Chapter 10
Chapter 10
wanda yayi yunqurin hanata kukanta saboda sun fahimci damuwarta bata buqatar rarrashi lkc ne kawai yake da ikon rarrashinta, itadai a wannan dare idan barawo ya rintsa Juhud ta sake Rintsawa saqawa take kawai da warwarewa ta taba lalitar jikinta yakai sau uku taji wadannan abubuwan da Innatu ta bata sunanan. Da asuba Nurse Karima ce ta taimaka mata ta kaita bayi tayi alwala babu damar wanka saboda baa buqatar ruwa ya taba ciwon dake qirjinta a zaune tayi sallar duk da cewa ba wani ilimin addini ne da itaba cikin surorin qur'ani uku ta iya Fatihatul kitabi Iklas da Khausar su dai take karantawa a duk wata sallarta bayan ta idar ta daga hannunta tanason yima iyayenta addu'a Amma bakinta yayi nauyi ta kasa furta komai sai yararin hawaye da batasan ta inda yake fitowa ba da yakebin kuncinta ganin cewa addu'ar batta samuwa yasata sauke hannunta ta juya ga Nurse Karima dake hada kayanta tace "inane nan?" Juyowa tayi tace “barikin sojoji ne" wani dam gabanta yayi tace “bariki Kuma oye ayye na shiga Sha biyu waye ya kawoni nan....." Mgnr ce ta maqale lkcn da taji an turo qofar an shigo wani qamshi ya gauraye dakin nurse Karima ta Sara masa tace “Sir Alhmdllh anyi nasara petiant dinka ta samu lfy Amma....." daganta hannu yayi yace “nasan me zakice jeki kawai banson surutu" sumsum ta fice yaja tsaki ya juya ya zuba idanunsa ga Juhud daketa barin jiki yau taga mala'ika ido biyu a rayuwar Juhud babu abinda take tsoro kamar Soldier batason ko a hanya su hadu yau gata a cikin barikinsu wannan wacce irin masifar qaddara ce daga wannan sai wannan? Inuwarsa da taga ta lullubeta yasata dago kanta kafin ta gama sauke idanunta akansa fitsari ya fara qwace mata hakan yayi daidai da lkcn daya daka mata wata uwar tsawa yace “meye hakadin banason shashanci sanyi kikeji da zaki rinqq wata tsumar jiki?" Kafin ya rufe bakinsa ta saki kuka me gunji cikin kukan take cewa “ni dama nasani mutuwar Innatu bazata taba zamemin Alkhairi ba wlh gara na mutu na hutt....." Ko kadan bai daukan shirme da raini hakan yasashi shaqota ya miqar da ita ta rintse idonta lkcn da shikuma yayi saurin sakinta saboda qarnin manshanun daya shaqa a hancinsa daya sanyashi jin amai ya yunquro masa da sauri ya nufi bathroom din ya fara kelaya aman ta miqe zaune tana jan zuciya har yanzu jikinta rawa yakeyi. Fitowa yayi daga bathroom din yana qwafa baiko tsaya a dakin ba ya fice ya jima da fita kafin ya dawo dauke da wata jaka a hannunsa ya cilla mata yace “kije kiyi wanka ki cire abinda yake qarni a jikinki bana zama inuwa daya da qazami" Dagansa kai tayi cikin yanayin tsoro ya sake ajiye gongonayen Madara da Milo da nescafe ya fita can saiga wata Christy ta shigo dauke da flast na ruwan zafi da wata kula a hanunta ta aje ta juyo ta watsawa Juhud wani dan iskan kallo ta tabe baki tace “gashinan yace ki tashi kiyi break kafin ya dawo" ko kallon tsiya bata samu gurin Juhud ba balle na arziqi bama tasan tanayi ba ta lula duniyar tunanin rayuwarta ta baya hakan yabata damar qare mata kallo taja tsaki a ranta tace “dubeta kamar aljana" a fili Kuma waya ta dauka ta Kara a kunnenta tayi turancinta Juhud ta juyo da sauri ta kalleta sai taji ta burgeta tanason mutumin da ya iya turanci a rayuwarta a fili tace “lah gwaggo kin iya turanci nima zaki koyamin?" Dariya abin ya bata ta Harareta tace “saboda yar iskance niba