Skip to content

Chapter 74

Chapter 74

Juhud Book One 1 Complete Hausa Novels 1,204 words 0 views Progress saved
Download Book

saidon bata damar kasancewa dakai domin kaine zabinta, dani qaddara ta rubutawa bacewa ka auri matata idan na dawo gdy zanyi maka badon bana kishinta ba aa saidon nasan ta cancanta ne shiyasa ta zama matar gado cikin ahlinmu".......... A daren nan Rasheed bai rintsa ba kwana yayi Yana tuna abubuwa da dama da suka faru tsakaninsa da Kareem tun daga ranar farko da suka fara qullah soyayya da Meenah kawo lkcn daya aureta ta qarfi da irin wahalar da Kareem ya rinqa Sha ta ciwon zuciya duk akanta kawo yanzu yanayin da suke ciki da irin bibiyar da Kareem ya rinqa yi masa akan yayi hqr ya daina gaba dashi sosai yayi kuka da baitabayin irinsa ba a duniya tabbas ya tafka kurakurai masu wuyar gyarawa Kareem baya duniya labarinsa ya shude balle yaje ya nemi afuwarsa akan abinda yayita qoqarin ganar dashi yaqi bashi qofa. Da asussuba kuwa ya dokawa Mom Kira itanma yanda ya kwana haka ta kwana saboda tun Daren itama aka fada mata abinda ke faruwa Meenah kam batasan meke faruwa ba Amma ranar ta kasance cikin wani yanayi domin a daren waya sukeyi da Kareem Yana mata wasu kalamai data kasa fahimtarsu can taji yace “Meenah kada ki manta wannan wlh tallahi duk duniya nafi kowa sonki ban barki don biyayya ga umarnin Addah ba nabarki ne don nasan kedin banine a zuciyarki ba Meenah in son samuna ne Muneefah ta rayu a qarqashin kulawarmu ni dake nasan hakan bazata samu ba wani abu yana gaf da faruwa dani, Ina kukan rabuwa da abubuwa biyu da nafi qauna ke Meenah da Kuma yarmu Muneefah Amma a wani sashin Ina farin cikin kasancewar zata rayu da cancanta madadina wato Rasheed Meenah ki komawa Rasheed don Allah don taimakon maraicin Aishatuna kinji......" Daga haka ya tsaya da mgnr taji wata qara can taji yace “ina zuwa zan kiraki kamar Yan fashi sun shigo unguwarmu" daga wannan tajishi shiru kalamansa sun tsayanta a rai zuciyarta ta karye tabbas lamarin Kareem akwai taqawa da tsoron Allah baitabayin Abu don jin dadin kansa ba komai zaiyi yanayine don mafitar Al'umma Kareem yakai masoyi a gurinta. Miqewa tayi zumbur lkcn da taji Ya'isha ta rushe da kuka tana cewa Innanillahi wa Inna ilaihir raji'un Allahumma ajirni fih musibati Mom da gaske Ya Kareem sun kasheshi ya mutu shikenan bazai qara dawowa duniya ba Muneefah ta zama marainiya....." Juhud is not free read... regular 300 VIP 600 via👉🏼 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank Then you show ur evidence via WhatsApp 09013718241... Juhud ba littafin kyauta bane ki biya 300 regular VIP 600 kafin ki karanta ta wannan account din 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank ko katin MTN pls ban buqatar vtu hoton katin ko digit number ta WhatsApp number 09013718241..... *Oum Hairan* [8/22, 8:04 PM] Oum Hairan: Da mugun gudu cikin fitar hayyaci Juhud ta fito daga dakin da take cikin gigita ta cacumi Rasheed dake shigowa idanunsa kamar garwashi ta jijjigashi tace “da gaske ko gizo kalamin Ya'isha sukemin Ya Kareem ya mutu....." Zubanta idanunsa yayi so yake yayi mata mgn ya kasa sai kawar dakai da yayi hawaye suna zubo masa yasa hannunsa ya janye nata, ganin yanda yake goge hawaye da tissue yasata zama a gurin dabar ta daura hannunta akanta ta rushe da kuka tana cewa Innanillahi wa Inna ilaihir raji'un" Ya Kareem kada ka mutu dom girman Allah ya kasance mafarki shudadde Wanda bazan qarayinsa ba har abada wlh na aminta da kai zan dawo gareka na qara Haifa maka qannen Muneefah