Chapter 47
Chapter 47
Sanya kayan a mota Mai Martaba ya iso gurin yace “ya subhanallah meye Kuma hakan Ina zaka?" Juyowa yayi idanunsa sun kada sunyi jawur ya dubeshi ya kawar dakai Alh Aminu ne ya matso shima lkcn Rasheed din ya koma cikin gdan ya figo hannun Meenah ko dankwali Babu akanta Mai Martaba daya fahimci barin gidan yake niyyar yi yace “wai ba mgn nakeyi maka bane" a fusace ya juyo yace “banaji Mai Martaba banji abinda kaceba ka kauce kabani guri yau kam ko baku koreni ba na gama zaman gdan sarautar nan akan matata zan iya hqr da komai....." Muryarsa ce ta sarqe ya jefata a mota ya kulle har yanzu kuka takeyi yama kasa rarrashinta ya sake kallon Alh Aminu ya nunasa da yatsa yace “ka sanar da munafukar matarka ni Abdulrasheed nafi qarfin yayanta a aure kun bani Zulaihat banaso na karba Allah ya dubeni ya kasheta kun bani Hidaya na sakar muku kayarku shine yanzu zaku liqamin bazawara kwancen wasu saboda kun Mai dani jani talau waima ni kadaine da namiji ne a gidannan Ina Salman Ina Arman Ina Kareem Ina Muntaz hatta Urwat kukayiwa aure zama zaiyi da matarsa saini akanme zaku sanyawa rayuwata idanu ne banaso na fada muku banaso wlh tallahi zanci mutumcin duk ubanda ya qara tunkarata da mgnr aure auren banza auren wofi da har zaku sanyawa matata tsura akansa aiba ita ta hanani ba nine naga batada tamka bare mahadi, Abu na qarshe ka fadawa Bilki ta kiyayi dawowata gdannan Kuma ta shirya Amsa Kira kotu saita fadamin uban wa matata ta kashe da take fadawa duniya cewa in mutum ya cika rabar Meenah saidai yajishi a Ramin kabari?....." Sosai Mai Martaba ya girgiza da yanayin Rasheed din yasan tabbas yau yakai qarshe akwai gagarumar matsala idan yabarshi yabar gidan dama Meenah ce zatake kawoshi tunda shi dama asalinsa bayada ra'ayin zaman gdan sarautar to ya dauke abarsa meye Kuma zaisa suganshi? Mai martaba na Shirin mgn Mom ta iso gurin ita da wasu mata su uku dole tasashi yin shiru ta kama hannun Rasheed tajashi gefe sun jima suna bugawa kafin ta shawo kan kayanta Yana kuka kamar wani yaron goye daqyar ta lallabashi ya yarda zaibar Meenah a gidan sarautar Amma da angama biki da ita zai tafi. Zuwa tayi ta fito da ita a mota ta janye mata sumar data rufe mata fuska tana ganin Mom din ta fada jikinta ta sake rushewa da kuka itama hawaye ta share tana tausayawa rayuwar Meenah Babu uwa Babu uba babu shaqiqin dan'uwan da zata zanta dashi taji dadi ga rayuwar taqi mata dadi wata murya taji ta bayansu tace “kiyi hqr Aminatuh komai yayi tsanani sauqi na zuwa hakanan Allah yake jarabta bayinsa zababbu domin ya gwada imaninsu ba sonki ne bayayi ba qaunace ta kawo miki hakan bantaba ganin Wanda akayiwa irin wannan qazafin ya qare rayuwa a wulaqance ba ko baizama wani ba zai samu yardar Allah" Juyawa tayi ta zubawa matar idanu gabanta ya yanke yabada wani rass ta janye jikin Mom da sauri tana qara kallon matar tare da langwabar dakai a rayuwarta nata taba ganin kamar tsagin Kara irin wannan ba kama haske da jiki inda kasan innatun ta a hankali ta sauke ajiyar zuciya tace “mom wannan fah?" Dadine ya cika mom ganin ta fara warewa tace “Wannan Kharimatu kenan qanwata ce babanmu daya daga Mali suke ita da Mamanta Hamida kinganta can" juyawa tayi ta kalli dattijuwar matar da tayi tsufan jin dadi fatar nan kamar a matsa a tatsi jini tana sanye ds farin tabarau tayi mata murmushi ta bude mata hannu ta fada jikin matar hakanan takejin wata nutsuwa na ratsata da kwanciya a jikin Kumbo