Skip to content

Chapter 34

Chapter 34

Zazzafar Kauna Book One Complete Hausa Novels 1,198 words 0 views Progress saved
Download Book

sannan tayi wucewar ta kan gadon ta, dukan su suka bita da kallo kafin Ruks ta jinjina kae tana ta6e baki cike da mamakin halin Ayrahn "Cha66 d'i jam!" Jidda ta fad'a tana cigaba da kallan Ayrah. Ta 6angaren Ayrah kuwa ba ta bi ta kan kowa ba ta zura hijab ta shige toilet, kamar wasu sokaye suka sake bin ta da kallo, yarinyar ta chanja musu sosae, duk da dama tun can sun fahimci miskila ce ta k'in k'arawa, amma yanzu abin yayi gaba sosae, dole su jira Abeeda dan su tabbatar da abinda ta fad'a musu, duk da abin ne akwae wuyar yadda. ... Babu nisa su Ayrah suka yi last paper d'in su ya zamana se komawa gida kenan. A 6angaren Abba kuwa se Allah ya taemake shi lokacin da ze je d'auko Ayrahn ya kar6i albashin sa, dan haka ba k'aramin dad'i yaji ba. Ranar daze tafi ya gama shiryawa cikin manyan kaya na wani yadi, daga d'aki ya fito lokacin Umma na d'akin Yah Sadeeq ta kae masa abinci, ta kalle shi tana murmushi tace "An fito kenan?" shima murmushin ya maeda mata sannan yace "Wallahi kuwa zamu wuce" yayi maganar yana d'ora hular sa samfurin zanna bukar akan sa "Toh Allah ya tsare.." "Ameen Ameen.. amma kafin nan zan biya nayi wa Baban Zaenab ya me jiki, saboda jinjirar da aka haefa masa da aka sallamo su daga asibiti" "Toh ayi mata sannu, gobe idan Allah ya kaemu se mu shiga mu duba ta" "Toh madallah" Abba ya fad'a yana yin gaba, seda ya shiga d'akin Yah Sadeeq dake zaune akan gadon sa yana danna er k'aramar wayar sa, Abba yace "Sadeeq!" "Na'am Abba zaka wuce ne?" "Ehh ba kaci abincin ba" d'an murmushi kad'an yayi sannan yace "A'ah yanzun dae zan ci, Allah ya dawo daku lafiya Abba" "Ameen_Ameen" Abban ya fad'a yana mik'ewa ya fice daga d'akin. Kae tsaye seda ya fara zuwa ya gaeda mara lafiyar sannan ya dawo ta hanyar gidan sa dan wucewa titi ya nemi abin hawa, a k'ofar gidan nasu yaga wata mota me kyau, tunda suka gan shi suka sauke glass d'in motar, wani malamin su Ayrah ya sauko ya k'arasa da murmushi kan fuskar sa yace "Barka da wannan lokacin Alhaji" yayi maganar yana mik'awa Abba hannu, shima Abban mik'a masa hannu yayi suka gaesa yana amsawa da "Barka dae, ashe kae ne?" "Wallahi kuwa, ina zuwa haka ne?" Abba yace "Zan je d'auko Ayrah ne kasan da yake sun gama exam" murmushi malamin nasu yayi sannan yace "Ahh toh ae dama daga makarantar ne aka aeko mu muzo mu d'auke ka a motar nan mu wuce can makarantar" "Toh Ikon Allah" Abba ya fad'a yana bin motar da kallo, dan sosae abin ya cigaba da bashi mamaki, tabbas makarantar tasu Ayrah mutane ne masu karamci da sanin ya kamata "Allah ya saka da alkhaeri" Abba ya fad'a "Ameen Ameen.. Muje koh?" ya fad'a yana yin gaba sannan Abba ya rufa masa baya zuwa wajen motar, shi malamin ya shiga gaba yayin da Abba ya shiga baya, a haka driver ya soma driving babu dad'ewa suka d'auki hanyar Zaria. ... Ayrah ta gama had'a komae nata ta kammale shi inda ya kamata, wani irin d'oki ne keta d'awaeniya da ita, ji take kamar tayi tsuntsuwa ta gan ta a Kano taga Abban ta, Umman ta da uwa uba kuma Yah Sadeeq d'in ta, gaba d'aya ta kasa sukuni tun d'azun wayar ta ke hannun ta tana jiran kiran Yah Sadeeq ko Abba, Jidda ce kawae a d'akin tun