Chapter 11
Chapter 11
ko?" Warmer din kawai ya karba ya fita ya nufi asibitin lkcn ta shiga wankan da Nurse Karima ta takura mata tayi kasancewar an kwance bandejin saura dinkin ta Nina mata yanda zatayi wankan sannan ta barta koda ta gama wankan ta dauki riqarta ta mayar ta fito riqe da towel din da Nurse Karima ta bata domin daurowa. Da sauri tayi baya jikinta ya kama tsuma tana ganinsa ta tuna da dukan da yayi mata dazun ya kuwa daure fuska yace “kici abinci na kaiki gda na gaji da yawon asibitin nan ba Mai martaba ne babu lfy ba ba Mom ba" ajiyar zuciya tayi ta rinqa takowa da sanda dariya kecin Karima babu halin yi, a haka harta iso ta karbi doguwar riga ta rinqa juyata a hannunta tana kallon duwatsun jikinta sai ta ajiye ta Kuma daukar wata taga har tafi ta farko kyau a haka Saida ta gama qarewa kayan kallo duk ta ajiye ta dauki rigarta ta Fulani zata mayar Karima tayi saurin riqewa tace “meyesa bazaki Sanya wadannan ba?" Turo baki tayi tace “dagawa da almubazzaranci niba yar kowa ba haka kawai nasa kayan sarakai salon asani a wutar jahannama ........ Kallon da ta dago taga yanayi matane yasata rufe bakinta da hannunta yayi Alama da yatsansa Karima ta dauki wata milk ta miqa mata ya kafeta da idanu babu yanda ta iya hakansn ta karba tasa tana qunquni tana hawaye ita a dole anyi mata laifi ansata almubazzaranci.🤣 Flat ya dauka ya zuba mata tuwon shinkafar da miyar agusi da tantaqwashi da qashin rago ya aje mata a qasa ta ya sake kafeta da idanunsa tayi qasa da nata tare da zama a qasan ta Sanya hannu tana jajjagula tuwon tana gutsurar gaya tanaci idan ta dauki saita goge miyar sannan takai bakinta, Karima ce taga abin yayi yawa tace “meyesa bakicin miyar" kamar me jiran kadan kuwa ta fashe tace “bayan mun fada muku kudaina cinye kaza da shanuwa da tumaki Amma kunqi ku Kadawan nan bakuda Imani nikam bazanci nama ba idan naci sai Allah yayi Mana hisabi" Ba Karima ba shi kansa Saida ya murmusa ya zubanta ido yanda take tsakurar abincin take karkade miyar abin yaso bashi dariya saidai bazaiyi ba ta samu fuskar rainashi haka ya tsaya akanta Saida ta cinye tuwon sannan ya zauna yana karkada qafa yace “uhum maza cinye naman ki shanye miyar...." Yanda ta zaro ido yaso yasa dariya ta kubce masa ya maze yace “idan kinqi" hannu yasa Yana qoqarin zare belt dinsa tayi saurin daukar kwanon ta kafa baki ta shanye miyar tas sannan ta rinqa yagar naman kamar tana yagar jikinta har Saida ta cinye ya miqe ya dubi Nurse din yace “tayata fito da kayan nan zata koma gda ta rinqa zuwa ganin likitan kafin ta qarasa warkewa" ficewa yayi Karima ta debi kayan ta fita ta miqe tabita da sauri ai tana zuwa jikin motar ta cake taqi gaba taqi baya tsoro ya kamata ta janye ta koma gefe ta rakube bayan sun gama zuba kayan ya juyo ya kalleta tayi wani kalar tausayi ta sakeyin raurau da fuska yar fara'ar da yakeyi ya daina yace “kizo ki shiga mu wucce malama" girgiza masa kai tayi ya cije lebe a fili yace “ciwon kai wannan yarinyar zatayi taurin kan tsiya" itadai bataji me take cewa ba Kuma bata bar inda take ba Saida ya daka mata tsawa tayi saurin nufar motar tana zuwa gabansa ta zube cikin in...Ina tace “ka rantse bazaka saidani ba Baffa'am yace masu sulluwa suke sace mutane suna kaiwa burnin Kano da Lagus suna saidawa anayin fate²nsu............. *THIS BOOK IS NOT FREE... REGULAR GROUP 300 VIP 600 VIA