Chapter 21
Chapter 21
baqin....." Bugu yakai mata suka zuba a guje yana cewa sai kin fadamin waye dan baqin ciki yarinya itakuma tanayi masa gwalo da haka har bangaren Mai Martaba tana shiga ta shige bayan Mai Martaba tana dariya shima dariyar yayi ya janyota ta lafe a jikinsa yace “ya akayi ne Aminatu sarkin wasa kekam kamar ba yar soja ba" tana haki tace “ba Ya Kareem ne yakemin baqin cikin hawa cinyar Baffa'am dina ba don Mom tace saura wata biyu ya dawo" murmushi Mai Martaba yayi yace “aifa kaima ka taro March inakai Ina shiga tsakanin ya da ubanta wannan ai sai Allah" gwalo ta qarayi masa yace “to kagani fah Mai Martaba gwalo takemin" daquwa ya watsa mata yace “tayi din kaine babban kwabo ai" zama yayi shima suka fara karatun anan inda batayi daidai ba ya ranqwasheta kafin su gama duk ya tara mata gajiya ta narke tace ita bacci takeji dakansa ya rakata har qofar falon Muntaz na tsaye a harabar gdan fuska duk tayi dameji yayi qwafa ya shige dakinsa shikuma ya qarasa rakata ta shiga dakin nasu sukayi sallama. Goma da rabi Amma babu kowa a dakin daga Amrah har Ya'isha kayanta ta cire ta daura towel ta fada wanka tayi wankanta cikin nutsuwa ta bude qofar zata fito taga duhu dakin tace “subhanallah An dauke wuta Bari na jira a kunna inj....." Mgnr qin qarasa fitowa tayi qirjinta ya doka da qarfi jin motsi a dakin cikin rawar murya tace “Am...rah.... Ya'isha yaushe kuka daw....." Nan ma kasa qarasawa tayi jin an rungumeta ta baya a razane tace “please Amrah nace miki banson wannan wasan ki daina Allah zan fadaki......" Wutar jikinta ce ta dauke jin an Sanya hannu an janye mata towel din jikinta an dora hannu saman qirjinta ta bude baki tasa ihu nandanan taji an saketa daidai lkcn da su Ya'isha suka banko qofar da sauri Amrah a lkcn ne Kuma wutar ta dawo tayi tsaye sangalgal babu komi a jikinta sai rawar baki data jiki takeyi da sauri Ya'isha ta matsa ta dauki hijjab ta zura mata suka dubeta sukace “yadai Baby meye ya faru?" Sai lkcn kuzarinta ya dawo ta fara dube² a dakin cikin firgici suma dube²n suka fara suna tayata ta fara bankada labule itane har qarqashin gado Amma bataga kowa ba suka dubi juna Ya'isha tace “wai meye kike nema?" A wahalce tace “mutum" kallon juna sukayi sukace “mutum Kuma?" Jinjina kai tayi sai lkcn taji hawaye ya qwace mata tace “wanka na fito kawai naga wuta ta dauke Ina tunanin kune naji an rungumeni ta baya kafin na gama saita natsuwata aka yagemin towel shine inayin ihu naji kamar an fita da gudu Kuma sai gaku kun shigo don Allah ko kune kuka tsorata Ni?" Numfashi suka sauke a tare Amrah tace “wlh bamu bane muma da muka shigo ihunki ne yasamu takowa da gudu wannan gdan wani banzan gdane kowa Yana bangarensa sai a saceka ma baa sani ba" Zama tayi cikin mugun tashin hankali suma suka zauna Amrah na binta da kallo tace “kece da shekiyar gardamarki da kin bimu Aida bakiyi gamo ba Kuma ko banza kyaga gari" numfashi ta sauke tace “to waiko inada Aljanu ne?" Dariya abin yabasu Ya'isha tace “to waye ya sani ni Amrah fito Mana da qwalam dinmu mu dan lasa Amma wlh yau Shafiq ya wahalar dani shege inaga magani yaje yasha ya gaji da miyar da nakeyi masa baya qosar dani" Amrah ce ta cafe da cewa “ke yau ni kinsan sabon kamu nayi wani alhajin birni infada miki quarter million yasamin a account yace next week zai dawo" tafawa sukayi itadai tana zaune tana kallonsu suka dauko ledojin da suka