Chapter 67
Chapter 67
tabe baki ta mayar da hankalinta ga Mom sukaci gaba da hirarsu tanata dariya abinta shirmen da Rasheed yake buga musu ko Sarki bazaiyi ba suna haka Fadila ta fito ta debesu ta watsar Meenah tayi murmushi tace “Allah Sarki wannan fah Mom?" Girgiza kai tayi tace “au Fadila auren ne yaqi dadi mijin neman mata har ksn gadonsu na sunnah shine tayo yaji ya aiko mata da takarda saki daya" dafe qirji tayi tace “ya salam Abin tausayi Allah ya daidaitasu" murmushi Mom tayi tace “kayyah dai itama Amrah jiya ta koma aure mijin ya qara shine zatayi masa haukanta ya korota uwar mijin tace ita dama batason wannan auren daidai ya nace ne daqyar dai aka sasanta ta koma kayy Meenah munga jarabawa dan ritsin nan " jinjina kai tayi tace Allah yasa ta zamo kaffara amsawa tayi da Amin sunata hirarsu ta yaushe gamo Kareem ya shigo suka gaisa da Mom ya dubi Juhud yace “bansan kin fito ba fah Saida na leqa dakinki naga bakinan" murmushi tayi tace “nazo mu gaisa dasu Mom ne" Miqewa yayi ya nufi part din uwarsa yace “ok ku gaisa sosai Amma ki nemamin abinci yau girkinki nakeson ci....." Rasheed dake tura motar wasan yara shida Sarki ya dago yace “lahhh zaka sammin?" Tsayawa Kareem yayi ya juyo ya dubeshi da tausayawa yace “in kanaso ma kullum ka rinqa zuwa kana karba Aminah ta iya girki sosai" tsalle yayi ya dafesa yace “itama sunanta Meenah nima tawa Meenan ta iya girki nifa tunda Meenah ta mutu ban qara cin abinci me dadin nata ba" Tsayawa yayi kamar zai juyo sai Kuma yasakai ya shige ciki sama² suka rinqa jiyo hargowar Addah Abulle basajin dai abinda suke cewa Meenah ta miqe tace “bari na koma Mom duhun magrib ya fara shiga saida safe" ta juya ga Rasheed daya zuba mata ido tace “Baffa'am Saida safe" daga mata hannu yayi yace “zanzo na karbi abincin naki ai" murmushi tayi ta juya ta fice ta nufi sashinta taji an bangajeta taja baya da sauri tare da cewa A'uzubillahi....." Tana duban Wanda ya bangajeta din Fadila ce qanwar mijinta tayi murmushi kawai ta juya taci gaba da tafiyarta a bayanta taji tana cewa “gayyar na ayyah gayyar tsiya an dawo zaaci gaba da dorawa uwarmu ciwon zuciya jarababbiya qalatacciya da wani shegen cikinki a gaba irin masifa irin maita......" Kalamin sun daketa ta cije lebe tare da tsayawa batare data juyo ba tace “hakane saidai kin manta abu daya bani na liqe mawa dan'uwanku ma shine qalatacce jarababben daya liqemin wlh da zaku bashi shawarar ya rabu dani ma ya dauka da dadi nikaji domin zan yar da qwallon mangwaro na huta da qudaje" Tana fadin haka ta shige tabar Fadila sake da baki lallai yarinyar ta riqa wato sune qudaje Kareem ne mangwaro tab yau da tashin hankali a gdannan, fuuuu ta shige ciki ta nufi sashin uwar tasu tana shiga ta fara karanta mata qarya da gaskiya aikuwa ta hau ta zauna ta dauki waya ta Kira Dada Hanne ta zayyane mata abinda ke faruwa Dada Hanne tace “ai Ni wannan jaraba na rasa dame tayi kama yarinya ta zamewa mutane qarfen qafa an kasa kwanceta a yar shima Mahfuz din kwanaki kamar abin arziqi aikin da mukayi ya fara cinsa yanzu Kuma yaqi kullum abubuwa lalacewa sukeyi" Takaici ya cika zuciyar Addah Abulle tace “ni takaicina ma cikin nan da yake jikinta ashe bai fadaman lissafin daidai ba boyemin yayi yanzu kawai Ina ganinta naganta da tsohon ciki haihuwa kusa" wata uwar ashar Dada Hanne ta qunduma tace “au ke yanzu kina