Skip to content

Chapter 27

Chapter 27

Juhud Book One 1 Complete Hausa Novels 1,201 words 0 views Progress saved
Download Book

ta kafesa da idanunta da yake tsiyayar da hawayen tashin hankali tasowa yayi ya matso gabanta ya miqar da ita yace “idan ya kasance kin kasa saka wancan Alkhairin da abu mafi daraja wato qaunar da wannan mutumin yake nema a gurinki to tabbas ke ba yar halak bace domin dan halak shine yake jiran gabar saka Alkhairi da komansa koda kuwa gurin bai cancanci sakayya ba shidai burinsa yaji a ransa babu bashi tsakaninsa da wannan mutumin" Sakinta yayi ya juya zai shiga bathroom har ya bude ya juyo yayi mata murmushi yace “kije kiyi tunani akan kalamai na" a mugum kasalce ta bude qofar ta fito ta nufi cikin gdan zuciyarta na kai kawo akan kalamansa tana shiga dakinsu ta zube a bakin qofar tana mayar da numfashi Amrah dake fitowa daga bathroom taja ta tsaya sake da baki ganin yanda ta cure jikinta tanata rera kuka takaici yasa Ya'isha miqewa tace “dallah malama ke baki rabo da kukane meye Kuma akayi miki" dagowa tayi ta kwantar da kanta jikin Amrah tace “nikam Ina ganin rayuwa Amrah don Allah meye wadannan kalaman suke nufi......" Zayyane musu komai tayi ta qarashe da cewa “bansan meye yasa qwaqwalwata bata gane abubuwa ba" numfashi Amrah da Ya'isha suka saki tare Amrah tace “kan ubancan lallai akwai qura a gdannan Juhud bafa wani abu Big Cele yake nufi ba kece yakeso kece Aminan da yake baki lbr ke kadai ce me wannan siffar daya suffanta" Ya'isha ce tayi murmushi tace “ke saiyau kika fahimta ai dake da Aminah dukkanku kallonku nakeyi Amma wlh batun yanzu ba na fahimci Big Cele son Juhud yakeyi tsabar miskilanci ne da girman kai ya hanashi bayyanawa yake wani bada fadi da hura hanci kamar kyankyaso aikin banza na dade da gano damuwarsa kekam ta bakin naki kina ganin rayuwa ga Mai Martaba yayima Ya Kareem alqawarin aurenki" cikin mutuwar jiki ta dago tace “nikam ya zanyi wlh da gaske bantaba daukar wannan gundumemen lamarin zai fadomin ba banyi masa muhalli a bangarena ba bantabajin Baffa'am zaice yanasona ba kai bama abinda yake nufi ba kenan babu abinda zaiyi dani" Dariya sukayi dukkansu ta zubansu idanu Amrah tace “waima to shi ya gani wlh yarinya tun wuri ki takansa birki inba hakaba zakisha wahala Big Cele bashida mutumci gashi da ganinsa zaiyi wuta babban tashin hankalin ma mgnr aurensa da Zulaihat tayi mugun nisa harma fah ankai kudin tambaya sa rana kawai zaayi anasa rana Kuma raqashewa zamuyi Kinga kenan bakida gurbi kawai batankin gomanki zaiyi dayanki bata gyaru ba" Tagaji dajin wadannan kalaman hakanne yasata miqewa ta shiga bathroom ta sakarwa kanta ruwa ta fito taji ana kiran magrib ta dauki dabino ta tauna ta fita ta dauko ruwa tana dawowa Amrah ta miqa mata waya ta Amsa ganin number Kareem ta Kara a kunnenta tace “nasha ruwa lfy Habiby kaifa?" Murmushi yayi yace “yanda kikasha Luv ya exams?" Kwanciya tayi tana lumshe ido tace “inajin dadin exams din da taimakonka" hirarsu sukaci gaba dayi tama manta da batun Shan ruwa saida yace “kije kisha ruwanki zan kiraki anjima" ta aje wayar ta tayar da sallah tayi buda bakin. Tun daga wannan ranar salon rayuwar gdan ta canza musamman tsakanin Juhud da Rasheed duk inda tasan zasu hadu gujewa gurin takeyi saboda ita har cikin zuciyarta bataji a ranta zata iya soyayya dashi ba bayan haka ma sannu a hankali Kareem ya gama siye zuciyarta da salon qaunarsa me tsayawa a rai da wuyar gogewa kullum idan sunyi waya kalmarsa daya itace don Allah Aminah ki kulamin da kanki nayi