Skip to content

Chapter 29

Chapter 29

Juhud Book One 1 Complete Hausa Novels 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

wata takarda qarama dake a ciki miqa mata takardar sukayi taqi karba saima miqewa da tayi Mom tace “ungo ana Kira ki daga kije me zaace miki" noqe kafada tayi tace “Mom....." Hannun Mom ta Dora a bakinta tace “shitttt Amina banson gardama da fada da Wanda baka sani ba ai gara kayi da wanda ka sani ko banza akwai sanayya" Hannu tasa ta karba tanabin number da kallo hannunta na rawa ta danna wayar ta Kara a kunnenta yaja ajiyar zuciya daga yanayin saukar numfashin ta gane wayene nan take zuciyarta ta hau kai kawo a qirjinta. Bai bata damar tunanin komai ba yace “baki tausayin me tausayinki ko Meenah?" Shiru ce ta ratsa ta juya ta dubi Mom ta nufi qofar dakinsu yafi minti biyar kafin ya qara qutawa yace “banyi tunanin wannan sakayyar daga gareki ba inaji a Raina a baya idan kowa ya juyamin baya ke zaki kalleni da idanun Rahma ashe ban fahimta daidai ba Meenah meye aibuna da kika kasa maye gurbin rashin cancanta da cancanta a tunanina ko ban cancanta ba ya kamata ki kama hannuna ki dagani matsayin gwaninki....." Shiru yayi saboda numfashinsa da yake sarqewa yaja numfashi sosai sannan yaci gaba da cewa shekaruna 37 bantaba ji ko a wasa ina muradin rayuwa da wata mace matsayin mata ba sai a wannan gabar da qaddarar ta hadani dake tabbas da nasan cewa kedin zaki zamo masheqin rayuwata da ban fara jin tausayinki a farko ba" jikinta ne yayi sanyi da kalamansa zuciyarta ta karye bai Bari tace komai ba yace “bansan meye laifina ba don nace inasonki wlh tallahi duk duniya babu namijin da yakeyi miki irin son da nakeyi miki Meenah ba iyakar farin cikina zan fansar gareki ba har rayuwata da mutumcina duk zan iya sallamasu dominki na rantse da Allah idan ban sameki ba matsayin mata to kuwa shima Kareem bazai sameki ba saidai muyi ragas gara ki fita waje ki auri wani Amma a gdanmu ki auri qanina ki rayu dashi gani Ina bulayi Ina bazan iya ganin wannan baqin cikin ba, yess kince yanada nagarta nasan haka Ni banida nagarta Mazinaci ne ni yanzu Kuma soyayyarki ta mayar dani mashayi Kuma a haka zakizo ki rungumeni ki rayu dani dole idan kinqi bani hadin kai don Allah zaki bani don dole Meenah kiji a ranki ni mijin mace daya ne Kuma kece ko babu aure zamu rayu tare" Cikin tsananin fusata da kalamansa tace “ya Isa Baffa'am bantaba ganinka matsayin qasqantacce ko marasshin daraja ba wlh ko lkcn da nasan kana zaman dadiro da arniya mara Imani banji na tsaneka ba Amma yanzu kalamanka suna aika saqo cikin zuciyata duk da kasancewata mara galihu na shaida niba banza bace kamar yanda kakejin izzar sarauta a cikin jininka nima inajin izza a nawa jinin saidai Ni bansan ta meyece ba da wannan nake son sanar dakai na gode da kulawarka gareni Amma bazan taba kwarewa Mai Martaba baya ba saboda jin ya isa dakai yasa yaji a ransa nima ya isa Dani ya zabamin Ya Kareem batare daya nemi shawararmu Ni dakai ba to danme Ni zan nuna masa nidin ba halattaciyar ya bace? Numfashi taja taci gaba da cewa “bari kaji Baffa'am bazan taba canza zabi ba domin ba zabina bane na ubangiji ne saboda haka bana buqatar kalamanka ka adanasu ka fadawa Aunty Zulaihat ita zataji dadinsu Kuma zasuyi mata amfani Amma Banda Aminatuh"....... Qit ta kashe wayar gabadaya ta cillah a wardrobe tana jan tsaki Baffa'am din nata ya fara kai hqrnta qarshe