Skip to content

Chapter 20

Chapter 20

Juhud Book One 1 Complete Hausa Novels 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

yawuna saidai idan mutuwa nayi"............ *THIS BOOK IS NOT FREE... REGULAR GROUP 300 VIP 600 VIA BANK ACCOUNT 0255526235 FAUZIYYA TASIU UMAR GTBANK OR CARD FOR THIS NUMBER 09013718241 ONLY WHATSAPP OR VTU ONLY FOR DIS 09031307566* *DON ALLAH IDAN KIN/KA TURA KUDINKA BANA BUQATAR DOGUWAR GAISUWA KAWAI EVIDENCE OF PAYMENT DA SUNAN LITTAFIN DA KIKESO NAKE BUQATAR GANI KO BANA ONLINE KIBARMIN IN NA HAU ZAN GANI KUMA ZANYI ADD NAKI A GROUP DINA COURSE MUTANEN DA YAWA.* *Oum Hairan* [7/18, 6:49 PM] Oum Hairan: *JH011* *(Pure love sex nd romantic story)* *Free page ya qare idan kinsan baki biya ba don Allah kada ki karanta, bansanki ba bare na yafe miki haqqina dake kanki* *Regular group 300 VIP 600 via bank Account 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank or card for This number 09013718241 only WhatsApp or vtu only for dis 09031307566* Cikin fusata Kareem yake qoqarin qwacewa yana huci Yana cewa “an fada maka kowa ma irinka ne mara Imani mara tsoron Allah Wanda zina tayiwa kanta cikin rayuwarsa" rirriqeshi suka sakeyi Dogari Ado ya kama Muntaz yasa a mota suka fice asibiti yakaishi akayi masa dressing din wajen da Kareem ya faffasa masa kai suka juyo sai huci yakeyi Yana furzar da iska baqin ciki ya hanashi furta ko kalma daya, Wai akan wannan tsintacciyar yarinyar Kareem ya fitar masa da jini wani huci ya furzar ya dunqule hannunsa ya daki dayan dashi yace “wlh saina wargaza wannan yarinyar tunda abin ya zama rashin mutunci ni zaaciwa mutumci akan wata banzar bafulatana mara galihu" Shidai Ado bai kulasa ba har sukaje gda fada suka wucce domin amsa Kiran Mai Martaba acan suka tarar da Kareem suka watsawa juna wani mugun kallo na kiyayi kanka, Mai Martaba ne ya nunawa Muntaz guri ya titsiyesu akan su fada masa meye ya hadasu har suke neman illata junansu?" Kareem irin mutanen nan ne masu baqar zuciya idan ransa ya baci baya mgn shikuma Muntaz ko hauka yake bazaice don yayiwa Juhud tayin shaidana bane yasa aka illatashi, tsawa Mai Martaba ya daka musu yace “ku tashi ku bani guri tunda bazakuyi mgn ba sakarkaru kawai" miqewa sukayi kamar zasu bangaji juna suka fita a daidai inda zasu rabu kowa ya shiga bangarensa Muntaz ya dafa Kareem yace “mu hadu a filin qwallo sabon wasa zan take leda ko ta tsiya kota tsiya tsiya" Murmushi Kareem yayi sai yanzu zuciyarsa ta fara sauka yace “bazan hanaka mummunan tunaninka ba saidai inaso kasani ita zina yado takeyi idan kayi da yar wani zaayi da taka idan kayi da matar wani zaayi da taka kazalika idan kayi da qanwar wani zaayi da taka wannan kadai ya ishi me hankali nutsuwa Aminatuh ba kowa bace marainiya ce me rangwamen gata idan da Allah yaso ta lalace saiya barta tayita galantoyi a duniya har ta samu abokin lalacewarta so baiso hakan ba saiya jefata hannun Big Cele duk da gurbatar yanayinsa ya kawar dakai gareta domin riqe amanar Allah kullum abinda yake fada a kula da ita itadin tanada qarancin hangen nesa kaico abin tur wai ace a gdannan zata lalace......" Dakatar dashi yayi da cewa “Dama kaje ka dauki speaker ka fara tafsir a masallacin fada qila da ka samu sadaka Dan m qauye kawai da ya kasa fahimtar rayuwa" shigewa yayi part dinsa ya banko qofar yabar Kareem tsaye cikin tsananin mamakin wannan qazamar rayuwar ta yan'uwansa qwafa yayi ya shige dakinsa ya fada gado Yana juyi tabbas akwai aiki a gaban maza shikam da Abba