Skip to content

Chapter 32

Chapter 32

Zazzafar Kauna Book One Complete Hausa Novels 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

bakin ta gaba, iska ya d'an fesar daga bakin sa sannan yace "Ohh am sorry.." yayi maganar yana d'an dakatawa, yana tunanin tsayin maganar da zeyi, ya san tabbas ze dad'e yana yin ta abinda ya tsana kenan, dan haka ya janyo rubber water ya tsiyaya cikin tambulan ya sha, ya d'an sauke numfashi a nutse sannan ya d'ora da "Tun bayan rabuwar mu, Allah ya bud'ewa Abbu sosae, harkokin da yake yi sosae suka samu kar6uwa a wajen mutane, ban san meyasa tun bayan rabuwar mu daga mu har ku babu wanda ya sake waewayar wani ba, bansani ba, abinda kawae na sani na sha tambayar su Abbu ku amma bana samun cikakkiyar amsa wadda zan kama daga wajen sa, tun ina tambayar sa har nazo na dena tambayar sa, se dae har lokacin kina nan manne a rae na, ina jin ki ne acan cikin zuciya ta wanda hakan ne yasa na kasa manta ki a duk tsayin shekarun nan, a cikin wannan lokacin ne na gama secondary school kullum arzik'in Abbu yana yin gaba, dan haka dana tashi yin University ba'a nan nayi ta ba, sena tafi can Cyprus na karanci Medicine, yanzu haka ni cikakken likita ne, muna zaune anan cikin garin Kano saboda harkokin Abbu da suka cigaba, yanzu haka ina da asibiti na kae na wanda shima Abbun ne ya bud'e min, abinda ya kawo ni garin nan kuwa, sanadin k'anin mahaefi na ne da nazo sanda ze bud'e wani Company, tunda nazo kuma Abbu yace kar na zauna haka nan shi ya nemar min wannan lecturing d'in cikin makarantar nan duk da ni ba za6i na bane, da son raena ne aekin da nake kawae ya ishe ni, toh dae dan farin cikin Abbun yasa na fara lecturing d'in, se dae yanzu maganar da nake miki tuni Daddy (k'anin Abbu) ya gama bud'e Companyn komae ya kammala, dan haka ina saka ran ni kam daga wannan semester na gama koyarwa a makarantar nan... And.. ina me tabbatar miki In Sha Allah duk sanda muka had'u zan baki labarin a nutse" ya k'arasa maganar yana sauke wani gauron numfashi lokaci guda kuma yana 6alle murfin gorar ruwan daya ajje ya shanye tass sannan ya ajje ta yana sauke numfashi, dariya ya bata daga inda take zaune jin yadda yake sauke numfashi kamar wanda yayi wani aekin wahala, se dae kuma a ran ta tana cigaba da mamakin rayuwar Rk d'in, lallae Allah abin godiya ne da kuma d'aukaka, dan kuwa shine me yin yadda yaso a kuma lokacin daya ga dama "Uhmm, fad'a min kad'an daga naki kafin mu had'u" sauke numfashi Ayrah tayi sannan a hankali ta shiga sanar dashi makarantar da tayi da er gwagwarmayar da tasha har zuwa yanzun, duk da ba wasu shekaru ne da ita na azo a gani ba, ga kuma ga6un ta dake damun ta, amma duk yadda take ganin Raj d'in take kuma jin sa a jikin ta bata sanar dashi abubuwa da dama daga rayuwar su ba wanda take ganin kamar sirrin su ne wannan da ba kowa ya kamata ya sani ba, shiru Rk yayi yana nazarin maganganun Ayrah a ran sa yana sake tsarkake sunan Allah "Ikon Allah" kuwa ya maemaeta yafi sau nawa "Akwae wata magana dana ke so muyi, amma kafin nan ina so ki gama exam kafin ki koma gida.." "Wace maganar toh?" ta fad'a kamar za tayi kuka, murmushi me sauti yayi sannan yace "Ae nace se kin gama exam tukunnah" shiru tayi tana tuna yanayin Rk d'in a cikin aji da kuma yanzun