Chapter 57
Chapter 57
gado rungume da wani hoto a qirjinta sai kuka takeyi me ban tausayi. Wani abu me nauyi ne yazo ya tokarewa Kareem maqoshi ya furzar da iska me zafi ya juya ya fice daga dakin sai Mai Martaba ne ya qarasa shiga ya kamo hannunta Babu musu ta miqe tanaci gaba da kukanta idonta lullube da alqyabba ya fito da ita harabar gdan Ya'isha ta nufosu da sauri suka sanyata a mota tana qarawa kukanta sauti tana Kiran sunan Baffa'am Sarki junior dukkan wanda yake a gurin hatta Mai Martaba Saida tasashi sharar hawaye. Hakanan suka nufi unguwar da gidan nasa yake Mai gadi ya bude musu suka shiga sukayi parking Aunty Hamida ce take riqe da hannunta har cikin gdan suka haura da ita saman itama kamar dayan sashin dakuna biyu ne sai wani qarami da alamun local kitchen ne wanda koda zaka buqaci wani abu da dare basai ka sauka ba, daya cikin dakunan suka bude suka shigar da ita sosai Hajiya Kulsum aminiyar Mom ta qara yimata nasiha akan biyayya ga mijinta itadai Babu abinda da takeyi sai kuka da rawar sanyi zazzabi ne yake neman rufeta Ya'isha ta matso jikinta ta sunkuya tace “ke banza ce wlh Ni banga abin kuka ba to kukan mafita ya zame miki kome?" Dagowa tayi ta sauke idanunta sa suka jima da komawa jajaye saboda kuka tace “shi....shikenan da gaske na rasa Baffa'am dina Ya'isha Kuma akeso nayi rayuwar farin ciki....." Muryarta ne ya kama rawa Ya'isha tace “mun shigai Aunty Hamida ku Kira mijinta zata tayar mana da aljanu" yanda jikinta ke tsuma ne yasa Hamida yarda ta Kira wayar Rasheed ya daga muryarsa can qasa shima rawar tasa muryar takeyi yace “ya aunty Hamida ya akayi?" Cikin zaquwa tace “Meenah ke neman rikice Mana mun kasa gane kanta don Allah kazo idan kana kusa" kashe wayar yayi dake dama Yana gdan duk motsinsu yanaji ya dauki doguwar riga ya saka ya bude qofar ya fito idanunsa kamar garwashi saboda ja dake duk yafisu Rasheed haske shi fari ne sosai daka kalleshi zaka gane kukan shima yakeyi. Kuka Fadila ta saka da ganin yanda yayan nata ya zama wani kalar tausayi tace “tunda yarinyar nan ta shigo zuri'armu muka daina cikakken farin ciki Ya Kareem kaima duk ta susutaka yanzu kukannan don ita kakeyinsa....." Hanya ya saita mata cikin zafin zuciya yace “kowa yaje na gde" binsa sukayi da kallo ya dubi Hajiya Kulsum yace “Mama wlh idan akaci gaba da hayaniya a gdannan tsaf zan haukace brain dina tana neman daina aiki" sumsum suka rinqa ficewa daga gdan saida suka fice gabadaya ya tsaya yana jin tashin motocinsu gabansa faduwa yake daqyar ya tura qofar da sallama ya shiga dakin ya tsaya tsakiyarsa Yana qarenta kallo tana zaune ta dora kanta jikin gado sai tsumar jiki takeyi a sanyaye ya isa gareta ya tsugunna gabanta yakai hannunsa zai dago kanta gabansa ya fadi ya janye ya sake saita idanunsa akanta yace “meye yake damunki?" Kamar me jiran yayi mgn ta dago kumburarrun idanunta suka shiga cikin nasa ya kawar da kansa ya dake zuciyarsa yakai hannunsa jikinta yajishi zafi zau yaja numfashi ya miqe ya dauki wayarsa Yana zagaya dakin can yace “Inada petiant a gdana kazo da wuri don Allah" da haka ya kashe wayar yaci gaba da zagaya dakin can yaji ana qwanqwasa qofar ya sauka ya bude suka shigo tare Dr Razaq ya fara tambayarta yanayin da takeji tayi masa shiru shikam Kareem ido ya kafeta dashi can da tambayar ta isheta tace “Kaje Dr Razaq bakada maganin matsalata Allah ne kawai zaimin magani" wata iska Kareem ya furzar ya juya