Chapter 46
Chapter 46
bank Account 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank or card for This number 09013718241 only WhatsApp or vtu only for dis 09031307566* *Ga yan Niger da suke son wannan littafi basusan ya zasuyi ba ga number da zasu tuntuba 94775574 zasu tura katinsu daidai da kudin littafin sai suyimin mgn na gde* *Oum Hairan* [8/1, 8:43 PM] Oum Hairan: *0025* Sake shigewa tayi jikinsa tana sunsunar qamshin turarensa cikin wata murya me kashe jiki tace “inasonka My world" matseta yayi Yana shafa cikinta na watanni hudu yace “inasonki fiye da yanda nakeson komai a duniyata ki zama amanata tawa Ni kadai kinji" murmushi tayi masa ya sake mirginawa kanta ta lumshe ido ya dora bakinsa saman idanun nata Yana lasar eyeslashers dinta tare da matse nononta a qirjinsa yana matsata yanda yaga dama wannan Rana an kurbi zumar qauna yanda ya kamata. Sunaji ana buga musu qofar sukayi likimo abinsu fir ya hanata fita wai yau lkcnsa ne bazaa yimasa ojoro ba hatta abinci Saida dare ya fita yaje ya siyo musu ya dawo suka qara bajewa suna tsinkar furensu da dare aka kwanta akaci gaba da bawa qauna haqqinta tun Juhud na jurewa har ta fara gajiyawa abinka dame yaron ciki shikuma dadinta ya hanashi qyaleta, da safe Mom da kanta tayo tattaki tazo barayin nasu domin babu wanda yasan ya dawo sai Muntaz daya daukoshi a airport. Ta jima tana bugu daqyar ya saki Juhud daya maqale ya fito parlourn yana tambayar waye? Jin muryarsa yasa Mom cewa ”haba nidai naji shirun tayi yawa Rasheedu ashe ka dawo?" Bude mata qofar yayi ya kwantar da kansa a kafadarta wannan tsohuwar al'adarsu ce yace “wlh tun jiya da yamma na dawo" murmushi tayi tace “babu Kuma ko nemanmu saima hanamin yata fitowa anata hada² a cikin gida tun jiya wayarta a kashe" sosa qeyarsa yayi ya zauna lkcn da Juhud din take fitowa ganin mom yasa taji kamar ta nutse ta rusuna a kunyace ta gaisheta tayi dariya tace “yar jaka ba ko sisi waike dadi miji mijinki ya dawo kin manta dani ko zai tafi yabarni dake ai muga qaryar rashin kunya" Dariya sukayi dukkansu Ya'isha da Amrah suka shigo da Khadija da Zahrah matar da zaa aurawa Kareem Ya'isha ce kawai ta kalli Juhud tace “ai dama Saida na kawo haka a Raina nace duk yanda akayi Babban ogane ya dawo kika manta damu" murmushi tayi tace “yo mi zanyi muku duniyata ta dawo gareni" dukkansu kallonta sukayi ta matsa jikinsa lkcn da Mom take fita tana cewa “aifa baki ya bude da alamun shima unborn din babansa yake buqata naga yau jiki ya wartsake ya samu abinda yakeso" Gaisheshi sukayi ya Amsa hankalinsa nakan Meenah ya miqa mata hannu ta kama ya dagota jikinsa ya zaunar da ita suka kalli juna Ya'isha tace “baba Aminu ne yace mu kawo maka Aunty Khadija ku gaisa Wai kun dade baku hadu ba" shafa qirjinsa yayi yace “wlh fah tun rasuwar mijinki halan kin gama idda ne?" Wani farr tayi da idanu tace “kayyy soja ai tun lkcn mutuwar Aunty Zulaihat ma nayi iddah" tabe baki yayi yace “ok to ai saiki fidda miji kiyi aure kada kice zakici gaba da shashancin da kika rinqayi a baya yaja miki aure da qananun shekaru" murmushi tayi tace “ai nama fitar Yaya Soja" bai bawa hirar muhimmaci ba ya kalli Zahrah yace “wannan itace dayar amaryan ance amaren ukune halan ya jikin Kareem din hope Yana samun sauqi?" Tabe baki Amrah tayi tana wani yatsina tace “to bama dolenshi ya warke ba wannan auren gayya da zaayi masa