d'azu su Bahijja suka fita ko sallama ba suyi ba, bata k'ara minti 5 ba kuwa sega kiran Abba a wayar ta ta, zumbur ta mik'e dan dama k'iris take jira ta d'aga wayar tana karawa a kunnen ta "Abba kunzo?" ta fad'a tun kafin Abban yace komae, murmushi Abba yayi kana yace "Qwarae kuwa ke muke jira yanzu haka" jin da tayi yace suke ya sanya ta tunanin tabbas shi da Yah Sadeeq suka zo dan haka da sauri ta kalli Jidda tace "Mu dae mun tafi" ta fad'a tana Allah Allah Jidda ta amsa ta fice daga d'akin "Ba zaki tsaya kiyi sallama dasu Ruks ba?" 6ata fuska tayi sannan tace bayan ta girgiza kae "A'ah ki fad'a musu na tafi ni dae, se an dawo hutu bye.." ta fad'a tana ficewa daga d'akin "Toh Allah ya kaemu" shine abinda Jidda ta fad'a tana bin Ayrah da kallo sanda ta fice daga d'akin cikin d'oki kae seka rantse tafi shekara ba taga Abban ba. Sosae taji dad'in ganin Abban dan murna gaba d'aya ta kasa dena murmushi se dae tayi mamakin rashin ganin Yah Sadeeq tare da Abban, dan haka ta kasa shiru seda tace "Abba Yah Sadeeq fa?" "Yah Sadeeq na gida, kin san yanayin aekin su hutu yake shiyasa.." se tayi murmushi, a yanzu da taga Abba se d'okin nata kuma ya koma na son ganin Yah Sadeeq da Umma, suna tafiya a hanya suna hira sosae cike da farin ciki da kewar juna, Abban ya zage yana jan d'iyar ta sa da hira, se dae da yake basu kad'ae ne a cikin motar ba ya sanya yawanci hirar tasu bata wuce akan karatu. ... Da wani sauri Bahijja ta turo k'ofar d'akin hannun ta d'auke da wayar Abeeda, Abeeda da Ruks suka biyo bayan ta, idanun ta a warwaje ta furta "Ina Ayrah take?" tayi maganar cikin d'aga murya, da mamaki Jidda ke kallan ta yadda take a wani birkice kamar mahaukaciya tace "Meya faru?" "Ke dae ina take kawae?" "Yanzun nan aka zo aka d'auke ta" Jidda ta fad'a sannan ta d'ora da "Pls meya faru?" komawa Bahijja tayi ta zauna, tana tuna yau da taga Ayrah a cikin d'akin nan babu abinda ze hana ta shak'e ta ko zata ji sauk'in abinda take ji a cikin zuciyar ta, kar6ar wayar hannun ta Ruks tayi sannan ta mik'awa Jidda tace "Kalla ki gani" hannu Jidda ta saka ta kar6i wayar sannan ta shiga kallan hoton sannu a hankali, tana kae hannun ta tana zooming, ta kae wajen minti 1 tana kallan hoton sannan ta d'ago ta kalle su cike da mamaki akan fuskar ta "Kenan abinda Abeeda ta fad'a gaskiya ne?" tayi tambayar tana kallan su su duka, kamar wata k'adangaruwa Bahijja ta shiga girgiza kae tana jin kamar ta rusa ihu "Shegiyar yarinya ta cuce mu, dama seda nayi tunanin kyawun ta ze iya rud'ar shi, ashe mu bamu sani ba ma sun dad'e suna soyayyar su amma shegiyar yarinya seta dinga nuna kamar ma tsanar sa tayi, bamu sani ba ashe wawaye sakarkaru ta maeda mu, k'aramar yarinya tayi wasa da tunanin mu kenan?" ajiyar zuciya Jidda ta sauke kana tace "Lallae kam, ni kae na abin ya bani mamaki wallahi, yaushe muna zaune har hakan ta faru bamu sani ba? Ya akayi hakan?" tayi maganar cike da mamakin dae, girgiza kae Ruks tayi kafin tace "Wallahi ku bari kawae, ni dan mamaki ma na rasa wane tunani ya kamata nayi" Abeeda tace "Ahh toh, ni kae na nasan amanar ku akaci shiyasa naga bazan k'yale ba gwara na sanar daku" "Aekuwa wallahi za taci uwar ta yarinyar nan"

Table of Contents

Chapters

70 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70