Chapter 18
Chapter 18
Mgnr ce ta maqale saboda kallon da yaga Yana watsa masa yasan tsaf zai fashe masa baki, miqewa yayi sumsum yabar gurin ya nufi dakinsa Yana saqa abubuwa a ransa, baitaba ganin kyawawar halitta irin wannan yarinya ba tabbas zaa huta da ita saidai idan mugunta tasa ta hanashi sakewa. Addah Abulle ce ta janyeta daga jikin Rasheed ta dubi Amrah tace “ku kaita dakinku ku bata ruwa tayi wanka kuzo ku hada mata abinci idan taci ta huta don Allah kada ku dameta da surutunkun nan kubarta tayi bacci ko na awa daya ne miqewa sukayi su biyun suka riqe mata hannu sunyi nisa ta juyo da sauri idanunta akan Rasheed tace “ayyah Baffa'am Amma ba tafiya zakayi ba ko?" Dagowa yayi daga kallon wayarsa ya dubeta sosai yace “bakison na tafi ne?" Dagansa kai tayi cikin karyewar zuciya tace “idan ka tafi waye zaike bani abinci waye zaike koyamin karatu sannan waye zaike daukana Yana zagawa dani gari Kuma waye zaike rarrashina?" Dukkansu ta Sanyaya musu jiki Kareem dake zaune yace “na dauki wannan nauyin zanke koya mata karatun qur'ani Dana bokon zanke daukarta Ina kaita tana ganin garin duk inda takeso zuwa a garin Katsina na dauki wannan alqawarin....." Dagansa hannu yayi yace “na riga na bawa su Ya'isha wannan damar sune zasuke daukarta suna zagawa da ita kai aikinka koya mata karatun qur'ani da tajweed tunda kai balarabe ne shikuma wancan mashiriricin ka fada masa ya zama malaminta na turanci bayan wannan Kuma banson wata alaqa tsakaninsu" jinjina kai Kareem yayi yana tuntunin alaqar Muntaz da wannan baquwa gabadaya Muntaz ba mutum ne me alqibla ba Amma hakanan zai qyaleshi kowa yayi aikinsa, Miqewa yayi ya fice ya nufi bangarensa ya bude ya shiga an gyara masa shi tsaf ya cire kayansa ya shiga wanka ya fito ya zauna yana duba wasu abubuwa a wayarsa wata baiwa ta shigo ta gaisheshi ta aje masa abinci ta fita bude abincin yayi ya lumshe idonsa Addah Abulle tanaji dashi abinda yafi qauna ne tayi masa tuwon shinkafa miyar danyan kubewa ya kuwa ci abincin sosai ya kwanta ya huta bai fito ba sai yamma da shirinsa tsaf ya fito cikin shirinsa na tafiya Illorin zuciyarsa gabadaya babu dadi sai yanzu yakejin kewar tafiya yabar yartasa. Cikin gidan ya shiga Momy ya tarar a falo suka qara gaisawa yana rarraba ido bai hango koji motsin yammatan ba ya dubeta yace mom Ina su Ya'isha" murmushi Mom tayi tace “sun shiga gari ya qamshin bararraken daddawa" da sauri ya dago yace “harda daughter?" Yagar apple dinta tayi tace “itama ai akarada ce sunanan suna hirarsu wancan mashiriricin yace su tashi suje kallon ruwa tace itama zata carton biyu sun zama uku dama sai abinda ya qaru ai Mai Martaba da daurewa qarya gindi dubu hamsin yabasu wai ko zasuga wani abun suyi sha'awa a hanya" Zuciyarsa ce ta karya ya taho da qwarin gwiwarsa yace “banason yawon nan Mom don Allah asa ido kanta Kinga itadin amanace riqon maraya yanada wahala abu kadan zaka karkace ka fada hallaka" tabe baki tayi tace “to Isah Wazirin Kano zaa kiyaye" yasan gatsali tayi masa ya juya idanunsa ya ciko da qwallah ya miqawa Addah Abulle dake saukowa daga sama wata takarda yace “ki bawa daughter Addah naso muyi sallama da ita hakan bata samu ba don Allah Adda ki kulamin da ita Amana nabarta gareku" dariya abin yabawa Addah Abulle tace “oh Ni Zainabu Abu Abdulrasheed abunnaka azimun ne wannan ya taka da matsayi take saboda rabuwa da ita kake kuka to kayi hqr guda ka bari guda zakazo ka tarar insha Allahu" Murmushin