me zai hana na tsaya koyawa bakin da bai iya ko A ba turanci qazama dake" bataji haushi ba domin ko dukanta zatayi indai akan turanci ne to zata jure “qwalqwal tayi da ido tanason yin mgn ya turo qofar gabanta ya Fadi tayi saurin zubansa ido sai yanzu ta ganeshi tace “lahhhh Kado dama kaine ashe kaine wanda ka siyemin nono na ranar da su Baffa Ribado suka qonemin Innatu na...." Shiba ma'abocin dariya bane hakan yasashi shafa sumarsa yace “dan uwarki waye Kadon?" Nandanan ta nutsu ganin ya nufota yace “wato ke dama da ganinki zakiyi raini nace kiyi wanka shine saboda kin quna kamar yanda aka qone Innatu kikaqi yi salon ki qara sani amai jibi babu abinda yake tashi sai qarnin manshanu a dakin nan" Kallon Christy tayi idanunta sun ciko da qwallah da sauri Christy ta dauke idonta tace “baby kace qanwarka ne Kuma naji tana mgnr tallar nono ya haka?" Harara ya maka mata ya juya ga fast din tea din ya dauki cup ya hada mata ya miqa mata da biredi sai soyayyen qwai da dankali, tea din ta karba hannunta na rawa dama yunwa takeji sai bread din ta soma turawa yanda takecin abincin a yunwace yasashi zama ya zuba mata ido ta cinye bread din ya sake yaga ya bata ta Kuma cinyewa tama manta da shayin Saida taji ta qoshi sannan ta kora da shayin ta ajiye kofin tayi gyatsa ta rinqa kallon qwan tana girgiza kai. “Ya sunanki?" Abinda taji ya fada kenan ta juyo da sauri tace girogal..... Da mamaki da takaici ya dubeta yace “sunanki kenan girogal?" Dagansa kai tayi tace “ayyah Kado tausayinta nakeji yanzu shikenan kun cinye mata qwanta da kinbar mata da ta haihi yaranta ta rinqa jansu suna tahiya kiwo" wata muguwar dariya ce ta qwacewa Christy lkcn da taga ya dafe kai ya juya ya galla mata harara ta gimtse dariyar kawai taga yakai hannunsa ga wandonsa ya fara zaro belt dinsa nandanan ta nutsu ta saita hanya tasan dukansa sai tayi wata guda tana jinya Juhud nacan tana sharar kwallah tana cewa Allah sarki girogal Allah shine zai saka miki kamar yanda zai sakamin nima....." Qara ta saki lkcn daya zumbuda mata belt din tayo qasa ta fadi aikuwa ta shige qarqashinsa tana ihu ya qwace qafarsa yace “ina tambayarki kina yimin hauka" da sauri tace “Aminatuh Juhud Baffa Haro Innatu Indo....." Jefar da belt din yayi ya dafe kansa ya fice daga dakin ya nufi gidansa yana shiga ya zube a kujera yace “Rasheed ka daukowa kanka da shegen kwashe²nka fitowa Christy tayi daga daki kasancewar ta rigashi shigowa ta zauna tana matsa masa qafa tace “baby anya yar qauyen nan qanwarka ce?" Cikin hassala yace “bansani ba kada ki Kuma tambayata game da ita meye damuwarki da sanin wacece itan?" Jan bakinta tayi ta tsuke yaja tsaki ya miqe ya shiga dakin da baya amfani dashi a gdan ya soma gyarawa kasancewar shima kamar dakinsa yake da katifa da wardrobe da TV na bango sai bathroom, Gyara yayi masa na sosai sannan yayi wanka ya fito ya fice daga gdan cikin gari ya shiga ya nufi wani Mall ya siyowa Juhud kaya bazai iya tantance tsayinta ba Amma ya qissimata da Ya'isha qanwarsa duk kayan daya diba mata qananu ne sai hijjaban sallah ya koma gda ya tarar da Christy a kitchen tayi masa sannu ya Amsa Yana shigewa dakin daya gama gyarawa ya zuba kayan a wardrobe ya dauki mukulli ya fito Christy ta tareshi da cewa “ga abincin petiant din nan am naji kamar tace sunanta Aminatu
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82