Skip to content

Chapter 83

Chapter 83

Abban Sojoji Book One Complete Hausa Novel 1,197 words 0 views Progress saved
Download Book

saude kuwa aza hannu tayi akai tana faɗin"goggo dan Allah kidaina !! Kidaina zaginsu mana akan abunda basu sani baaa...... tunkan ta ida goggon tasa hannu ta buge mata baki, dafe baki sauden tayi don taji zafin bugun, Ci gaba da magana goggon tayi a birkice tana kuka, " Ae dama nasani ba wanda zai goyi bayana akan magana ta, amma ni nasani wlh ku ƴa'ƴan ZAINABU ne, dama haka uwarku take kamar ku ɗinnan, shegen taurin kai da kafiyar tsiya, kunnan ta kamar na zomo, fitinanniyar yarinya ƙiri-ƙiri ta guji jini na, dama sai da nace mata cikin jikinta na Abusufyan ne amma taƙi yarda ae dama nace mata jiki magayi amma taƙii ji, kunnan ƙashi ko ae ynx nasan taji jiki bawan Allah bai mata komai ba amma taƙisa, wlh cikinsa ne ku ƴa'ƴansa ne amma kunƙaryata ni, ga falo falon kunnuwanku nan irin na abusufyan shima dayake baijin maganata kangararre ne yaƙi jin magana ae gashi nan...... Zuba kawae goggon katsina takeyi ba ƙaƙƙautawa kai kace radiyon da bata da saiti, notikan kanta sun kwance sai faman zazzaga musu bala'e take yi, tana yi musu magana akan mutanen da basu san da zamansu ba, tashi su kayi atare su ka tsaya suna kallonta haƙika sun tsorata da tsohuwar tuni idonsu ya cicciko da kwalla, Goggon katsina bata dakata da surutun ba har sai da Saude tace "goggon kiyi hakuri dan Allah, nima na yarda cewa su ƴa'ƴan Uncle sufyan ne, sai yanzu na ƙara lura da kamannin nasu dagaske ne abunda kika faɗa, saude na gama faɗan maganar ta kalli su hosana tayi musu alamar su amince suma da maganarta don asamu ta lafa, Cikin sauri suka zube saman guiwowinsu agabanta tare da cewa "Dan Allah kiyi haƙuri goggonmu, munyi miki laifi, tabbas mu jininki ne mu ƴa'ƴan abusufyan ɗinki ne, ki yafe mana munsa kin zubda hawayenki," Sanyi goggo taji aranta dama ita burinta kawai su amince cewa su ya'yansa ne, hannu tasa tana share hawayenta, bayan ta kammala ta miƙa hannayenta tare da ruko nasu ta tsayar dasu tsaye fuskarta da murmushi sai kace ba wadda tagama sharbar kuka tace " Alhamdulillah har hankali na ya kwanta ynx, amma fa kun wahalar da gaggonku sosae kun sani ina ta faman zubda hawaye na, da ace abusufyan na nan kuma yasan abunda ku kayi ma goggonsa tabbas sai ya muku dukan tsiya" , Sunnar da kai su kayi tare da cewa "ayi mana afuwa goggonmu, bazamu ƙara ba insha Allah," Murmushi tasaki tare da cewa " ku koma kuzauna ƴa'ƴana, yanzun nan zan kira mahaifinku a waya ku gaisa," 🙆‍♀️🙆‍♀️🙆‍♀️ BossLady❤️ Inaso naji ta bakin ku game da annoucement ɗina nasan kowa ya karanta, sannan comment akan page ɗin yau 👏👏👏 *💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋* ﻗﺼﺔ ﺣﺐ ﺭﻭﻣﺎﻧﺴﻴﺔ ﺑﻴﻦ ﺳﺤﺮﻳﺶ ﻭ ﺍﻟﺠﺮﺍﺡ ﺍﻟﻌﺎﻡ ﺭﺍﻓﻴﺖ🌹❤️ *Mallakin* *🌹Hafsat Bature Moh'd*🌹 ~BossLady~💋 Page 81-82 part 2 *Meaning of name sehrish is an arabic name, ma'anar sa kuma Glamorous Personality* 🌹 Har haɗa baki suke yi wurin cewa "mahifinmu kuma ! A waya !?. Da ƴar dariya a fuskarta tace"Eh mana, ae kullum sai ya kira ni mungaisa,' tayi maganar ayayin da ta kama hanyar zuwa bedroom ɗinta don ta ɗauko wayarta, Hannu suka aza akai alamar sun shiga uku, ita kanta saude tama rasa me zatayi abun ya ɗaure mata kai, lamarin goggo sai addu'a tsufanta da rigima yazo mata, "Kada ku damu kunji kawai, ku kwantar da hankalin ku, in ta kawo muku wayar ku amsa ku gaisa dashi amatsayin mahaifinku, Uncle sufyan ya riga da yasan rigimar Goggonmu wayayye