ya fice Dr Razaq ya biyosa yaganshi tsaye ya hade kai da garu ya dafashi yace “ka daina Sanya wannan damuwar a ranka Ranka shi dade kanada heart problem idan komai zaike damunka to rayuwarka tana cikin kwale²" Juyowa yayi ya dubi Dr Razaq yace “kana nufin Meenah zata soni nima?" Dariya tambayar tabawa Razaq yace “kama qaddara a ranka tasoka fiye da kowa ta gama karfa ka manta kaine ta fara so a rayuwarta ko ka manta Karin mgnr hausawa da suke cewa so baya tsufa saidai masoyan su tsufa bature kuma yace true love never end" wani murmushi yayi yace “na gde Dr Razaq zan jira lkcn da zan gasqata hakan"............. Juhud is not free read... regular 300 VIP 600 via👉🏼 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank Then you show ur evidence via WhatsApp 09013718241... Juhud ba littafin kyauta bane kada ki biya 300 regular VIP 600 kafin ki karanta ta wannan account din 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank ko katin MTN pls ban buqatar vtu hoton katin ko digit number ta WhatsApp number 09013718241..... *Oum Hairan* [8/8, 9:07 PM] Oum Hairan: *0032* Sallama sukayi ya rakashi ya hau motarsa tare da karbar magunguna bai koma gdan ba shima ya shiga tasa motar Yana duba agogo 8:30pm ya jinjina kai ya fice a gdan kai tsaye wani restaurant ya nufa yayi musu siyayyar abinda zasuci ya juya ya koma gdan ya kulle ko Ina ya nufi saman Saida ya shiga dakinsa yayi wanka ya sanya kayan baccinsa ya fito ya bude nata dakin tana zaune inda ya barta har yanzu kukan takeyi gabadaya lamarinta ya tsinka masa lakar jiki da gaske take jin damuwar a cikin ruhinta. Aje ledar dake hannunsa yayi ya tsugunna a gabanta ya kamo hannunta ta fuzge ya zauna sosai a gabanta ya dafe kuncinsa da hannayensa biyu ya zuba mata manyan idanunsa da a baya suke firgitata da sanyata shiga taitayinta baiji a ransa ko yace ta tashi suyi nafila zatayi ba shiyasa ya janyo ledar yace “Ya'isha tace tun shekaran jiya bakici abinci ba ko meye dalili?" Shiru tayi masa yaja fasali ya furzar da iska ya bude ledar ya fara yaga mata Naman yanda zataji dadin ci ya dauko yakai mata bakinta ta kawar dakai yayi murmushi yace. “Lamarinki abun mamaki ne Meenah sai naga kamar kina jayayya da hukuncin ubangiji ne ya kamata ace rayuwarki kadai ta ishenki darasin da duk wani abu da Allah yayi zaki tarbeshi hannu biyu wlh duk da nakasance me qulafuci da addu'ar idan kedin Alkhairi ce gareni ki zama gatana ki zama mallakina bantaba furtawa wani burina a kanki ba na fawwalawa ubangiji na yarda duk abinda yayi daidai ne so Kuma sama taka cikin lkcn da ban tsammata ba kiran Mai Martaba ya shigomin yana fadamin na tanadi sadaki a hannuna daga dubu hamsin zuwa abinda Allah ya horemin nazo masallacin Fada yana nemana bansan meye zai faru ba hakanan na tafi Ina zuwa naga dogare sun budamin na shiga kamar yanda baa nemi izininki ba nima baa nemi nawa ba wlh kudin aljihuna kawai Mai Martaba ya karba dubu tamanin yabada umarnin a daura nidai na nemi guri na zauna Ina jiran naji auren waye zaa daura kawai naji ance yace shi a matsayin waliyinki ya bada aurenki gareni akan sadaki naira dubu tamanin bisa sharadin zanyi miki lefe kamar yanda al'ada ta tsara" Shiru yayi yana mayar da numfashi sannan yaci gaba da cewa to meye laifina cikin lamarin nan Meenah?" A qufule ta dago tace “meyesa bakace bakaso ba?" Murmushi yayi yace “ko bake bace
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82