nasan shin....shine burinka a duniya....." Dagota Mom tayi tace “kiyi hqr Meenah shirya mu tafi" Babu wani shiri ta sunkuci Muneefah da taketa bacci abinta baccin asara abin tausayi mota ta debesu gabadaya harda Alh Garbu suka nufi airport dake abin na manya ne nandanan suka Isa Nigeria kamar a qasar suka kwana goma na safe suka shiga Daura lkcn an gama shirya Kareem da Zahrah zaayi musu sallah mazan suka tsaya wajen jana'izar sukuma suka shige ciki. Addah Abulle tana ganin Juhud ta miqe ta nufeta da sauri ta karbi Muneefah ta rungume ta qara rushewa da kuka tace “shikenan ya tafi Meenah yatafi yabar Mana duniyar Babu shi din Babu Zahra wayyoh Kareem dama inada dama Dana dawo dakai duniya nabarka da zabinka da yarka daya mafi soyuwa a ranka kullum kana fadamin bakajin dadin rayuwa baka tare da Muneefah ashe ita kadaice rabonka ita zaka tafi kabarni da ita Kareem wayyoh Ni Zainabu na cuci kaina na cuceka Kareem Allah na gde maka da bakabani saa ba lkcn da malam Mati yabani magani yace nabaki kici a waina da tuni Babu Aishatu da tuni Ni da kaina na kashe bayan dana kaicona Ni Zainabu Allah ya isa Dada Hanne da Hajiya Bilki kune kukayita dorani a keken bera ashe kaini zakuyi ku baro yau na rasa Kareem ban barshi ya rayu da farin ciki ba ya tafi da jin ciwon nice silar rabashi da matarsa mafi soyuwa a duniyarsa...." Surutai taketayi kamar wacce ta zautu hakan yasa wasu mata daga cikin danginta sukazo suka kamata suka tafi da ita daki tana kuka tana kiran Meenah Kareem shikenan Kareem ya tafi yabarmim duniyar Ina nutsuwata da hankalina yayi na kasa gane nauyin qaddararsa?" Kowa ka gani a falon kuka yakeyi mutuwar Kareem tabar tambari ba iya Daura ko Katsina kadai ba hatta arewacin Nigeria baki daya duk Wanda yaji labarin mutuwar ko baisanshi ba sai yaji alhini a jikinsa duniya tayi rashin nagartaccen mutum me hqr da kawaici kunya da kara wannan dabi'ar tasa yake soyuwa a zuciyar duk wanda yayi mu'amala dashi ta kusa kota nesa ranar anyi yinin alhini Juhud kam zazzabi ne ya rufeta sosai bana wasaba hawaye yaqi tsayawa a idanunta tayi danasanin zabar Rasheed akan Kareem ta zabi Rasheed tabar Kareem Rasheed din ya tattarata yayi watsi da ita yaqi saurarenta. Haka suka yini yinin koke² da dare kowa ya nemi guri ya kwanta itakam koda ta kwanta kasa rintsawa tayi rayuwarta da Kareem zamantakewarsu da yanayin salon qaunarsa me tsayawa a rai shudaddiya wacce bazata dawo ba tanayi mata yawo a kwanya saidai kawai lkc zuwa lkc ta dauke hawaye, wajen 10:30 taji ana taba qofar dakin data shiga ta kulle kanta ta miqe a wahalce ta bude ta dan ja da baya a tsorace ganin Rasheed ne jajayen idanunsa akanta ya miqa mata Muneefah da tayi bacci tasa hannu ta karbeta ta juya ta nufi cikin dakin taji muryarsa data shaqe da alamun yaci isasshen kuka yace “Duk da bansan irin radadin da kikeji a zuciyarki ba na rashin masoyinki uban yarki nasan kinajin fiye da abinda nakeji tabbas akwai daci daci mafi dacin daci rabuwa da abinda kakeso a lkcn da kake tsananin buqatarsa yaune kika farajin kwatankwacin abinda naji lkcn dana rasa hanyar dawowa gareki kwanyata ta daina fadamin daidai aka rinqa nunamin ke cikin wani yanayi dana kasa ganewa har yanzu and end aka nunamin ke wani mutum ya hankadaki cikin wani dogon rami Wanda na yanke shawarar binki mu mutu tare Meenah bayan na biki bansake sanin komai da hankali zai tuna ba sai bayan shekara bakwai dinnan Amma ko a cikin yanayin zautuwar qwaqwalwata ban mantaki ba duk wani furucina

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82