Skip to content

Chapter 37

Chapter 37

Zazzafar Kauna Book One Complete Hausa Novels 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

ya bud'e wajen me zaman banza ya shiga ya kalle shi cike da girmamawa yace "Yalla6ae daka bari dae ko zuwa goben ne kada su fahimci wani abun!" wani kallo Alhajin ya jefa masa se kuma yayi murmushi wanda ya sake k'ank'antar da jajayen idanun sa "Tunda kaga zan yi driving da kae na kasan abu ne me muhimmanci, na kasa jurewa gwara naje ko nan sati 1 ne a d'aura mana aure idan yaso seta cigaba da karatun a cikin gida na" jin maganar da Alhajin ya fad'a ne ya sanya Muttala jinjina kae kawae, bece komae ba har zuwa sanda Alhajin ya tayar da motar sa suka fice daga gidan. A k'ofar gidan yayi parking motar ta sa, sannan ya kashe ta ya kalli Muttala da tunda suka fara tafiya har yanzu be sake cewa komae ba yace "Yi mana sallama da shi pls" seya kalli Alhajin sannan yace bayan ya girgiza kae "A'ah fa Yalla6ae kada ka manta sirikin ka ne, ina ganin gwara ka fito ko kan dakalin can ne seka zauna" Muttala ya fad'a yana nuna wani dakali dake a k'ofar gidan dake kusa da nasu Ayrah, shiru Alhajin yayi kamar ba zece komae ba se kuma can yace "Toh yanzu kae dae je ka" yayi maganar yana sanya hannun sa ya bud'e k'ofar, kusan a tare suka fito, Alhajin ya kalli wajen yana yamutsa fuska sannan ya zauna yayin da Muttala ya tsaya k'ofar gidan ya k'wala sallama, daga can cikin gidan Abba ya amsa yana mik'ewa ya zura takalmin sa ya fito daga d'akin nasa, k'arasowa yayi yana kallan Muttala ganin da yayi be shaida fuskar ba, se dae ya mik'a masa hannu suka gaesa sannan yace da d'an murmushi kan fuskar sa duk da yanayin da yake ciki a yau d'in na damuwa "Se dae ban shaeda fuskar ba" murmushi shima Muttalan yayi sannan yace "Ehh dama baka sanni ba gaskiya, ga can wanda yazo wajen ka akan wata magana me muhimmanci" yayi maganar yana nuna Alhajin dake zaune kan dakalin yana kallan wani wajen, saboda k'arancin hasken dake a wajen ya sanya Abba be iya hangar fuskar sa ba, seya dawo da duban sa ga Muttala yace "Toh ikon Allah" ya fad'a yana yin gaba zuwa wajen da Alhajin ke zaune, dae_dae lokacin da Abban ke dab da k'arasawa wajen Alhajin haske ya kawo a wani k'wan lantarki dake k'ofar gidan dake kallan nasu, hakan ne ya bawa Abba damar ganin fuskar mutumin da akace shi ke son magana dashi, cikin son sake tabbatarwa ya sake bud'e idanun sa dan ganin da gaske fuskar da yake gani ita d'in ce ko kuwa dae? Shi kan sa Alhajin kallan Abba yake with shock all over his face, se yaji gaba d'aya jikin sa ya d'auki wani mahaukacin rawa, ya had'iyi wani yawu da k'yar sannan yace bayan ya mik'a masa hannu "Kae ne mahaefin Ayrah?" Alhajin ya fad'a yana kallan Abba, a ran sa yana tuna cikakken sunan Ayrahn, tabbas da gaske shine mahaefin ta, amma dae gwara ya tabbatar ta hanyar ji daga bakin Abban, da mamaki Abba ke kallan sa jin maganar da yayi, meya kawo zancen Ayrah a tsakanin su kuma? "Meya kawo ka k'ofar gida na?" Abba ya fad'a yana kallan sa fuskar sa a d'inke tsaff, jikin sa ya sake wani sanyi wata zufa na karyo masa yace bayan yayi k'asa da muryar sa "Kayi hak'uri mu zauna sena maka bayani, wallahi ba tashin hankali ne ya kawo ni wajen ka ba" "Alhaji