ne shi zai fahimce ku," Saude ce tayi musu wannan bayanin, jiki amace suka amsa mata da cewa "Toh," Sannan ta juya ta koma kitchen saboda tabar girki saman gas, Zuru su kayi suna jiran zuwan gaggon katsina da waya, babban tashin hankalinsu yarda zasuyi waya da mutumin da goggo ta ƙaƙaba musu a matsayin mahaifinsu wanda basu ta6a gani ba kuma basu san kowanene shi ba," suna nan zaune zuciyarsu nata bugawa sai ga goggo ta fito daga ɗakinta, hannunta riƙe da waya sai faman zabga murmushi take yi, Koda su ka ganta gabansu ne ya faɗi rass don su a tsorace suke, Miƙa musu wayar tayi tare da cewa "Maza ga mahaifinku nan akan layi kuyi masa magana," Kamar bazasu kar6a ba haka su kayi daker Jahad tasa hannu ta karbi wayar goggon tare da karawa a kunnanta tace ,"Assalamu alaikum," daga can 6angaren taji wata natsattsiyar murya ta amsa mata da cewa "Wa'alaikum salam," sai da jahad tayi jimmmm kafin ta daure ta cije tace "Abba Jahad ce ɗiyarka, ina fata kana cikin koshin lpy," Abusufyan ya amsa mata da cewa "lpy lou Alhamdulillah My daughter, kin yi missing ɗin abbanki kuwa,"? Yanda yayi maganar ba ƙaramin kashe ma jahad jiki yayi ba, sai kawai taji hawaye na ƙokarin zubo mata, Murya na rawa tace "Nayi missing ɗinka sosae abbana, ina kewarka," tayi maganar ayayin da take dab da fashe wa da kuka, cikin sauri tace "Abbana ga hosana ku gaisa, itama tayi kewarka sosae," "Okey bata wayar," ya umarce ta, Miƙawa hosana wayar tayi jikinta na kerma, hannu hosana tasanya ta karbi wayar tare da karawa a kunnata, duk goggo na tsaye tana kallonsu sai faman murmushi take yi, (ta haɗa Bomb) Tashi jahad tayi cikin sauri ta wuce bedroom ɗin saude tana shesshekar kuka tana idasa shiga ɗakin ta faɗa saman gado tare da fashe wa da matsanancin kuka, bakomai bane ya karya mata zuciya ba face tunda suke arayuwa basu ta6a sanin daɗin soyayyar mahaifi ba ga Uban amma bai da amfani," A can kuwa tun da hosana tasanya wayar a kunnanta tace "Abbana dagaske kaine mahaifin mu kamar yadda goggo ta faɗa," On the other hand abusufyan yace "My daughter are u doubting abt ur father? nasan kinyi kewata ne shiyasanya kike kokwanto akaina," aikuwa jin ya tabbatar mata da cewa shi mahaifinsu ne yasanya ta fashe masa da kuka tare da cewa "dama nasani kaine mahaifinmu, ba wancen mugun ba, sai da nace ma Oumma mu bamu kama dashi mummunane shi mai baƙar zuciya amma taƙi yarda, ni nasani ba abban mu bane, babu uban da zaiyi wa ƴa'ƴansa haka, kaine mahaifinmu,......" Katseta yayi tare da cewa "Silent pls, sorry my daughter bana fahimtar zancen ki i was busy now, zan kira anjima,' yana gama faɗan hakan ya kashe wayar saboda baisan inda zancen nata ya dosa ba, shi dai kawae ya amsa kira ne kamar yadda goggonsu ta sanar dashi cewa ƴa,ƴanshi sun zo, sarai yasan rigimarta shiyasa yabisu a hakan, Ganin ya katse kiran yasa hosana fashewa da kuka, wurgi tayi da wayar goggon saman kujerar sannan itama ta miƙe tana ci gaba kuka ta wuce ɗakin saude, Jikin goggo yayi sanyi, ita a tunaninta abusufyan bai kula da yaransa shiyasa suke kuka, don haka taci alwashin zata sashi dole saiya zo nigeria ya ɗauki ƴa'ƴansa ya koma dasu can qasar da yake zaune, a ranta tana cewa "in banda shiririta irin ta abusufyan ka kama hanya ka tafi ƙasar Turƙiya kabar yara cikin damuwa, gashi nan sai faman kuka suke yi, Allah ni da kai ne, saina sanar wa AMMI halin da ake ciki, Ta idasa maganar tata tare

Table of Contents

Chapters

113 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113