Chapter 42
Chapter 42
a WhatsApp wato wannan._ 👇🏼 _09013718241_ _Indai kika tura kudi a akasinta to ke kikaso su damfareki sannan littafin Juhud ba 100 bane 300 ne VIP 600 idan kinada ra'ayin biya ki tura ta wannan account din 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank ko katin waya MTN ta number dake sama vtu Kuma ta wannan 09031307566 saiki tura screenshot na biyanki a wannan number_ _09013718241_ _Na gde_ _Taku_ *_Oum Hairan_* [7/31, 8:47 PM] Oum Hairan: *JH0023* Dafe kansa yayi a fili yace “oh God ciwon kai Meenah naji tashi muje kiji fah ni bama abinda kike tunani bane" daqyar ya samu ya lallabata suka shiga ciki ta qofar baya suka shiga quarters din Yana riqe da hannunta suka shiga ciki ya rufe qofar ya saki hannunta ta fada kujera ta kwanta yayi murmushi yace “Meenah kishinki yayi yawa bansan meye kike kishin ba kullum cikin tuhumata kike meye yasa kike zargina ne?" Lumshe idonta tayi taba banza ajiyarsa yasan tunda tayi haka bazai samu arziqin mgn ba dole ya haye sama ya cire kayansa ya watsa ruwa ya dawo ya dauketa cak suka haura saman har yanzu a sama take dashi bata bashi fuska ba Ganin hakan yasashi shima ya qyaleta da asuba kuwa Yana shafawa yaji Babu ita ya bude idonsa yaganta saman sallaya ya miqe yayi miqa yayo alwala yazo ya tada sallah. Kitchen ta shiga ta dora tea yanzun bata jure yunwa jikinta har rawa yakeyi ta dafa Indomie ta fito. Jerawa tayi a dinning ta zauna tanacin Indomien ya sauko sanye da doguwar riga bata dagoba balle yasaran zata kallesa yaji babu dadi sosai hakanan ya zauna ya zubanta ido sun hada ido yakai sau biyar sannan tace masa morning" zuciya yaja yace “kin tashi lfy" bata bashi Amsa ba ta hada tea dinta ta fara Sha ta miqe zatabar gurin ya riqota ta juyo ta zuba masa manyan idanunta baisan sanda ya saketa ba tabar gurin. Duk jikinsa yayi sanyi baison ganinta cikin damuwa miqewa yayi yabi bayanta tana tsaye a tsakiyar dakin sai kaiwa da kawowa takeyi ya jingina jikin qofar ya kira sunanta ta tsaya Amma bata juyo ba takowa yayi ya tsaya a bayanta suna kallon juna ta madubi ya shafa gemunsa ya nemi guri ya zauna yace “bawai fushinki ne yake damuna ba not akan abinda kike fushin shine yake damuna nifa ba abin da kike tunani ne yasa....." Dagansa hannu tayi tace “na tsani qarya a rayuwata wlh bazan iya hanaka ba domin bani na dora maka ba kaine ka dorawa kanka kawai abinda nakeso ka fitarni a lissafinka ka qyaleni nayi rayuwata kayi taka. Da sauri ya dubeta kamar zaiyi mgn sai Kuma ya miqe yace “ok" daga haka wata kalma bata kuma shiga tsakaninsu ba har ya gama shirinsa ta hada masa kayansa ya dauki jakarsa yace “zan tafi" batare da wani basa muhimmaci ba tace “Allah ya tsare ya taimaka" kudi ya zaro ya aje mata ya juya Yana tafe Yana cewa banida isassun kudi a hannuna ki riqe wadannan ba dadewa zanyi ba kafin bikin su Ya'isha zan dawo" Yana fadin haka ya fice da sauri saboda karyar masa da zuciya take neman yi itama jikinta yayi sanyi sosai tabisa da kallo tana hangensa har ya fice daga quarters din ta zauna tana saqawa da warwarewa can dai taga bazai kaita ba ta shiga daki ta kwanta. Kasancewar ita kadai ce bata tashi a bacci ba sai yamma tayi wanka ta tafasa taliyarta da bushasshen kifi taci ta kora da lemo ta miqe ta lalubo wayarta zaro ido tayi 7 missed nasa tana Shirin kiransa ya sake Kira ta Kara a kunnenta yace “kina