Chapter 28
Chapter 28
Candy samarin Ya'isha da Amrah suka aiko neman aurensu da farko Mai Martaba yaqi amsar batun a cewarsa karatu zasuyi Alh Ibrahim wani amininsa shine ya sameshi ya bashi shawarar tunda sun nuna auren sukeso yayi musu ba lallai sai mace a gdan iyaye zatayi karatu ba a gdan mijinta ma zata iya karatunta da farko bai dauki mgnr ba saida Addah Abulle ta sake samunsa da mgnr Kareem fah ya matsa akan mgnr aure da Momy da ita da Ya Arman sune suka sameshi suka rinqa nuna masa abin hakan suna nuna masa Kareem namiji ne Kuma yanada kawaici tunda har ya fito da maitarsa ayi masa kada azo a samu matsala. Badon yaso ba ya amshi shawarar tasu dake dama an gama shirya komai na baikon Rasheed da Zulaihat hakanan ya Kuma bada maqudan kudade aka shiga kasuwa aka sake yo siyayyar baikon Kareem da Meenah Meenah batasan meye akeyi ba ranar baikon korasu akayi Katsina gdansu Addah Abulle acan suka yini suna tantalbadedensu akatsai da ranar aure Rasheed da Zulaihat wata biyu masu zuwa ya kama bayan azumi da sati uku dake azumin ya rage saura kwanaki bakwai ne sukuna akasa wata shidda saboda an qiyasta abinne da yanda zaizo daidai da hutun shekarar Kareem din ayi bikin ysnana ya dauki matarsa su tafi. Ranar farin ciki gurin Juhud da Kareem kamar su hadiye juna ta waya inda Rasheed yayi yinin qunci da baqin ciki a qarshe ma daki ya shiga ya kulle kansa yini sur har dare har safiya bai fito ba Mom ce ta kirata tace taje ta duba Baffa'am dinta tun jiya bai fito ba, bataso ba batason haduwa dashi tsoronsa takeji batasan da wacce irin fuska zai kalleta ba, hijjab dinta ta dauka ta Sanya ta fita ta nufi part din nasa tun daga falo ta fahimci akwai matsala kaca² ta tarar dashi gabanta ya fadi ganin kwalaben wine da wasu qananun kwalabe ta matsa ta dauki daya ta duba tare da dafe qirji da sauri tace “A'uzubillahi Baffa'am Alcohol kakesha?" Tsorone ya sarqeta takai hannunta qofar tana bugawa kusan 20 minutes bataji motsi ba murdawa tayi tajita a kulle ta rinqa bugawa da dukkan qarfinta Amma shiru dube dube ta farayi a falon can ta hango mukullaye a hade ta dauka da sauri ta fara gwadawa cikin saa na qarshen da tasa ya bude qofar ta tura da sauri, toshe hancinta tayi saboda warin daya daki hancinta takai dubanta inda ta hangeshi kwance a qasa cikin amai ta saki qara tana cewa “innanillahi meye hakan meye ya sameshi?" Matsawa tayi ta shiga jijjigashi Amma kamar tana jijjiga dutse daidai lkcn Momy da taji shirun tayi yawa ta shigo ganinsa a wannan yanayin yasata sakin ihu tace “Abdulrasheed meye hakan bakada lfy ka kulle kanka a daki zaka kashe kanka....." *Oum Hairan* [7/22, 6:51 PM] Oum Hairan: *JH016 littafina na kudine idan kinsan baki siya ba don Allah kada ki karanta, bansanki ba bare na yafe miki haqqina dake kanki* *Regular group 300 VIP 600 via bank Account 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank or card for This number 09013718241 only WhatsApp or vtu only for dis 09031307566* *Ga yan Niger da suke son wannan littafi basusan ya zasuyi ba ga number da zasu tuntuba 94775574 zasu tura katinsu daidai da kudin littafin sai suyimin mgn na gde* Gabadaya gidan ya rude Big Cele babu lfy Mai Martaba dakansa yazo suka daukeshi da likitan gdan suks nufi asibiti dashi suka fara bashi kulawa sosai likitan ya kadu dayin hoton zuciyarsa da yaga ta kumbura jininsa ya hau fiye da misali tashin hankalinsa ya