Mato!" Abba ya fad'a cikin er d'aga murya, a ran sa Abba na sak'a lallae duk abinda Alhaji Maton yazo da shi me girma ne "Bani da lokacin 6atawa, idan ba kada abin fad'a na shige gida" Wani yawun Alhaji Mato ya sake had'iyewa shi kan sa yana tunanin ta ina ma ze fara sanarwa da Abban son er sa yake? So na aure, ganin dae da gaske Abban yake idan bece wani abu ba ze iya tafiya ya k'yale shi ya sanya shi fad'in "Wallahi abin alkhaeri ne ya kawo ni, d'iyar ka na gani kuma ina son ta da aure shine kawae abinda ya kawo ni, kuma kada ka damu wancan lokacin akasi aka samu na fad'i magana saboda 6acin rae amma zan dawo maka da kud'in daka biya ni, kuma zan baka sana'ar da zaka dinga yi kana.... " "Dakata Alhaji Mato" Abba ya fad'a bayan ya d'aga masa hannu, zuciyar sa na wani irin zafi da jin kalaman Alhaji Maton na son zuciya "Kada na sake ganin k'afar ka a k'ofar gidan nan, kud'i kuma har abada na riga na biya ka kuma bazan ta6a kar6a ba, saboda haka kada ka sake tunanin zan d'auki 'ya ta in baka ita bayan na san wanene kae, ka cire wannan ma a cikin ran ka" daga haka Abba ya juya yana jin wani jiri jiri na d'ibar sa kamar ze fad'i, da kallo Alhaji Mato ya bishi zuciyar sa na wani irin tafasa, lallae yau ya kuma yadda Abban matsiyaci ne, be san me ake kira da arzik'i ba, har yanzu dae yana zaune cikin duhun kae, har abada ma baya tunanin Abban nada rabon arzik'i a rayuwar sa, tunda gashi yanzu arzik'in ya biyo shi har gida amma ya saka k'afa yayi fatali dashi saboda wani banzan ra'ayin sa na rik'au. Seda Abba ya shiga gida sannan Muttala ya kalli Alhaji Mato cikin mamaki yace "Yalla6ae wae dama ka san shi ne?" "Bar shashasha me k'ashin tsiya, arzik'i na kiran sa yana guduwa, wani k'aramin abu ne ya ta6a shiga tsakanin mu amma da yake zuciya ce dashi irin ta kafirae ya kasa mantawa, toh se yayi tayi ae, ba dae er sa bace na gani ina so kuma sena aure ta, dan kuwa ban ta6a ganin abu inaso ban same shi ba, kuma baza a fara akan ta er talakawa ma da ita ba, ko da amincewar sa ko babu wallahi sena aure ta.. Wuce muje.." ya fad'a yana huci sanda ya k'arasa ya bud'e motar sa ya shige, Muttala ma ya shiga, Alhaji Mato yaja motar da wani irin gudu kamar ze tashi sama. .. Akan la66an sa kawae Abba yayi sallamar dan baya jin ze iya d'aga murya sosae saboda yadda yake jin jikin sa, da kallo Umma ta bishi dashi sanda yake shigowa cikin d'akin, seta mik'e da sauri cikin mamakin yadda taga yanayin nasa ya sake chanjawa fiye da d'azun "Abban su" shine abinda ta iya furtawa tana cigaba da kallan sa, Abba ya nemi waje ya zauna amma har lokacin bece komae ba, fita Umma tayi ta d'ebo ruwa me sanyi cikin randa sannan ta koma d'akin ta mik'a masa a nutse tace "Gashi" babu musu Abban ya kar6a kofin ya sha ruwan sosae sannan ya ajiye shi yana sauke ajiyar zuciya "Don Allah ka dena d'aga hankalin ka haka nan, in dae akan wannan maganar ne nayi mata bayanin dalilin ka na hana ta auren sa" girgiza kae Abba yayi sannan yace bayan yayi murmushi me ciwo "Ba wannan kad'ae ba, yanzu fitar da nayi wae neman auren Ayrah akazo yi" "Ikon Allah.. Amma shine ka shiga damuwa haka?" Umma ta fad'a tana sake

Table of Contents

Chapters

70 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70