bacci ko?" Murmushi tayi tace “eh na tashi naga missed naka Ina fatan ka sauka lfy" Amsa mata yayi sukayi shiru na dogon lkc can yace “fushinki gareni Yana azabtar dani Meenah kiyi hqr don Allah" a kasalance tace “yafa wucce Baffa'am kawai dai Raina baya dadi ne idan na tuna kana raba Mana Abu mafi daraja da wasu wadanda basu cancanta ba. Yaji dadi sosai sukaci gaba da hirarsu har zuwa wani lkc sannan sukayi sallama cike da kewar juna tana kashe wayar wayar Amrah ta shigo ta daga shigo ta dauka daga yanayin yanda suke gaisawar tasan da wani saqo a zuciyarta Amma ta maze taja numfashi tace “burinki ya cika hankalinki ya kwanta kin yaudareshi kin Sanya masa ciwon zuciya kawai saboda wani quduri naki Meenah Ya Kareem bai cancanci wannan sakayyar daga gareki ba yasoki lkcn da bakisan komai ba shine yanzu dan kin zama komai kika gujeshi......" Dakatar da ita tayi da cewa “kina mgn da yaen da bana ganewa Amrah meye ma laifina ne cikin zarginki nima kamar yanda kowa yaji sama taka hakanan naji bansan wani abu bayan abinda kuka sani ba nidai na wayi gari naganni matsayin matar Baffa'am dina Kuma na yarda da abinda Allah ya tsara na karbeshi to meyece tawa a ciki?" Wata dariya Amrah tayi tace “bawai inayi miki mgn don kaina bane domin ni da eh dinki da aarki babu abinda zata qaramin Amma dai ki sani baki auri mijin daya dace dake ba domin kuwa ya rainanki hankali ne kawai saboda sha'awa ya aureki Kuma bazai taba canza hali saboda ke ba ke mufa a qarshe ma godiya mukayiwa Allah da Allah baisa mun dauko Kara da kiyashi ba maita ai bala'i ce a qarshe dai Ina Mai farin cikin sanar dake Ya Kareem zaiyi aure zai auri wacce tafiki asali nasaba da nagarta kinsan dama rayuwar duniya qwarya tabi qwarya akeyi" Dukkannin kalaman Amrah babu Wanda ya daki zuciyar Juhud kamar Wanda tace Allah ne ya taimakesu Basu dauki Kara da kiyashi ba maita ai bala'i ce....." Kashe wayar tayi cikin dimuwa tayi tagumi itadai tana ganin jarabawa Wai ya akayi ta zama mayya ne? Tana tsaka da tunanin nan Kiran Mom ya shigo ta daga a sanyaye cikin rawar murya tace “Mom.... Momy Ina yini" zuciya Mom taja tace “me Amrah tace miki?" Saita muryarta tayi cikin kuka tace “babu komai Mom" shiru Mom tayi sannan ta kashe wayarta ta miqe ta shige daki ta fada gado ta rushe da kuka yau ce Rana ta farko data fara jin shauqi da tunanin Ina zata Sami wani dazai zame mata abokin shawara dazai bata mafita cikin matsalarta maita? Maita? Ta maimata yakai sau goma sannan ta iya miqewa ta shiga bathroom tayi wanka tayi magrib ta dauki qur'ani tana karantawa har akayi Isha tayi ta haye gado zazzabin dare ya aurenta ga kadaici hakanan tayita juyi da missing din Baffa'am dinta bacci ya fara daukarta taji wayarsa ta dauko ta gyara kwanciyarta ta Kara wayar a kunnenta tace “tsarki ya tabbata ga ubangijin daya halicci zuciya biyu makusantan juna" numfashi ya sauke yace “Same to ur my Meenah meye ya hanaki bacci 11:40pm" kasa tayi da muryanta tace “kewa da tunanin mijina gami da missing lallausar fatarsa" dariya abin yabashi yace. “Au haba dama kina jina a zuciyarki haka" Murmushi tayi ta shafa saman kanta tace “komai na duniya hawa yake Yana sauka nikam sonka baitaba sauka a zuciyata ba Baffa'am tunda ya riga ya hauhawa don Allah ka riqemin amanar kanka kaji" qaramar ajiyar zuciya yayi yace
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82