da yar asali me cikakkiyar nasaba" kallonta yayi batare daya fahimci meye takeso tace ba ya miqe yace “Life help me breakfast kin yasheni jiya fah" Saida taso ta nutse dan kunyar qannen mijin nata hakana ta miqe Khadija na harararta ta nufi kitchen cikin yan mintuna ta sama masa abinda zaici ta dauka ta nufi dakinsa ta aje masa zata fita ya riqota yace saurin na meyene?" Zama tayi tana hada masa tea din tana cewa “mom tace idan na gama naje mu gaisa da baqin Mali sunzo tun jiya sunata buga sashin nan ka Hana a budensu" yasan da hakan shiyasa baice komai ba ya rinqa janta da hira Saida ya gama yayi wanka sannan suka fito tare sunsha kyau na ban mamaki suna fitowa da ango Kareem suka fara kicibis sukayi musabaha ya tambayesa aiki shikuma ya tambayesa jiki itadai gaba tayi saboda zuwa lkcn wani haushin Kareem din takeji yanda yake nacin kallonta. Ta rigashi shiga tana shiga parlourn Hajiya Bilki da su Nana da sauran mutanen suka fara watsewa ta tsaya sake da baki kawai sai tajiyo a bayanta wata mata na cewa “ai wannan kina ganinta kyaun dan maciji baqar annoba kenan yanzu kina cika wargi zaki tsinci kanki a Ramin kabari ta tsotse bargo ta lashe kurwa" Juyawa tayi ta zubawa me mgnr ido hawaye wani nabin wani shiyasa jiya taqi fitowa saboda gudun abinda zatayi gamo dashi a wannan taron bikin, ji tayi an saqalo qugunta taja ajiyar zuciya tare da share hawayenta da gefen mayafinta ya zagayo gabanta yace “dame Kuma kika gamu daga fitowarki" murmushi tayi tayi gaba ya riqo hannunta yace “wlh bazaki shigaba saikin fadamin uban waye ya tabaki?" Tana Shirin mgn Ya'isha tace “wato Ya Rasheed yau zaayi kutmar uba a gidannan....." Fuuuuuu tayi gaba tana zuwa ta dauke Hajiya Bilki da Mari ta kama qunduma mata ashar abinka da bakatsina yau jini ya motsa bala'i takeyi tana dara nandanan gurin ya kacame taron biki ya koma taron fada shidai Rasheed baisan meye yake faruwa ba Saida yaji tana cewa “aikin banza aikin wofi har wasu kune zaku dubi Meenah ku rinqa jifanta da miyagun kalamai dama ai na dade Ina jiran damar cin bura uban kowannen shege a gdannan idan kuna taqamar ance muku itan mayya ce to ai gara ita ansan wacece ita ku waye yasan asalinku yayan bayi kawai Wanda tsiya da munafurci ta Haifa ta goya ta shayar Bilki kibi a sannu halwa ce dake gaba da baya Kuma mata ba maza ba aure Big Cele yace bayaso bazai auro irin masifa irin jaraba ba wlh dadai auren halwarki gara auren mayyah so million indai msita irinta Meenah ce Kuma Meenah ta zame muku ciwon ido a gdannan kowanne dan iska saidai yaganta yabarta idan da meja Kuma yaja shima ya wullah barzahu kamar yanda Zulaihat data dage saita shiga tsakanin rabo ta fece, yan iskan banza munafukan wofi" Tunda yaji dalilin rikicin jikinsa ke tsuma ran maza ya baci idanunsa suka kada sukayi jawur ya dubi Juhud data durqushe a qasa taketa aikin kuka me cin zuciya ya juya ya dubi mutanen kowa jikinsa ya hau karkari baice komai ba baiwa kowa mgn ba ya figi hannunta da qarfi suka fice daga falon gurin Mom din da baajeba kenan ya mayar da ita sashinsu ya kulle ya zauna yanata huci ya miqe ya zauna yafi sau ashirin sannan Kiran Mai Martaba ya shigo yayi jifa da wayar ta tarwatse ya tashi ya shiga dakinsa batasan me yayi ba ya fito dauke da jakankuna manya guda biyu ya fice ya jefa a mota daidai lkcn da yake
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82