Chapter 79
Chapter 79
ya lumshe idonsa yanajin wata natsuwa na shigarsa shaidan na qoqarin tuno masa da abubuwa Yana yaqarsa daqyar yayi galaba akansa ya koreshi ta hanyar zarmewa wa tabe²nsa itakam lumshe idonta tayi banda hawaye Babu abinda takeyi ganin Yana qoqarin zaqewa Kuma tasan kowanne lkc Muneefah ko Jummai in sunji shiru zasu iya fitowa yasata janyewa. Kafin ta gama daidaita natsuwarta ya sunkuceta sai dakinsa ya azata a gadonsa ya turmusheta tana tureshi tana komai yaqi barinta sai rawar jiki yakeyi da ta murya Yana cewa “Mee.... Meenah.... please..... Long time banci ba wlh tunda nabarki banqaraci ba banqara sha'awar ciba sai da kika dawo rayuwata kibarni naci naji da...din...ki...." Batada mafitar data wucce qyaleshin duk da tanajin fargaba koda yake tasan duk masifar Rasheed baikai Kareem ba saidai shi dabanne Yana bata nutsuwar da takeji a ranta Babu me bata kamarta sambatunsa kadai ya isa gamsar da mace me gajeran zango, Rasheed ya mayar da qwalamarsa a wannan yammaci anci amarcin gaske taji a jikinta koda komai ya kammala gumi ta rinqa hadawa ga ciwon jiki tare sukayi wanka yanata narke mata kunyarsa ma ta kamaji saboda ta fahimci shi baya da kunya ko kadan akan wannan abun. Bayan sunyi wanka sukayi sallar magrib da ake binsu sukayi Isha sannan suka nufi dinning sukaci abinci yanata zubanta shagwaba itakam duk jikinta yayi sanyi ta dago idonta tace “amma Ya Rasheed ka fasa tafiyar ko?" Murmushinsa na Izza yayi mata yace “sai yanda ta yuwu" Miqewa tayi ta shige dakinta ta haye gado ta zauna ta zuba uban tagumi itakam ta tsorata da wannan al'amari batajin zata iya yarda ya tafi ya barta idan ta tuna da hakanma hawayenta nunkuwa sukeyi ita da kanta takeji ashe zuciyarta tashice har yanzu ashe Baffa'am dinta bashida na biyu har gobe a duniyarta to meye yasa da ta farajin haushinsa?" Jinjina kai tayi tana qissima ta yanda zata fara rayuwa cikin zulumi sai ta dauki wayarta kamar ta kira Kumbo Hami ta fada mata sai Kuma taga kamar bai dace ba haka ta rinqa saqawa da warwarewa har dare ya fara nisa ta shiga tayi wanka ta dawo ta kwanta abinka da farar fata idanunta har sun kumbura koda Jummai ta kawo mata Muneefah cewa tayi taje su kwanta tare ganin kwanciyar bazata kaita bane tasata tashi ta sake alwala ta dauki qur'ani tana karantawa tana hawaye. Shigowa yayi dakin mamaki ya cikashi jin shassheqarta ya kunna globe din da sauri yaganta rungume da qur'ani tana rera kukanta ya qarasa gareta ya zare qur'anin ya aje ya dagota ya mannata da jikinsa yace “meye kikewa kuka Meenah kinsani ko a baya bana qaunar kuka ko?" Maqalqaleshi tayi tana qarawa kukanta gunji tace “ni don Allah kace ka fasa tafiya kabarni wlh zanyi maka duk abinda kakeso" dariya tabashi sosai ya shafa kanta yace “to na fasa saime Kuma?" Rungumeshi tayi tana ajiyar zuciya tace “shikenan idan sun matsa ka bar musu aikin kawai kaji?" Daganta kai yayi ta shafa sumarsa tace “na gode Baffa'am...." Janta yayi suka zube a gado ya fara luguiguiceta ta saki masa jiki kuwa suka raya Daren da wata irin azababbiyar qauna me narkar da zuciya sun gurji juna sosai tanajin sabuwar qaunarsa na ratsata, tun daga wannan dare komansu ya fara saituwa cikin ruwan sanyi da dabara ya shawo kanta riritashi takeyi kamar qwai bata yarda ta tabashi saboda karma yaji yanason tafiya yabarta shima mugun tattalinta yakeyi Abu daya yaso Basu damuwa tanason zuwa Daura watanni sun fara nisa tanason taje taga Mom Amma fir yaqi tun tana