BANK ACCOUNT 0255526235 FAUZIYYA TASIU UMAR GTBANK OR CARD FOR THIS NUMBER 09013718241 ONLY WHATSAPP OR VTU ONLY FOR DIS 09031307566* *Shares Please* *Oum Hairan* [7/15, 7:34 PM] Oum Hairan: *JUHUD* *(OUM HAIRAN)* *( Pure love sex nd romantic)* *FREE PAGE SEVEN 7* *SANARWA* Wannan littafin na kudine idan kina buƙatar ci gaba da samunsa bayan gama free page kiyi ƙasa a ƙarshe an faɗi hanyoyin da zakubi don biya da karatu cikin Aminci. *SUBSCRIBE* _DUNIYAR LITTAFAN HAUSA TV_ https://www.youtube.com/channel/UCcAjVQ74qod9_dL0e_AqkiQ *CIGABA* Wani takaici ne ya cikawa Rasheed ciki ya sanya hannu ya dagota ya cillata a motar yana mita Yana cewa “wata wawuya dake to ke ko Ina Saida mutane tsada zakiyi da zanyi wahalar kashenki kudi a asibiti ki warke na kaiki kasuwa" figar motar yayi ya nufi gidansa parking yayi ya bude motar tun kafin ya bata izinin fita tayi wuf ta fita ta kama kwara amai ya tsaya jikin motar yana kallonta harta gama yaja qwafa ya shige gda, komawa tayi jikin motar ta tsaya tana jiran yazo ya tafi da ita amma shiru Saida taga abin bana qare bane sannan ta Sanya kai a gidan tana kalle² batakai da shiga cikin falon ba ta tsaya gurin wata fulawar roba me hoton tumatur ta kuwa zame a gurin tana kallon flower tana dariya tana cewa Allah na gde maka yau zansha tumaturi na qoshi dama rannan dana sato na gonar Mal Yusha'u bansha ba akace yayi gyewayar qur'ani" Hannu takai zata balli tumatur din Rasheed dake fitowa a daki ya dakanta tsawa ta miqe zunbur jikinta na rawa ta koma gefe ta maqale hanya ya nuna mata yace “oya zoki shige ciki banson hauka fah" sumsum ta kama hanya ta shigo falon tare da sakin baki tana kallon ginin karo na farko a rayuwarta data taba shiga gini irin na qasa daga kai tayi sama taga fanka na wulwulawa aikuwa tayi tsalle ta maqaleshi tana ihu tana cewa “zai fillemin kai wannan abun don Allah a taimakeni kada ya filleni" daqyar ya bambareta a jikinsa ya figeta ya wullata dakin daya gyara mata ya juya ya fice nan dinma rintse idanunta tayi ta maqale jikin bango ta qudundune tanata tsuma qarar fankar na qara razanata tsayin lkc tana a haka sannan Allah ya jefo Christy ta tsaya ta zubanta ido tare dayin qwafa tace “dan kauye meye aka din" bude idonta tayi kadan tana nuna mata fankar tace “zata filleni ki hanata....." Dariya abin yabawa Christy ta Sanya hannu ta kashe fankar sana ta qarasa shiga ta bude wardrobe din kayane shimqim. Cije lebe tayi tare da girgiza kai ta dubeta tace “dallah yar qauye ki tashi kije Yana nemanki" harararta tayi ta miqe tsaye tana dafe qirjinta ta nufi qofar ds taga itama tabi suka fito suka iskeshi a falo yana latse²nsa da waya zama Christy tayi kusa dashi ta kwantar da kanta a cinyarsa inda Juhud tayi saurin kawar dakanta tare da zamnawa nesa dasu kadan, ya bata kusan 20 minutes kafin ya dago idanunsa kasassu ya dubeta sosai Yana nazarinta. Can yayi gyaran murya yace “daga wacce rugar kika fito?" Idanunta ne ya ciko da ruwa ta sunkuyar da kanta tana wasa da yatsunta har Saida ya qosa yayi mgn da qaraji yace “wato ke yar iskace naga alama bana mgn biyu sau daya nakeyi Amma kina neman mayar dani wani playing man dinki tambayarki nake daga wacce rugar kika fito Kuma meye dalilin barowarki gda?" Cikin rawar murya ta tsoro tace “rugar Wandu" zubanta ido yayi kafin ya Kuma cewa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82