Chapter 13
Chapter 13
kallan d'an uwa, kamar d'an uwan da suka fito ciki d'aya, yana ganin kamar ya samu wanda ze iya kular masa da dukiya koda baya wajen, wanda ze rik'e masa amana ko da a bayan idanun sa ne, se dae kashh ashe be sani ba duk wannan a banza ne, ashe Abbun ya yaudare shi ne da halayen bogi, yayi amfani da yaddar daya bashi ya yanke shi son ransa, ashe tun farko akwae k'udurin da yake son cikawa shiyasa ya kwantar da kae, ya nuna kamar shi na Allah ne "Meyasa zaka min haka Kabeeru?" Abba ya fad'a a fili yana dafe da k'irjin sa da har lokacin yake jin ya masa wani irin nauyi. ... Bin Abban tayi da kallo sanda ya shigo cikin gidan, a hankali ta bud'e baki ta amsa sallamar sa da taji yayi ta a hankali, seta mik'e tana goge hannayen ta daga cikin ruwan d'aurayar wanke wanke ta k'araso tana kallan sa tace "Sannu da zuwa Abban su" "Yawwah.." ya fad'a yana yin gaba, haka nan kawae taji zuciyar ta ta buga, seta lumshe idanun ta a ranta tana fatan Allah yasa ba wani mummunan abun ne ya faru ba, a hankali ta yaye labulen d'akin ta shiga da sallama seta nemi gefen gadon ta zauna tana cigaba da kallan sa tace "Ko na had'a maka ruwan wanka ne?" girgiza kae Abba yayi kafin yace "A'ah" cike da damuwa ta furta "Abban su lafiya dae koh?" Abba ya runtse idanun sa yana jin zafin abinda ze fito daga bakin sa "Kabeeru.." tun kafin Umma taji k'arshen maganar ta dafe k'irjin ta dan ita ta d'auka ko wani abun ne ya samu Kabeerun, se dae sa6anin abinda tayi tsammani se taji Abban yace "Kabeeru yaci amana ta, ya tattara kayan sa ya gudu da kud'ad'en nan da kuma takaddu na.." runtse idanun ta Umma tayi a ranta tana fatan ta bud'e idanu taga ba gaskiya bane abinda take ji a kunnuwan ta ko kuma ya kasance mafarki ne take yi, se dae har zuwa sanda ta bud'e idanun ta se taga Abban a yadda ta barshi "Anya kuwa Abban su?" ta fad'a cikin k'arfin gwuiwa, murmurshin takaeci Abba yayi wanda ake cewa yafi kuka ciwo kana yace "Tabbas haka ne, ban dawo gidan nan ba seda na bincika, har unguwar su naje aka tabbatar min a jiyan shima ya bar garin shi da iyalin sa" "Inna lillahi wa inna ilaehi rajiun" Umma ta shiga nanatawa tana kallan Abban tana jin da wani ne ya fad'a mata wannan zancen har abada ba zata ta6a yarda ba "Abban su.. Abbun Raj fa kake magana, mutumin da kullum zancen sa a bakin ka baya wuce na alkhaeri kirkin sa da kuma rik'on amanar sa, koda sau d'aya ban ta6a jin ka fad'i aebun sa ba, se dae gashi yau ina jin wata magana mara dad'i akansa tana fitowa daga bakin ka, Abban su kana nufin duka kud'ad'en nan ya gudu dasu don Allah.." "Toh ina suke Ruk'ayya? ae yanzu kinga irin sakayyar da yayi min na d'aukar amana ta da nayi na bashi koh?" wani numfashi me zafi Umma taja ta fesar sannan ta sake yin salati, daga nan kuma tayi shiru ta kasa cewa komae, dan kwata kwata ma bata san me za tace ba, mamakin ta d'aya yadda Abban da kansa yake fad'in Abbu ya gudu da kud'in sa, abin kamar almara, gaba d'aya k'wak'walwar ta ta tafi can tana mata bitar alak'ar Abban da kuma Abbu.... Sanda Yah Sadeeq yaji zancen nan seda yayi kuka sosae cikin tausayin Abban nasa, yana tuna irin gwagwarmayar da Abban yasha kafin ya samu wannan damar amma