jin dadi yayi ya juya ya fice driver yajashi sai Kano daga Kano jirginsa ya daga sai Illorin zuciyarsa gabadaya babu dadi ji yake kamar yaje ya dauko yarsa suci gaba da rayuwarsu tare, daqyar yake cusawa zuciyarsa dangana saboda yasan wannan matakin shine kawai gatan da zaiyima Meenah kenan yabarta a Daura a cikin ahlinsa ko ba komai zatayi karatu koda baya gari Kuma zata samu kulawa. Koda ya sauka Benin zuciyarsa kasa nutsuwa tayi hakanan da ya tuno da Meenansa sai ya nemi nutsuwarsa ya rasa zamansa kwanciyarsa tashinsa Meenah ce keyi masa gizo da salon shagwabarta me tsayawa a rai da Hana zuciya sukuni ya rasa irin shaquwar da yayi da ita da bayajinta akan sauran qannensa, da taimakon addu'a ya samu damar ci gaba da aikinsa ya dangana saboda yasan duk nacinsa yanzu bazai samu damar karbarta hanun Mai Martaba ba. Itama farkon tafiyarsa gabadaya rikice musu tayi suka kasa gane kanta saita zauna tayita kuka idan aka tambayeta meye sai tacce Baffa'am dinta take tunani idan kaga ta saki jiki to Mai Martaba ne ya kirata yasata a gaba yake zolayarta to yanzu zata ware ta kama harkokinta a haka har ta saba da kadaicin rashin Baffanta ta saduda ta saki jiki cikin yan'uwanta Ya'isha da Amrah. Ya kasance duk safiyar duniya idan su Ya'isha sun tafi makaranta Kareem zaisa a kirata su zauna suyita karatunsu yanajin dadin koya mata saboda nandanan take daukewa a falo suke zama gaban kowa har Mai Martaba suyi karatun indai kaga sun kebe to baqi akayi hayaniya bazatabar karatu ya shiga ba, shiko Muntaz duk sanda zai koya mata saidai yajata Garden su kebe ya rinqa koya mata karatun bokon shima yanajin dadin koya mata Amma dake yasa almundahana a ransa duk yanda zatakai da ganewa sai yace bata gane komai ba haka zatayita qunci ta Hana kanta sakewa saita iya turanci saboda baqin nacinta har tafi mayar da hankali akan bokon fiye da karatun addinin Amma kullum a bata iyaba take. Hikimarsa shine idan ta matsa da son saita iya to zaiyi amfani da damar wajen cimma burinsa, babban abinda yake damun Muntaz yanda Kareem yake sanyawa duk motsita idanu sau tari idan suna garden din suna darasi shikuma sai yaje can gefe ya kama buga qwallo Sarai Muntaz ya fahimci sabodashi yakeyin hakan wannan dalilin yasa ya tattara koyarwar ya watsar. Tayi nacin tayi nacin harta hqr gashi jarabawar WAEC din da zasu zana da Baffa'am dinta yasa Mai Martaba ya biya mata takusa dama da lesson din take gane abubuwa. Tanason bawa Baffa'am dinta mamaki musamman da yace indai batamai da hankali taci WAEC ba rugarsu zai mayar da ita wannan abu ya qara tashin hankalinta ta rasa abinda keyi mata dadi. Yau ma kamar kullum suna zaune a daki Ya'isha na chat Amrah na karatun novel itakuma ta rafsa uban tagumi sai tsiyayar hawaye takeyi batason tayi asarar wannan damar Amma ta lura damar batasonta kufcewa zatayi....... Dagowa tayi tana sauke numfashi Ya'isha tace “kina damun kanki da karatun nan nifa da Mai Martaba zai yarda Allah inayin candy aure zanyi miqewa Amrah tayi tace “mema kikaji da son aure bakiga kaya ba Nifa ko a yarda ko kar a yarda Allah sai anmin aure na gaji da cin na Allah ya isa" tabe baki Ya'isha tayi tace “waisu tsoffin nan so suke su mayar damu bahuna nifa Allah badon kin takura ba da babu abinda zaisa na zubar da cikina gara susan mun girma munsan dadin maza su auraddamu ko su dauki jikokin soyayya" Katsesu Juhud tayi da cewa “nikam don Allah
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82