'ara wani shahararren kyau kamar ita tayi kan ta, se dae har yanzu halin ta na nan, ga6untar nan da shagwa6ar nan har yanzu babu abinda ya ragu, tilas abinda ya tuna d'in ya sanya shi sakin sassanyan murmushi yana gyara zaman sa kan kujerar da yake, Muneerah data d'aga kae ta kalle shi taga murmushin da yayi, abinda yake da tsada a wajen sa, se gashi yau kusan zata iya cewa babu dalili yayi shi, seta samu kan ta da gyara zaman ta tana murmushi dan ita ta d'auka da ita yake "Yaya Daddy ya maka magana kuwa?" ta katse masa tunanin tana fatan Daddyn ya masa magana kuma ya kar6i zancen hannu bibbiyu, da mamaki ya d'an kalle ta sannan ya d'auke kae "Magana? Anya kuwa!" ya fad'a cikin er basarwa, seta yamutsa fuska sannan tace "Ohk toh ka sauko kaci abincin mana" ta fad'a tana cigaba da satar kallan sa ganin da tayi yanzu babu wannan murmushin akan fuskar ta sa, iska ya furzar daga bakin sa dan shi kam kwata kwata baya jin wata yunwa, toh wata ma yunwa zeji bayan gaba d'aya hankalin sa da tunanin sa na wajen Ayrah ne "Ban jin yunwa fa" ya fad'a yana zuba mata idanun sa, cikin er rawar murya ta furta "Haba mana Baby, pls kaci kada ka kwana da yunwa!" ta fad'a cike da kulawa kamar itace zata kwana da yunwar bashi ba, baya son dogon zance kuma ya k'agu ta fita dan yana jin idan har ta k'ara wasu mintuna bata fita ba toh ze tashi ne ya bar mata d'akin ita d'aya, dan haka ya furta "Ohk.. zaki iya tafiya, se da safe.." kallan sa ta cigaba dayi dan ita kam sam bata gajiya da kallan sa, jin shiru ya sanya shi sake fad'in "Ko na bar miki d'akin ne?" yayi maganar in a serious tune, da sauri ta mik'e sannan tace "Ohk bye luv, kayi bacci lafiya.." ta fad'a tana cigaba da kallan sa, ba tare daya kalle ta ba ya furta "Ohk" ya k'arasa maganar yana janyo wayar sa dake gefen sa, babu yadda ta iya haka ta fice daga d'akin zuciyar ta a cunkushe, ita ta k'agu kawae ayi auren nan kowa ma ya huta. Number ta ta ya lalubo ya danna kira, a 6angaren ta tana kwance kan gadon ta hannun ta rik'e da wayar ta ta tana jiran kiran sa tun d'azun, ganin kira da wata sabuwar number ya sanya ta tashi zaune da sauri tana kallan jerin gwanon numbobin dake shimfid'e reras akan wayar ta ta, kamar yadda yake special haka number sa ma take special, haka kawae taji a jikin ta shi d'in ne dan haka ta sake kallan gadon su Jidda taga duk bacci suke sannan ta d'aga tana karawa a kunnen ta, kafin yace komae tace bayan ta tura bakin ta daga inda take "Se yanzu ma zaka kira?" murmushi yayi daga inda yake yana kishingid'a a inda yake kwance sannan yace "Am sorry.." "Naqi ni dae, Allah kuwa tun d'azu fa nake jira ka kira" wani murmushin ya sake yi mara sauti yana karanto zallahr k'uruciyar dake tattare cikin maganar ta, da alama ko soyayya za'ayi da ita ba zata zama cikin mak'aryata ba, cikin k'asa da murya ya furta "Amin afuwa Uhmm? Raj ne fa" ya fad'a da er tsokana a maganar sa, se tayi murmushi kawae "Ina Umma? ina Abba? Ina Yah Sadeeq?" yayi maganar kamar ba Rk ba, seta sake gyara zama sannan tace "Alhamdulillah kowa lafiya k'alau, ina Abbun ku" "Abbu yana lafiya.." "Raj!" ta fad'a dan ta k'agu ta masa tambayar data tsaya mata arae sosae "Na'am" ya fad'a a nutse "Kae likita ne?" murmushi yayi daga inda yake sannan yace bayan ya d'an lumshe idanun sa kad'an "Yeah! likita ne, ki gyara zama na baki labarin rayuwa ta tun bayan rabuwar mu" kamar tana kusa dashi ta shiga gyara zama, dae_dae lokacin da Bahijja ta farka daga bacci saboda wani fitsari daya matso ta, ta kalli Ayrah dake zaune kan gadon ta sannan ta furta "Ayrah" cike da mamakin ganin ta, da sauri Ayrahn ta juyo tana kallan ta, se dae ba tace komae ba har Bahijjan ta shige toilet d'in, babu dad'ewa ta fito memakon ta nemi waje ta kwanta seta zauna tana cigaba da kallan Ayrah, haushi ya kama Ayrah ta had'e face d'in ta tsaff, sannan cikin had'e ran dae ta furta "Gobe zamu yi wayar" bata jira yace komae ba ta katse wayar sannan ta juya ta kwanta tana jin kamar ta tashi ta rufe Bahijja ta duka, cigaba da zama Bahijjan tayi dan so take ta gane da wanda take waya saboda abu ne da basu ta6a gani ba a wajen Ayrahn tunda tazo ba, kamar wadda aka tsikara ta janyo wayar data wulla gefe ta lalubo number Yah Sadeeq ta danna kira, se dae

Table of Contents

Chapters

70 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70