shigo dasu suka baje Ya'isha tace “sauko kici rabonki" girgiza kai tayi suka miqe sukace “aikuwa baki isaba yarinya dole kici" danna mata tsiren sukayi a baki ta lumshe idonta tana taunawa suka sata a gaba suna dariya saukowa tayi tasa hannu sukaci sukayi hani'an. Bayan sun nutsa ne Ya'isha tace “nayiwa Saleem alqawarin gobe zan taho dake yace dubu dari zaibani tukuici idan Kuma kin amince yazo gda" dagowa tayi tace “aa nidai kar yazo banason zuwansa wancan zuwan da yayi Ya Kareem kamar zai cinyeni saboda masifa har cewa yayi zai fadawa Baffa'am" Tsaki sukaja a tare Amrah tace “ke muguwar bahuwa ce waike meye yasa bazaki waye ba koda yake dama ance sai mutum ya shekara arba'in yake wayewa badon hakaba kawai kita nuqu² da kayan dadi a jikinki saidai ki wanke kisa masa pant yayi gashi ki aske babu me mora" watsa mata harara tayi tace “ai cikar mutuncina kenan" wata dariya suka kwashe da ita sukace “sakarya ita ajiya yanzu haka mijin da kike adanawa ma yana kwance da wata zaa daura masa aure dake Kinga ta banza kikayi, tabe baki tayi tace “eh shida ubangijinsa nidai nafiso na hadu da nawa salin alin murmushi sukayi sukace ai saikitayi aikine be isheki ba duk gindin da baayi masa susa ya zama sorry rayuwar ga ta hutawa daga duniya sai Habuja aljanna tamai rabo" Da wannan tasa rigar baccinta ta juyansu baya tayi kwanciyarta tanajin kowacce na waya da saurayinta itakam ko a jikinta washegari da wuri ta tashi tayi wanka tayi sallah ta fito ilai kuwa ta iske malamin nata a falo yana duba wani littafin addini ta isa gabansa ta zauna suka gaisa cikin larabci kamar yanda ya sabar mata ya zuba idanunsa akanta yanajin saqon daya dade yanayi masa yawo a zucci na tasowa hadda take kawo masa shikuma hankalinsa nakanta Saida ta gama ta dago taga yanda ya kafeta da ido taja numfashi tare dakai hannunta idonsa ya qifta da sakin wata babbar ajiyar zuciya ya fara Bismillah sannan ya fara yimata qari bayan ya gama biya mata suka koma Hadith suka sake gangarawa tajweed haka ya rinqa karbar haddarta mataki mataki yana sake ware injin idonsa akanta gabadaya yau kallon da yakeyi mata yasa ta kasa sakewa dashi suna gamawa ta miqe ya riqo hannunta yace “na takura miki ko?" Qasa tayi da kanta tana wasa da yatsunta yaja numfashi ya qara rage sautin muryarsa yace “wasu fararen kyawawan furanni ne suke sauka saman shararriyar hanyar da babu komai a samanta sai wasu korayen bishiyu da suka kewayeta gefenta Kuma ruwa ne yake kwaranya ta saman wani farin dutse a gefen dutsen wata yar bukka ce irin taku ta fulanin asali tsuntsaye nata shawagi dangin su Kanari Dawisu Jimina Alhuda'huda dadai sauransu" Gabadaya ya dauke mata hankali da lbrn nasa jin yayi shiru ne yasata dagowa ilai kuwa idanunta ya fada cikin nasa kwarjini yayi mata irin zaman da yayi saman kilishin dole ne ka kiyayeshi yayi murmushi yace “ina tafe cikin nutsuwa Amma zuciyata matse take data isa inda wannan bukkar take wacce ta gefenta ruwa yake gudana take, Ina isa naja na tsaya saboda wata busar sarewa me kashe jijiyoyin jiki dake tashi ta cikin wannan bukka tare da wata zazzaqar murya tana rera waqe cikin harshen fullanci" sake tsagaitawa yayi ya hadiyi yawu can yaci gaba da cewa “bansan wace a ciki ba Amma zuciyata ta kwadaitu dason ganin mamallakiyar wannan murya me saukar da kasala Kuma me irin suffar matan aljanna,
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82