kamar bashi bane, kamar mutum biyu ne masu kama d'aya wanda wancan da yake shigar musu aji daban shi kuma wannan da suke waya daban "Promise?" ta fad'a tana d'aga yatsan hannun ta kamar yana gaban ta "Yeah.." "Ohk". Wayar sa da tayi k'ara bayan ajiye wayar Ayrah yabi da kallo, ji yayi kamar kar ya d'aga dan a yanzun yana so ne ya dinga samun lokacin daze zauna kawae ya dinga hasaso kyakykyawar fuskar ta, kallan wayar yayi dan ganin me kiran nasa, seya kae hannu ya d'auki wayar ganin Daddy ne ke kiran, ya kae kunnen sa da sallama d'auke a bakin sa "Likita kana ina ne?" "Ina d'aki" yayi maganar cikin girmamawa "Ohk ka same ni a d'aki na idan babu abinda kake" babu musu ya amsa da "toh" sannan ya mik'e bayan ya jefa wayar a aljihun sa ya zura takalmi ya fito daga d'akin nasa cikin nutsuwa. Kae tsaye parlourn Daddyn ya wuce, a hankali ya zura kan sa ciki yanzun ma da sallama a bakin sa cikin nutsatsiyar muryar sa, amsawa Daddy yayi yana kallan sa lokacin da yake k'ok'arin zama a k'asa "Tashi ka zauna akan kujera magana nake so muyi ae" seya d'an yi murmushin nan nasa me tsada wanda ke sake fito da aenahin tsagwaron kyawun sa ya zame akan kyakykyawan Carpet d'in dake shimfid'e a k'asan d'akin yace "Daddy nan ma ya isa" murmushi Daddy yayi a ransa yana sake jaddadawa kan sa lallae abinda suka yanke ba suyi laefi ba "Amm yaushe zaku yi hutu ne?" seda ya d'an yi shiru sannan yace "Ina tunanin baza mu wuce 1 month ba" "Toh Allah ya taemaka, me kake shirya mana zuwa lokacin?" yamutse fuska yayi dan shi sam bema fahimci maganar Daddyn ba dan haka ya furta abinda ke ran sa "Daddy ina ganin zan ajiye lecturing d'in nan gaskiya am tired" ya fad'a dan da gasken ya gaji da lecturing d'in musamman daya kasance dama ba za6in sa bane, ga kuma muhimmiyar maganar da yake so daya koma yayi wa Abbun magana akae, wadda yake had'e da albishir d'in daze fad'a musu su duka cewar bayan tsawon shekarun nan ya had'u da Ayrah, wanda hakan na nufin Abbu ze had'u da Abba, may be ma abotar su ta da ta dawo sabuwa duk da be san abinda yasa kowa yayi watsi da d'an uwan sa ba "Haba haba dae Raj ka gaji kuma?" jinjina kae yayi ba tare daya kalli Daddy ba "Toh ya za kayi da Abbun ka kuma?" Daddy ya tambaya yana kallan sa "Zan same shi da maganar In Sha Allah" "Toh hakan ma yayi, seka maeda hankalin ka waje guda kenan, Allah ya taemaka.. Ameen" shiru ne ya biyo baya Daddy na tunanin ta inda ze farawa Rk maganar se can dae yayi k'arfin halin fad'in "Kana jina koh?" "Ehh.." Rk ya fad'a, kafin Daddy ya kae ga cewa komae wayar sa ta shiga ruri, seya janyo wayar yana kallan me kiran, da sauri ya kalli Rk yace "Raj je ka, za muyi maganar In Sha Allah, zan yi waya ne yanzun" jinjina kae kawae yayi ba tare da yace komae ba ya mik'e ya fice daga d'akin. ... A d'aya 6angaren kuwa Umma ce ta fito daga d'akin ta, dae_dae lokacin da Yah Sadeeq ke tsaye bakin k'ofar d'akin sa hannun sa dafe da k'ofar d'akin yana sauke numfashi kamar wanda yayi tsere, da sauri Umma ta k'arasa tana kallan sa "Sadeeq lafiya kuwa?" tayi maganar tana rik'o shi "Haki kake?" ta fad'a sanda ta gama d'ago shi tana kallan fuskar sa, da sauri ya k'ak'alo murmushi ya wanzar

Table of Contents

Chapters

70 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70