zaune sakarai kika bari tayi ciki kema zaa jorner miki tsiyar?" Da muryar takaici tace “to ya zanyi kefa kika sani na rinqa rabar da kudi tsakanin gurin malamanki dana Hajiya Bilki nidai banga wata nasara ba saita dawowa ta gdannan" Qwafa Dada Hanne tayi tace “ai shegiyar gantalalliyar yarinyar ce masifar taurin kaine da ita bansan wanne irin shiri ne a jikinta ba Amma bari intasan wata batasan wata ba" sun jima suna saqarsu a mugun zare sannan sukayi sallama da shirinsu na cimma matsaya. Meenah kam tana shiga part dinta idanunta ya sauka qasan tiles din taga wani garin magani duk an barbadar dashi kiyayewar Allah ce kawai tasa taga maganin saboda shima arsh ne kalar tiles din, taja baya da sauri tana a'uziyya a fili ta fara dube dube bataga Wanda zata Kira ba ta koma gefe ta tsaya tsam jikinta na tsuma tsoro ya cikata tana nan tsaye Allah ya jefo mata Kareem taja ajiyar zuciya, qarasowa yayi da sauri yace “meye kikeyi anan Kuma?" Dubansa tayi jikinta na tsuma tace “naje zan shiga naga wannan abun" idanunsa ya zuba a tiles din ya na kallon abin ya girgiza kai yace “ki shigo da Bismillah babu abinda zai sameki sai abinda Allah ya hukunta kiji haka aranki".......... Kama hannunta yayi suka shiga cikin gdan ya janyota jikinsa yana sunsunar qamshin gashinta yace “kin wahalar da zuciyata yau" dagowa tayi ta kalleshi yayi mata murmushi yace “kiyi komai ba komai ya lfyr babyna" ajiyar zuciya tayi tace “nima nasani" dariya yayi yace “kuma kina tare dashi?" Kautar da kanta tayi sukaji ana buga qofar suka kalli qofar tare ji sukayi anyi sallama gabanta ya Fadi ta janye yace “ina zaki?" Kallonsa tayi tace “Baffa'am ne ke buga qofar nan fah...." Janyota yayi yace “to me zaki bashi?" Tsayawa tayi tayi sororo sai Kuma ta juya da sauri tace “zan bashi hqr ne yace yau bazaici abincin kowa ba sai nawa" Zama yayi ta bude qofar tana budewa ya shigo yace “ina abincin nawa?" Yana mgnr yana kalle kalle ta kalli Kareem tace “yanzu zan girka maka me kakeson ci?" Kallon kitchen din yayi yace “nima fah na iya girki muje na tayaki nawa ma sai yafi naki dadi" zaro ido tayi tayi dariya tace “habadai aiko Ya Kareem bazan sa girki ba balle kai da girmanka da matsayinka" nuna mata hanya yayi yace “ok aje abani abincina naci na kwanta sallar ma yau bazanyi ba" kitchen din ta nufa Kareem ya tashi yabi bayanta taliya ta dauka ta girkata fara ta tace ta dauko kayan miya ta soya ta zuba kifinta bushasshe data gyara ta dauki hantarta ta zuba ta soya sannan ta zuba kayan dandano ta juye taliyarta ta cakuda a cikin man nan da kayan miya ta barsu suka dahu daidai buqatarta ta sauke. Bata tsaya hada lemo ba ta dauko na kwali ta dora akai ta zuba mawa Baffa'am dinta nasa sannan ta zuba nasu ta fita yana zaune har yanzu Yana karkada qafa ta ajiye masa a gabansa ya dauka ya miqe yace “yawwa na gde" ficewa yayi ta girgiza kai ta dauko nasu ta jera a dinning ta nufi dakinta tayi wanka ta fito ba kwalliya take ba ita dama doguwar riga kawai tasa ta fito ta qwanqwasa dakin na Kareem tajishi yana karatun qur'ani ta bude ta shiga, Saida yakai simuni sannan ya juyo ya dubeta yaja ajiyar zuciya tace “barka da hutawa" jinjina mata kai yayi tace “na kammala" murmushi yayi yace “kin bawa Ya Rasheed din?" Dagansa kai tayi yace “ya tafi?" Ta qara daga masa kai yace “ok
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82