Chapter 78
Chapter 78
dago kanta ta zame kannnata yayi mata murmushi yace “kinajin meye game dani?" Batace masa komai ba ta fara qoqarin tashi ta nufi parlourn yabi manyan bombom dinta da kallo yana lasar lips dinsa ya lumshe idonsa Yana tunano rayuwarsu ta baya da irin soyayyar da sukewa juna, zuciyarsa ce tayi baqi idanunsa ya kada yayi ja daya tuna Kuma fah irin abinda takeyi masa shine tayima Kareem shima ko?" Tuni hasken zuciyarsa ya disashe yaji wani qunci a ransa a fili da qarfi yace “Oh God meyesa hakan ta farune..........." Juhud is not free read... regular 300 VIP 600 via👉🏼 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank Then you show ur evidence via WhatsApp 09013718241... Juhud ba littafin kyauta bane ki biya 300 regular VIP 600 kafin ki karanta ta wannan account din 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank ko katin MTN pls ban buqatar vtu hoton katin ko digit number ta WhatsApp number 09013718241..... *Oum Hairan* [8/28, 8:41 PM] Oum Hairan: Dafe kansa yayi ya koma ya zauna kalmar Innanillahi wa Inna ilaihir raji'un tana kaiwa da komowa azuciyarsa shi kansa Yana jinjina baqin kishinsa baya iya jurewa abubuwa game da Meenah tun kafin takai haka, qwafa yayi ya miqe ya fito falon tana zaune Muneefah tana wasa ya nufi inda yarinyar take ya dauketa suka nufi dinning ya hadansu abinci yanaci Yana bata tanajan gemunsa Meenah na satar kallonsa har suka gama ya miqe suka fice ta Isa ga abincin ta diba daidai cikinta ta shige dakinta taci tasha yourghut dinta taje tayi brush ta sake kwanciya Basu suka shigo gidan ba sai Tara na dare tana kwance Muneefah ta shigo Yana biye da ita da qatuwar yar tsanarta ta fada jikinta ta miqe tana mata dariya tace “sarkin yawo kin sama abinda kikeso ko Ina kukaje" Gwarancinta ta rinqayi ya nemi guri ya zauna batako kallai ba taci gaba da wasa da yarta shikuma Yana kallonsu ganin ba zai samu arziqin kulawa ba yasashi miqewa ya fice ya shiga dakinsa ta miqe tana murmushin mugunta ta nufi bathroom tayima yarinyar wanka tasa mata kayan bacci ta kwantar da ita ta kulle dakinta da key ta kwanta,. Ba wuyar bacci gareta ba nandanan bacci ya dauketa sai Kuma kashegari da safen ma shine ya tasheta ya shigo cikin shirinsa na tafiya office tunda ya shigo suka hada ido ta kawar dakai tare da lumshe idonta ya matsa kusa da Muneefah yayi kissing nata ya zubawa fuskar Meenah idanu yana ganin yanda take qifqifta idanu yaja fasali ya sauke bakinsa a kuncinta yace “kin tashi lfy" ajiyar zuciya ta saki wata kasala na saukar mata tace “normal" murmushi yayi yace “gud zanje office me kuke buqata" Kada masa kai tayi ya zaro kudi a aljihunsa ya ajiye mata yace “is ok akwai ma'aikata a gidannan idan na fita zanyi musu mgn zasuzo kowa zai gabatar miki da aikinsa idan kina buqatar wani abu ko baby akwai dan aike saiki bashi" jinjina kai tayi ya sake sunkuyawa yayi kissing Muneefah ya fice tana binsa da kallo ita mamakin sanyinsa takeyi cikin kwanakin nan ta lura ya sauko sosai don ita kanta tasan da Rasheed din dane rainin hankalin da takeyi masa da tuni ya ladabtar da ita Amma yanzun ta fahimci kamar bama abun na damunsa. Da wannan tunanin ta miqe ta shige bayi tayi wanka ta gyara jikinta ta fito tasa kayanta ta sanya dankunne ta nufi kitchen ga mamakinta a dinning ta tarar da kayan Karin kumallo ta fara budewa ko baa fada mata ba tasan aikinsa ne doya ce da taji qwai sai miyar