Chapter 6
Chapter 6
nufi hanyar kitchen din tana cewa "Allah ya wadaran naka ya lalace har waning nayi muku kada ku taba komai amma saboda kan kifi gare ku baku gane komai salon kujama mutane ko !? Hajajju tace "ke ma da laifinki akan me zaki baro min su a kitchen salon suyi mun barna ," mayar da idon ta tayi kan Sehrish "ki je ki huta time din sallah ma yayi nima bari na tashi ," Ta shi tayi ta shiga ciki , wanka tayi ta dauro alwala , ta fito ta shimfida prayer mat tayi sallah , kamar yarda ta sama kullum sai ta daga hannayenta tayi sama da 30mins tana rokon Allah cikin harshen larabci take jero addu'oin ta da bukatanta da damuwarta tana neman Allah ya yaye mata su , Bayan tagama ta tube hijabin ta ajiye , sannan ta hau saman bed ta kwanta dama jiya bata samu isasshen bacci ba , don haka lokaci guda bacci ya kwashe ta , tana cikin bacci y'an matan nan suka shigo , sai faman fadin wash Allah suke , koda sukayi arba da ita kwance ta baje gashi ta cire hijabin kan ba head tie, nan fa suka fara santin gashin kanta , ita dae bata son meke wakana ba tadai ji sama sama ana ja mata gashin kai , Zama sukayi kamar sun sami television sukai ta kallonta , ba karamin lalata sukayi ma kanta ba duk sun cukuikuye mata gashi yar kalaban nan sun warware mata ita , sun mai da karamar mahaukaciya , Nauyin bacci ne ya hana ta farka amma tabbas taji ana shafa mata kai kasa kasa , Sai da ana kiran sallan isha sannan ta farka , mika tayi tare da yin hamma , time din sun fita daga cikin bedroom zuciya sauko da legs dinta tayi kasan tiles din tana sauke ajiyar zuciya , kafin ta mike ta shiga toilet , tana cikin yin alwala tayi shafuwan kai ta shafo gashin kan ta mamaki ne ya kamata jin ba kitson dake kanta da sauri ta idasa alwalar ta je gaban mirror ita kanta sai da ta firgita da ganin yadda suka susuce mata gashinta , amma ba wannan bace damuwarta , zullumin kada husanna ta mutu da kuma aikin da zata fara , Zama taci gaba da yi a bedroom din , tana tunene tunane , ga yunwa tana ji amma takasa fita ta nema , Turo kofan sukayi suka shigo hannunsu dauke da tray abincin aka zuba musu shinkafa da miya ne sun cinye sun rage mata d'an kadan, ajiye mata sukayi suna dariya suka fice , abunda basu sani ba ita kallon Shashashu take masu , Bin a bincin tayi da kallon ba don tana jin yunwa ba da bazata ci Ba don sun jagula shi, haka ta zauna ta dinga turawa a baki kamar zatayi kuka , har dare yayi tana zullum abu daya kuma dashi ta kwana, .......................................ABBAN SOJOJI .......................Story by MrsBature ..................Part 1 In the morning Around 10:30am makeup artist dinan ta iso gidan a time din duk sun hallara a falon hajjaju , bayan sun gama gaisawa , ma'reea ta bukaci ganin Sehrish , kwala mata kira hajajju tayi fitow tayi da sauri ta iso inda suke , bin ta da kallo mareeya tayi frm head to toe , sannan tace "Wannan ae mai sauki ne , naga tana da tsayi jiki ne dai babu sosai , abunda za'ae kayan maza za'a samo riga da wando oversize saboda su kara mata girma , sannan wadannan abubuwan , tayi magana tana nuna kirjinta da hannunta " dole a matse su don naga suna da girma ssae tubarkalla , " cikin jin kunya rishi ta dukar da kanta kasa , murmushi larai da hajajju sukayi , su kuwa y'an matan nan dake baje a kasan carpet dama basu da burki washe baki suka shiga yi wato anzo dai dai inda suke so , Hajajju tace "ynx me za'a sa a yi tighting dinsu "? Ma'reeya tace "mai sauki ne akwai wani abu da muke amfani dashi na matse tumbi shima zai iya yi ," hankalin rishi ba karamin tashi yayi ba har bata son lokacin da tayi subul da baka ba tace "in suka bace fa ya zanyi ,"? gaba dayansu suka kwashe da dariya mareeya tace "wato kada su bace a rasa nayiwa miji gayu ko ," cikin jin kunya ta dukar da kai , larai tace " dagaskiyar ta fa nono ae yana daya dagacin abunda ke kayatarda maza in suka bace ae ba magana ," ta karasa magana tana dariya , duk kunya ta gama kamata, Ma'reeya ta ci gaba da magana "Sannan naga kamar tana da tsayin gashi ko,"? hajajju tace "Sehrish cire hijabin mana tagani , hannu tasa ta cire hijabin ta rungume a kirjinta , Hada baki sukayi wurin cewa "Tubarkalla masha Allah ," ma'reeya tace " yarinyar kamar balarabiya wurin tsawan gashi, gsky ni kishi nake da wannan gashin naki don haka dama dole indai zakiyi acting a matsayin namiji sai an datse miki shi ya koma guntu kamar nawa dai", nan fa hankalin ta ya tashi saboda tana bala'en son gashin nan nata , kamar zatayi kuka tace "don Allah hajajju karki bari ayimun aski ni inason gashi na ," takarasa maganar tana kallon hajjaju , Murmushi hajajju tayi tace " Sehrish ba Aski zata miki ba rage miki shi za'ae , ke da zaki neman kudi wake ta wani gashi , " Shiru tayi tana wasa da yatsun hannunta , larai tace "Gsky yarinyar nan da ace a matsayin mace zata je aikin nan tsaf zata auren mai gidan," hannu hajiya tasa abaki tace "ke ! tab y'ay'an sa kuwa da sun yi farfesu da namanta sojoji fa akace hmmm !! " dariya sukayi su duka , mareeya ta cigaba da bada bayani "Sannan dole a canza mata suna daga SEHRISH zuwa TUKUR ," a tare suka hada baki wirin cewa "Tukur kuma !"? murmushi ma'reeya tayi tare da jaddada masu maganarta ta " kawai kuwa ! sannan zan sa mata gashin baki irin na maza wanda ake fixing dinsa tare da eyebrows na kanti. *_Hafsat Bature_* ~(Boss Lady)~ Page 7-8 Hajajju ta ce "Gashin baki dai. wannan dana nasani ? amma me amfanin hakan "? ma'reeya tace "Wannan wani salo ne kuma ina tabbatar miki da zaiyi aiki , duk da sehrish yarinya ce har a fuskarta amma indai nasa mata gashin baki dana jagira , zata kara suffanta da namiji zata koma kamar d'an daudu kuma dama in kin lura yanayin jikin y'an daudu basa da kiba sai tsayi ," Gaba daya sun amince da maganar ma'reeya , shiri na musamman akayi ma Sehrish a washe garin ranar cikin riga ta maza milk colour mai maballai a gaban rigar , sai wani burgujejan wando falazu da aka sama ta kamar kafar agwagwa haka yake pink colour , sun matse mata kirjinta , shafe ta koma kamar babu su , an datse dogon gashin kanta an barmata guntu irin nawa sai suka samu kallabi irin launin trouser din suka nannade mata shi akai kamar rawani , kallabin nada tsayi sai da yar jela ta zubo ta gefe , sai
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113