lokaci d'aya wani yazo yayi masa awon gaba da komae nasa, ya kuma yi alawadae da hali irin na Abbu, ya kalli Umma dake zaune ta jinginar da kanta kan kujera kamar me tunani "Umma bansan meyasa ba ni gaba d'aya daga shi Raj d'in har mahaefin sa ba suyi min ba Umma, Umma mutumin nan ya cuci Abba ya cuce mu, Allah ya isar mana wallahi" kallan sa Umma tayi, bata jin komae idan ta tattauna magana da Yah Sadeeq d'in dan k'ananun shekarun sa basu hana shi hankali ba, idan yayi wani abun kamar wani babban mutum tace "Bama seka fad'a ba Sadeeq, sakayya kam se Allah yayi mana ita, shi kuma yaje ya gani idan haram wata abace" dae_dae lokacin da Ayrah ta shigo d'akin ta k'arasa ta kwanta akan cinyar Umma kamar zata fashe da kuka ta furta "Umma Raj.." Yah Sadeeq dake zaune kujerar kusa da Umma ne ya janyo ta da k'arfi cikin fad'a yace "Wallahi idan kika sake mana maganar Raj a cikin gidan nan sena miki duka kinji na fad'a miki" ya fad'a yana d'aga hannu kamar ze mare ta, kuka ta fashe dashi kamar wadda ya ida dukan nata, Umma ta kae hannu ta rik'o ta ta d'auke ta zuwa kan cinyar ta ta kwantar sannan ta kalli Yah Sadeeq tace "Ita me ta sani? Wannan fad'an babu abinda ze janyo se rigimar ta kasan hali dae" "Umma ba duk itace ta janyo ba, da bata san Raj d'in bama ta yaya Abba ze had'u da baban sa ballantana har ya cuce shi" Umma na cigaba da rarrashin Ayrah tace a nutse "Ya zamu yi da k'addara Sadeeq?" ... Sau wajen 3 Umman na farkawa daga baccin da babu dad'i cikin sa se tarin damuwa da tunanun nuka tana ganin Abban zaune babu alamar zeyi bacci, se daga k'arshe dae ta kasa shiru tace "Kayi hak'uri Abban su don Allah kayi bacci, kada damuwa ta maka yawa.." Abba ya lumshe idanun sa, baya tunanin ko awa nawa zeyi zae iya yin wani bacci, amma dan ya kwantar mata da hankali ya sanya shi fad'in yana gyara zaman sa "Toh shikenan, yanzu zan kwanta kiyi baccin ki.." ... Wasa wasa wajen kwana 3 kenan Abban baya samun yin bacci, shi kansa besan dalili ba dan ko yayi niyyar yin baccin baya samu yazo masa, se dae kawae ya kwanta yayi ta tunani, zuwa lokacin tunani ya zama kamar wani mahad'in rayuwar sa ne dan kuwa in dae ze zauna toh fa zeyi tunanin nan ne, har kuma zuwa lokacin mamaki yak'i sakar shi, ga Kabeerun da kullum da shi yake kwana yake tashi, duk da guduwa da kud'in da Abbu yayi ya masa zafi amma be kae zafin yadda ya d'auki duk wata yadda tasa ya dank'awa Abbun ba amma daga k'arshe yaci amanar sa, ya yaudare shi, gefe guda kuma tunanin halin da zasu shiga a yanzun yake, yana ganin kamar rayuwa na gab da juya musu baya, babu sana'a, babu takaddar da ze iya zuwa ya nemi aeki, ga kud'in da Alhaji mato yake bin sa, duka tunanin sa yafi karkata nan 6arin ne "Allah ka bani ikon cinye wad'annan jarabobin" Abban ya fad'a akan la66an sa, yana jin wani irin rauni a tattare dashi.... https://chat.whatsapp.com/DH0EIIWNPnSICxsGgh2DSd *♡☆ZAZZAFAR KAUNA☆♡* *FREE BOOK* *CHAPTER ONE* ✨ *TITAN'S OF TALENT* ✨ Page 007_008 ___Washe gari wajen k'arfe 8 na safe Abba na zaune cikin parlourn yana yin iya bakin k'ok'arin sa dan kada iyalan nasa su fahimci damuwar da yake ciki se ga kiran Alhaji
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70