nunku ya fito Yana sharce gumi iyakar saninsa Abdulrasheed ba mutum ne me shiga sabgar mutane ba balle su Dora masa damuwa to meye yaja asalin damuwar tasa? Da wannan tunanin ya fito ya sami su Mom a zaune suna ganinsa suka miqe ya sake share gumi ya dubi Mom yace “dama Rasheed yanada heart issue ne?" Da sauri suka kalleshi Mai Martaba yace “aa bashida ita" iska likitan ya furzar yace “to mgn ta gsky akwai abinda yasa a ransa da yakecin zuciyarsa har yayi mata Ramin da ciwo ya shigeta hoton da nayi masa ya nuna cewa zuciyarsa ce ta kumbura jininsa yayi mugun hawa fiye da misali nikam lamarin ya firgitani meye damuwarsa meye yasa a ransa da yake neman salwantar da rayuwarsa akansa?" Goge gumi Mai Martaba yayi ya dubi likitan yace damuwa Kuma a Rasheed din to wacce irin damuwa ce wannan nikam bansan irin yaron nan ba zurfin cikinsa yayi yawa" Mom ce tace “kuma ba akan yarinyar nan bane da yace bayaso kasanshi fah da baqar gaba idan yaqi abu zai iya komai akansa Mai Martaba ka duba lamarin Rasheed fah da Zulai......" Daganta hannu yayi yace “dakata Ayshatu indai akan wannan ne to zan tanadi likkafanin suturarsa don wlh bazan watsawa zuminci baqar toka ba ko zai mutu saina daura aurensa da Zulaihat......." Kwanansa goma a asibitin duk sanda zasuje dubashi daya ganta saiya lumshe idonsa bazai bude ba harsai ta fita a dakin maganar duniya bazai kulata ba tun abin na damunta har ya daina damunta da zugar qannensa da suketa famfata akan kada ta kuskura ta bashi qofar da zai gane tanajin tausayinsa zai kaita ya baro ne qila ma ba aurenta zaiyi ba Kuma ma yaushe zata saki saurayi ta kama tuzuru tuzurun ma me Shirin auren wata a fari ba itaba, quruciya da wauta da rashin mafadi ya hanata gane kuskuren da take qoqarin tafkawa Wanda ita kadai takeda ikon canzashi hakanan akaci gaba da tafiya har yaji sauqi aka sallamoshi kwanansa Tara da sallama ya tattara nasa ya nasa yabar gdan batare da kowa yasan da tafiyar tasa ba koda ala fada mata ya tafi Saida yaji babu dadi a ranta Amma zugar su Ya'isha ta hanata saukar da kanta a gefe Kuma da sabon haukanta na dokar da Kareem ya kafa mata cewa indai namiji ba muharraminta bane to ya haramta mata mu'amala dashi wannan dalilin yasa tanason taje ga Baffa'am din nata Amma babu dama gani take kamar Allah ma fushi zaiyi da ita ta karya dokar mijinta. Ana azumi ana shirye²n sallah ana na biki gda ya dauki harami sosai komai na bikin Baffan nata ita dasu Ya'isha suke shiryashi Basu Katsina Basu Kano siyayyar ashobin biki da kayan sallarsu kwanaki sunsta tafiya soyayya tsaksninta da Kareem tanata qaruwa dare rana yammaci suna maqale a wayar daya Sanya aka kawo mata sabuwa dal suna tsara yanda bikinsu zai kasance. A haka aka cinye azumin ana gobe sallah tana falo tana waya Ado drive ya shigo da sallamarsa suka gaisa ya miqa mata wata leda yace “gashi inji wani soja a waje yace akawo miki" Saida gabanta ya Fadi da akace soja Mom ta zubanta ido tace “soja Kuma Amina Ina kika samo soja?" A sanyaye tace “bansani ba Mom" karbar ledar tayi ta bude ta dauko kwalin dake ciki wata rantsattsiyar wayace Sumsum me matuqar kyau da tsadar gaske Mom ta juyata sosai a hannunta ta dubi Juhud data zuba tagumi tana kallon Mom. Sake zaro kwali na biyu tayi wasu fitinannun turaruka ne masu masifar qamshi a ciki sai tarkacen Sweet da chocolates sai
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82