to waima anayin so dolene da zai takura saita qaunaceshi bayan tariga tayi kyautar zuciyarta ga waninsa?. Komawa tayi ta zauna a hankali Kuma take auna kalamanta sai takejin babu dadi duk da cewar gsky ta fada masa, turo qofar akayi aka shigo ta dago ganin Muntaz yasata miqewa ya zubawa qirjinta iso yana murmushi wayarsa tayi ring ya miqa mata yace “kin tara kayan dadi baby Amma na hqr na fahimci babu rabona a wannan gurin gonar manya ce" tsaki tayi ta karbi wayar ganin sunan dake kai yasata miqa masa ya matsa da sauri yace “ai baki isaba yarinya dole ki Amsa wayar nan bazaki jamin masifa ba" jifa tayi da wayar ta shige bathroom bugun duniya taqi budewa Saida taji ya cewa “taqi karba fah tama shige bayi tabarni shanye kamar maratayi" Bata fito daga bathroom dinba Saida taji shigowar su Ya'isha ta fito tana goge idanunta da suka canza kala, da dare ma daya kirata a tata wayar da yasa aka tura masa number tana ganin numbersa ce ta dannata a silent ta koma ta kwanta washegari ta kama idi tun asuba suketa shirye²n tafiya idi sai bakwai suka gama suka fito sunata baza selfie Suna Shirin fita ya shigo sanye da kakinsa hularsa a hannu ya sauke idanunsa akanta tare da kwantar da kansa a jikin qofar yanajan wata wawuyar ajiyar zuciya me qarfin gaske qwarjini yayi mata ta kasa motsawa daga inda take su Amrah sukayi masa barka da zuwa ya dagansu hannu tare da nuna musu hanya suka fice ta daga qafarta daqyar zata bisu ya cafko hannunta ya janyota ya shigar da ita jikinsa ya matseta sosai yanda bazata iya motsawa ba yace “barka da sallah My wife" qoqarin qwacewa taketayi da hannu daya ya hardeta Amma ta kasa qwaqqwaran motsi ya figi hannunta ya nufi sama da ita ta cake a bakin qofar ta riqe qarfen benen ya juyo ya zuba lumsassun fitinannun idanunsa akanta yace “idan Kuma nayi amfani da qarfina nace saikin shiga cikin fah ya zakiyi?" Qasa tayi da kanta ya dagota yace “banson kuka kawai maimaitamin kalamanki na jiya zakiyi" da sauri ta dago yayi mata murmushi yace “zanyi amfani da duk wani abu daidai ko rashin daidai domin naga na hanaki samun abinda kike tunanin shine ya dace dake badon na cutar dake ba saidon sama miki yanci zaifi miki dadi ki rayu da wanda yasan mutumcinki" Dagowa tayi ta zuba idanunta cikin nasa tace “kana nufin Ya Kareem baisan mutumcina ba kai kadaine kasani?" Baitaba tunanin abinda zatace kenan ba ya tsaya cak Yana nazarin me zaice mata ta juya zata fice ya sake riqota yace ki shirya zaki rakani unguwa" hannunta ta janye batare da tace masa komai ba ta fice ta nufi masallacin suna idar da sallar ta zille ta nufi wani bangare na gdan ta zauna tana wayarta da Kareem dinta taji an cire wayar a kunnenta ta juya da sauri yayi wanka ya canza kaya cikin wata brown gezna yayi mata kyau sosai taja fasali yace “zaki?" Kallonsa tayi zatayi mgn yace “bama zabi zan baki ba dolene kizo muje" bata kawo komai ba batayi tunanin komi ba tabisa har inda yayi parking motarsa ya bude mata ta shiga ya sake mata murmushi yaja motar a guje suka fice Muntaz ne kawai yaga lkcn daya dauketa suka fice, Sunyi tafiya me nisa da gidan sarautar ya dauke wata hanya itadai batace masa komai ba wasa kawai takeyi da yatsunta Yana satar kallonta yayi parking jikin wani gda ya fita ya bude ya dawo ya shigar da motar ya sake rufewa ya bude mata qofar ta fito tana qarewa gidan kallo koda bata

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82