albasa da attaruhu sai ruwan tea a flast da kayan hadi a gefe taja fasali ta zauna ta fara bawa cikinta haqqinsa taji dadin break din sosai tana Shirin tashi ma'aikatan suka shigo mace daya maza biyu suka gaisheta ta amsa musu macen tace “ranki ya dade ni sunana Jummai daga Daura Yallabai ya kawoni nan aikina shine shara da mopping da wanke² sai kula da Muneefah yace tsarin gdansa baa masa girki shine yakeyi ko Kuma ke kiyi" jinjina kai tayi dayan yace “nikuma sunana Hadi duk abinda ya shafi fita unguwa da aike zuwa waje alhakinane" juyawa tayi da dayan yace “nikuma dan ruwa ne aikina shine kula da fulawa da wanki da guga ranki ya dade sunana Badaru" yanda yayi mgnr yabata dariya tayi murmushi tace “yayi kowa yaje yayi aikinsa" Godiya sukayi suka fita kowa ya kama aikinsa Jummai ma ta fara gyaran falon ita Kuma ta shiga dakinsa ta gyaro ta kunna masa turaruka ta fesa na fesawa ta wanke toilet ta fito ta shiga nata shima ta gyara biyun da suke rufe ne kawai bata shiga ba ta koma tayi kwanciyarta ta rashin aikinyi har daya sannan ta fito ta dora girki Jummai nayi mata hira har suka gama suka Muneefah nata wasanta tayi wanka ta shirya cikin wata atampa blue tayi mata kyau dinkin doguwar riga me aljihu tayi sallar la'asar ta kunna kallo tana kallo tana chat har biyar sannan taji tsayawar motarsa ya shigo da kaya niqi² a hannunsa Jummai ta miqe tana masa sannu da zuwa itakuwa hakimar kawar dakai ma tayi yasan tayi ne don yaji haushi yayi murmushi ya aje kayan yace “barka da gida ranki ya dade Allah ja kwana ya qara lafiya fulanin gobe" duk yanda taso da shareshi dole Saida yasa tayi murmushi tace “sannu da shigowa" cire rigarsa ta sama yayi ya rage dagashi sai singlet ya qarawa A.C gudu yace “nasha wahala yau inata qoqarin naga tafiyar nan bata ritsa dani ba Amma Saida ta fado kaina Meenah banson tafiya nabarki wlh....." Ai tuni ta fara hada gumi ta juyo da sauri tana cizge dankwali tace “tafiya Kuma Baffa'am tab wlh aa bazaa Kuma sakani a tara ba nikam qafata qafarka" Murmushi yayi Yana kallonta a zucci yace yar iskar qarya zanyi maganinki ta ruwan sanyi ni zakiyiwa hauka! Amma a fili sai yace “to ya zanyi Meenah Babu damar tafiya da iyali Australia sunada mugun sanyi dole sai kaje kaga yanayin gurin tukunna ko zaka dauki iyalinka Kuma ma Banda abinki mu ai zaman gaba mukeyi Inna tafi dake amfanin me zakiyimin abinda bakaso ai nesa kakeyi dashi ko?" Girgiza kai tayi ta zame qasan kujerar tace “nikam mubar batun wasa wlh nasha wahala a wancan karon har zaucewa Saida nayi Saida Mom da Mai Martaba suka rinqa sawa ana yimin addu'a sannan na dawo hankalina ya Rasheed don Allah ki million nawa ne kabasu subarmin kai a gida ni idan bamaka dashi zansai da shanuna da Kaka ya karbarmin gurin dangin mahaifi na nabaka kabasu subarmin kai kaji?" Tana mgnr muryarta na rawa. Shima zamowa yayi ya zauna a gabanta ya riqo hannunta yanajin wani spark na jijiyoyinsa saboda rabonsa da riqe hannun mace haka shekara an tafi takwas kenan, jan wani numfashi yayi yace “kinaso na ne?" Tambayar ta daketa ta dago da sauri idanunta ya kawo ruwa yayi saurin dora hannunsa a bakinsa yace “aa ba kuka ba tambaya ce my Meenah kinasona?" Daga masa kai tayi ta fada jikinsa ta rushe da kuka tana cewa “don Allah don Allah Ya Rasheed please kada ka sake tafiya kabarni wlh zaucewa zanyi....." Hade bakinsu yayi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82