lallabashi har Saida suka daina mgn ta daina kulashi da ya matsa mata sai ta kama kuka tace don yaga batada galibi ne batada uwa bata da uba shiyasa yakeson ya nuna mata Mom ba ita ta haifeta ba. Sosai ya fahimci Meenah yar sharri ce ta qaro wulaqanci dole ya shiryanta tafiya Katsina aikuwa tayita murna shikuma yayita kumburi zuciyarsa na basa kawai so take taje taga uwar mijinta ta tuno da ubar yarta Kareem idan zuciya ta raya masa haka sai kawai yaji koma me zatayi tayi bazai barta ba ranar data shirya tafi tun asuba take shiri yayi kwanciyarsa yaqi fitowa harta shirya ta shirya Muneefah ta shiga dakin nasa da sallama ya Amsa mata a ciki ta zauna tace “Baby na shirya banga kana shiri ba Kuma kace kaine zaka kaimu airport" iska ya furzar yayi miqa yace “ina zakije ne?" Da sauri ta dubesa tace “Ban fahimta ba Daura Mana" hade rai yayi yace ba yau ba..." Ai baigama rufe bakinsa ba ta miqe tana cewa “haba don Allah Ya Rasheed kada kayimin haka wlh na fadawa su Mom dasu Ya'isha yau zanzo har Sarki junior fah na fadawa yanata murna hatta Amrah da Addah Abulle sunata murna zasuga Muneefah....." A fusace yace “shut-up Meenah nace bazakije ba yau ki fita ki bani guri dama nasan dokinki kije kiyi hirar tsohon mijinki kiji dadi ko? To bazaki ba idan kika matsamin ma wlh zan iya cewa keda Daura har abada muga ta tsiya" Juhud is not free read... regular 300 VIP 600 via👉🏼 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank Then you show ur evidence via WhatsApp 09013718241... Juhud ba littafin kyauta bane ki biya 300 regular VIP 600 kafin ki karanta ta wannan account din 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank ko katin MTN pls ban buqatar vtu hoton katin ko digit number ta WhatsApp number 09013718241..... *Oum Hairan* [8/29, 8:00 PM] Oum Hairan: Tsayawa tayi ta zuba masa idanu tanajin ciwon yanda yake canzawa duk motsinta fassara hadiye wani abu tayi me daci ta juya ta fice daga dakin ta koma nata ta hade kai da gwiwa tanajin baqin cikin wannan wulaqancin na Rasheed Shi komansa baya aikatashi da lissafi kawai abinda yayi masa dadi shine yake aikatawa, kwanciya tayi tanajin Muneefah na buganta qofar taqi budewa tasan abinda zatayi masa kawai ta bata masa rai kenan. Ilai kuwa yarinyar ta riqa kuka ya taso ya fito ya isheta a qofar dakin taqi bude mata ya dauketa ya juya ya shiga dakinsa yasa kayansa suka fice so take y kulata bakuma zai kulata dinba, tun tana tsammanin dawowarsu harta hqr ta tashi ta shiga kitchen ta dora musu abincin Rana sai daya da rabi ta gama tayi wanka tayi sallah ta dawo parlour Kiran Mom ya shigo kasa dagawa tayi saboda takaici meye ma zatace mata? Da wannan tayi qarfin halin daga wayar suka gaisa tace “munjiku shiru" kukan da take hadiyewa ne ya kwace mata tace “mom zamuzo Amma ba yau ba" tana fadin haka ta sauke wayar a kunnenta ta kwanta taci gaba da karatunta. Sai biyu da rabi suka shigo da tarkacen kayan wasansu ya aje yarinyar ya zauna a gefenta daga kallo daya bata qara kallonsa ba ya sanya hannunsa ya dage rigarta da sigar zolaya yace “ 4 mouths kinqi karbar ajiyata sai zuba miki vitamin nakeyi kina shanyewa Babu wani good result" sake dauke kanta tayi daga gareshi tama fara yunqurin miqewa ya saqaleta ta baya ya miqe ya hadeta da jikinsa yace “meye kuma ya faru My Meenah Baffa'am dinki baison fushinki kin sani" Tureshi tayi tace “ai dama nasan bakaso Baffa'am ka rabu dani please kada kasa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82