Hami Kumbo Hami ta shafa kanta tace “kiyi hqr jikata zakiga ribatai a gaba munci wannan baqin cikin nida babbar yata Aysho tana jaririya a tsumman goyo aka koremu daga gdan babansu Aishatu surukarki......" Kuka ne ya qwacewa Kumbo Hami ta share qwallarta tace “saboda qin jini da yanayin qabila wannan abu yake bibiyarmu kamar garin Bodde wani babban garine da yake cikin Qasar Mali So garin yazamo kamar Biddah a Nigeria sunyi qaurin sunan asiri da maita Wanda ba dukkan garinne suke da wannan hali ba su masu yinma sune kaso mafi qanqanta. Baffana attajiri ne a garinmu a zahiri bama maita bama tsafi Amma saboda dukiyarsa yasa ake cewa shine shugaban mayun garinmu Baffa Garbu wato babansu Aishatu surukarki yaron babana ne hakan yasa yabashi aurena tunda nazo garin lkcn baa auro uwayen su Aishatu ba matan gidan suka tsangwamin Kuma Allah dabawa mugu dama haka akayita rashe rashe a gabar tun baa yarda har suka amince da gaske ni mayyace hakanan na haifi Aysho ranar dana haifeta Garbu bayanan uwarsa tasa aka daukemu akaje bayan gari aka yasar damu daqyar na iya komawa Mali daga Senegal naci gaba da rainon Aysho Garbu nasona Amma bashida ikon dawo dani domin babana ya fusata hakan yasa Aysho nada shekara goma ya karbeta a gurina sai labari naji ya auradda ita ga dan qanwarsa ya taho da ita Nigeria tun daga wannan Rana nakebi akaini inganta nakasa samun dama dakaina nazo Nigeria neman Ayshatu na ban dace ba a qarshe dai nama hqr domin jikina na bani Ayshatu bata raye don da tana raye inni ban nemeta ba ita zata nemeni, bayan na rasa Ayshatu ne qulafucina da son naganta yasa na komawa Alh Garbu shine har na sake haihuwar Kharimatu, Aminatuh yanzun komai ya wucce bayan ansha wuya kema idan kikayi hqr watarana zai wucce"........... Juhud is not free read... regular 300 VIP 600 via👉🏼 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank Then you show ur evidence via WhatsApp 09013718241... Juhud ba littafin kyauta bane kada ki biya 300 regular VIP 600 kafin ki karanta ta wannan account din 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank ko katin MTN pls ban buqatar vtu hoton katin ko digit number ta WhatsApp number 09013718241..... *Oum Hairan* [8/2, 6:36 PM] Oum Hairan: *0026* Jinjina kai Juhud takeyi da jin wannan rikitaccen al'amari tabbas duniya ta cika da mutane marasa tsoron Allah saidai kayi fatan Allah ya dada maka Imani kawai, dubanta Mom tayi tace “Kumbo Hami itace ta riqeni tun bayan rasuwar mahaifiyata banida uwar data fita a duniya Meenah" sosai Meenah taji dadi da ganin dangin surukar tata hakanan taji tanayi musu wata qauna me game jini suma sosai suke nuna mata qauna da kulawa sun jima sosai a sashin nata sunata hirarsu gabadaya su anan suka qarashe bikinsu basajin Hausa sosai hatta Rasheed fullanci yakeyi musu wannan tasa Juhud sajewa dasu. Kwana uku aka dauka ana bikin qofar falo Rasheed hana Juhud zuwa yayi da sunan biki to itama bata matsa ba ganin Mom ta goya masa baya a gdanta tayi nata bikin saidai tasa ta cire kawai idan yaga garara mutane sunwa bangaren sauqi yasata a corner yayita hadanta aiki ta rasa a wanne bigire zata aje Rasheed irin mazan nan ne masu jarabar nacin masifa shi indai zaki dagansa qafa to bakida matsala dashi idan har kaga Yana ciccin mazu to ya nema anyi masa rowa ne. Tunda ta fahimci haka itakuma taci alwashin kozata wahala indai ya nemi haqqinsa zata bashi domin shima Babu ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82