miki tanadin kaina na tsare kaina tsayin shekaru burina ya kasance a halali na na fara shuka inason gonata tayi kyakkyawan yadon da yabanyarta zata burge kowa idan amfanin ya nuna ya isa moro ya morawa duniya baki daya Aminah samawa yayana uwa ta qwarai shine abinda na dade Ina addu'a nasani bazan taba danasani ba idan kin kasance mata a gurina zaki bani farin cikin da zanyi alfahari dake a duniyata da lahirata" Idan ya fada mata haka Yana kashenta jiki matuqa takanji kamar ya daureta da jijiyarta ne duk saitaji wani shauqin qaunarsa Yana qara mamaye ruhinta wannan dalilin yasa ta qara qaimi wajen tsare kanta tunda me bata kariyar bayanan gashi ya Daura mata nauyi Mai girma na amanarkai. Kwanci tashi lkc ya rinqa tafiya cike da matsaltsalu Rasheed mugun miskili da baa gane matsalarsa Amma yanzu kusan kowa ya fahimci yanada damuwa gashi da baqin zurfin ciki ya kasa furtawa kowa damuwarsa saidai yaje Garden yayi tagumi ko ya tusa waya a gaba yayita kallo. Ranar da sukayi Candy suka hada qwarya²r party a gidan sarautar Juhud batada qawaye su Ya'isha ne suka gayyato samarinsu da qawayensu Mai Martaba shine ya daure gindin partyn harda dauko musu Dan Hausa yazo don qarawa abin armashi qarfe hudu suka fara caskalewa samarinsu duk sunzo itace kadai saurayinta baizo ba baya qasar ma Amma yayi mata fatan Alkhairi sun dauki wanka na tashin hankali sunyi kyau na bam mamaki dama dukkansu ba baya ba wajen kyau Amma sukansu Saida suka sallamawa Juhud tayi kyau kamar wata amarya suka fito daga gdan ana take musu baya suka fara hotuna anyi mata hoto yafi kati dari da shiga daban² ta karbi wayar Ya'isha ta zagaya baya ta Kira layin Ya Kareem bugu daya ya daga tayi ajiyar zuciya tace “rayuwata tana cike da kewar masoyi banajin komai yana tafiyar min daidai" dariya yayi yace “kinajin abinda nakeji kuwa Aminah nifa inajin kamar zanyiwa Mai Martaba mgn ne zanzo hutun azumi kawai a hada bikinmu dana Big Cele ayi a bani ke mu taho nan" Juyowar da zatayi suka hada ido da Rasheed dake tsaye jikin swimming pool kallon da yake mata ne yasata kama in...inar qarfi da yaji tace “am...in...." Ji tayi ya warce wayar ya duba yaga number qanin nasa yana mgn Yana cewa “hello..... Luv....." Qit ya kashe wayar ya jefa a aljihunsa ya juya yabar gurin daga Ya'isha dake qarasowa ta dafata tace “wai me kikeyi ne anata nemanki" juyowa tayi idanunta ya ciko da qwallah tace “ya qwace wayar Amrah...." Binsa sukayi da kallo Ya'isha tace “hmmm wannan mutumin dan rainin hankalin mutumin wlh bashi da mutumci yanzu duk hotunan da mukayi sun tashi a banza kenan?" Qwafa Amrah tayi tace “kuma duk baqin cikinsa bazamu fass shagalinmu ba Allah yasa ba layina bane akai daya cuceni" janta sukayi suka shiga filin itadai yaqe kawai takeyiwa mutane har takwas taron ya tashi suka shiga gda ta shige daki ta kwanta tana mayar da numfashi. Da wayar Ya'isha Kareem ya sake kiranta yake tambayarta Ina wayarta ne yanata Kira a kashe taja fasali tace “Baffa'am ya qwace tawa ta Amrah ce nakesa layin itanma dazun ya qwaceta" wata iska ya furzar yace “ina Gsky abin nasa ya fara yawa fah banason shigarmin hanci da qudundunen nan da yakeyi Ina ganin girmansa kada azo ayi babu dadi zan fadawa Mai Martaba ya dakatar dashi gsky na gaji duk yabi ya takuraki to ko hsihuwarki yayi kikakai yanzu ai ya qyaleki balle a sama yaganki" itadai batace komai ba saboda itanma duk kawaicinta da kararta Baffa'am din nata ya fara duba juriyarta. ************* Satinsu biyu da

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82