zai barshi daya nemi auren Juhud cikin lkc qanqani kodon ya tseratar da ita daga sharrin Muntaz Amma yasan abune ma bame yuwuwa ba tunda bai gama karatunsa ba a burin irin na Mai Martaba ba mazaba yaransa mata na bayayi musu aure sai sun hada degree certificate maza kuwa sai sunyi Masters degree ya samawa kowa gwaggwaban aikin yi. Lumshe idonsa yayi cikin yanayina tausayin kai da Kuma abar qaunar tasa shikam zaiyi qundunbalar furta mata koda bazaa Basu damar soyayya ba Allah ya jarabceshi da muguwar qaunarta baiji a ransa zai iya sakacin Bari ta kubce masa ba, da wannan tunanin yaji ana Kiran sallar magrib ya tashi ya fita domin zuwa masallaci ya jima a masallacin sannan ya tashi ya nufi cikin gdan a falo ya tarar dasu dukkansu suna kallon wani Indian series gabadaya hankalinsu ya bayu ga kallon da sukeyi duk cikinsu babu me motsin kirki. Ya jima tsaye akansu bai gano Juhud ba can ya hangeta kwance a kujera da littafi a hannunta da alamun nazari takeyi, zuciya yaja ya nufeta inda Momy tabisa da kallo ya tsaya akanta ya sanya hannu ya zare littafin ta dago idanunta ta saukesu akansa ta kawar dakai, sake jan numfashi yayi ya zauna a gefenta yace “Ina Ya'isha da Amrah?" Miqewa tayi zaune ta duba bata gansu ba ta dawo da dubanta gareshi tace “bansan sanda suka fita ba" jinjina kai yayi yace “wato Addah kun qyale yarannan suna abinda sukeso babu me iya tsawatar musu basuda aiki saidai suyi wanka su fice su kwaso wannan su kwaso wancan samari saikace budurwar karya idan anyi mgn Momy tace farin jini ne don Allah wannan wacce rayuwa kuka zaba musu a matsayinsu na mata da zasu tafi gdan wasu?" Dubansa Addah tayi tace “nikam bansan da wanne yare zan ganar dakai ka gane ba Abdulkareem wlh nafika jin ciwon wannan abin da yarannan sukeyi to baka isa kayi mgn bane kawai sun samu daurin gindi daga Mai Martaba abinda sukaga dama shi sukeyi kayi mgn suje su fadaka dashi yazo yayita fada shiyasa na tattara na zubansu ido kaima yanzu nemanka yakeyi sunje sunce masa kaine ka hana Aminatu zuwa chilling" Jinjina kai yayi ya bude littafin ya fara dubawa ya dubeta yace “ni ba turanci na karanta ba Amma zanyi bakin qoqarina wajen ganar dake abinda Allah yasa na fahimta ki tsara lkcnki da safe zanke miki darasin addini da dare Kuma na boko hakan yayi miki?" Rufe fuskarta tayi tana dariyar jin dadi tace “wlh yayi Ya Kareem na gde Allah yabarmana kai" murmushi yayi yace “dole saiya kasheni tashi muje ki nunamin assignment dinku na qarshe da Muntaz nagani saina samu gabar dora miki" Miqewa tayi tayi tsalle ta rungume Addah Abulle tace "idan na zama gwamna Ya Kareem zan fara kaiws makka" dariya sukayi Momy tace “baki rabo da shirme me sunan yaya to Ina kika baro Baffa'am din naki ni kwana biyu ma banjinsa ko yanayin aikin ne?" Cokalo baki tayi tace “bayan ya daina sona ko waya ya Kira baya cewa abani" murmushi Mom tayi tace “ai kedin ce da hayyata kimbi kin damesa yaushe zai dawo naji yace saura wata biyu ya samu hutu ya dawo gida" tsallen murna ta kamayi tace “na kusa na kwanta a jikin Baffa'am dina me dadi Allah duk duniya banga Wanda yafi Baffa'am dina iya rarrashina ba sai Ya Kareem da yake kwatantawa......" Fuzgarta yayi yace “kin cika surutun banza Amina to shidin muharraminki ne da zakike kwanciya a jikinsa dan wauta idan kinyi a baya yanzu shima yasan kin wucce wannan shirmen dubeki fah mace daya da rabi haba wannan ai shirme ne" murguda masa baki tayi tace “eh dai dan

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82