Skip to content

Chapter 82

Chapter 82

Abban Sojoji Book One Complete Hausa Novel 1,193 words 0 views Progress saved
Download Book

time ɗin na tashi daga bacci, muka haɗa ido dake zaki fice, kawai sai kika fashe mun da dariya ko ba haka akayi ba,'? Ya ƙare maganar tasa da tambaya, Hannu sehrish tasanya a bakinta, tana ta faman tiƙar dariya shima kansa dariyar yake yi, Bayan sun tsagaita da dariyar tasu junaid yace "bayan nan akwai time ɗin da kina saving ɗinmu abincin dinner, phone ɗina yayi ringing, nayi picking call ɗin kwatsam sai ki kaji muryar Sister ɗinki, wanda hakan yasanya arazane ki ka saki cup ɗin dake hannunki har ki ka 6arawa Ayaan ruwan coffee mai zafi, Anyi hakan? Ya sake jefa mata tambayar yana yi mata kallon MAGE TA KAMA 6ERA, Cikin jin kunya sehrish tace "Am so sorry pls," "why are u saying sorry to me sehrish? Ni baki mun laifin komai ba, abun ma sai ya zamar mun kamar drama, naji daɗin hakan," ya faɗi yana ci gaba da kallonta, After some minutes duk sunyi shiru sai da arinƙa jefa wa juna murmushi ana satar kallon juna, rishi jin abun take tamkar a mafarki wai yau itace tare da ɗaya daga cikin ƴa'ƴan abban sojoji mai sauƙin kai haka, addu'arta shine Allah yasa sauran ma su kasance masu sauƙin kai a duk lokacin da Allah zai sa su gane cewa ita maca ce," Jin tayi masa shiru yasanya shi sake cewa "a matsayin me zaki ɗauke ni yanzu Aboki ko ɗan uwa"? Sehrish tace "Da so samune duka biyun, I need both,' Wani irin daɗi ne ya rufe junaid kamar kamar me, ji yake kamar ya rungume sehrish ajikinsa, farin cikinsa sam yagaza 6oyuwa, Sun sha fira har wurin sallar magrib sannan suka tsagaita, sehrish ta maida gashin bakinta da hularta duka yadda suke sannan suka kama hanya atare suna ƙara tattaunawa kamar karsu rabu da juna, sai da rishi ta fara shiga ciki da jimawa, sannan junaid ya shiga saboda kar a gansu atare, (Guys nima fa sun burgeni wlh, haɗuwarnan ta rishi da junaid ta tafi dani)💋 ________________________________ *Dama nace akwai annoucement to gashi, Littafin nan littafi ne mai yawan gaske Kuma idan nace zan datse shi to tabbas zan lalata littafin daɗinshi zai ragu sosae bama zai yi tsari ba don haka Part 3 of this Novel will be paid Book, abubuwa da dama waɗanda basai na faɗa ba Ina fata zaku goyi bayana, Nasan duk ranar dana ce na dakata da rubutun littafin nan babu wanda zaiji daɗi acikin readers ɗinshi don haka muyiwa juna Adalci, Sorry 4 the late annoucement* 😔🙏 Ci gaba _________________________ Zuba musu ido goggon katsina tayi tana kallonsu ko kyaftawa babu, kamar wadda tayi gamo da aljanu, Zaune suke suna facing ɗinta sun matse juna cike da tsoran abunda tsohuwar zata ce musu, Ta jima da farka wa daga bacci amma batasan dasu acikin gidan ba, saboda suna can cikin ɗakin saude suna bacci, ita kuma sauden bata sanar da ita cewa Omar ya sa an kawo wasu ƴara ba sai yanzu bayan sallar magrib ta ke sanar da ita, shine tasa ta kira mata yaran tagansu," "Jahad me yasa take kallon mu? bata son mu ko? Korar mu zatayi ko"? Hosana ce tayi ƙasa ƙasa da murya tana raɗawa Jahad a kunne, Jahad tace "nima bansani ba, amma ina tsoran kartace bata son mu, in ta kore mu, ina zamu sa rayuwarmu? Cikin raɗa suke maganar tasu, duk sai da suka gama raɗe-raɗen sannan su kaji goggon katsina ta fashe da dariya tare da cewa "kun ta6a jin inda uwa ta guji ƴa'ƴanta !? Ku fa jinina ne, ƴa'ƴan abusufyan ae ƴa'ƴana ne halak malak," Kallon juna su kayi jin abunda tsohuwartace, atare suka hada baki tare da cewa "ABUSUFYAN kuma wanene shi ? mu bamu son shi ba,' ɗaure fuska goggon katsina tayi tare da cewa "Bansan shashanci in ma zolayata ku keyi to ku daina, ni ba amun irin wannan wasan yanzu na burkice, ku faɗamin gaskiya ku ba ƴa'ƴan abusufyan bane,? Babu wasa a fuskarta tayi tambayar, hankali atashe suka ce "wlh bamu son shi ba, bamu son wa kike magana akai ba, mu yau muka zo gidan nan," Sassauta murya goggon katsina tayi tare da cewa"kuna nufin ku ba ƴa'ƴan abusufyan bane ? Ni zaku raina wa hankali ko? Kubar ganin nafara tsufa da hankali na wlh Wannan furfurar da kuke gani akaina, bata tsufa bace ta arziƙi ce," 😡 ta yi maganar tana hararansu, cikin tsananin tashin hankali jahad tace "wlh goggo gaskiya muke faɗa miki, bamu son shi ba, mu ba ƴa'ƴansa bane," Jin yadda jahad ta karyatata yasa ta fashe wa da matsanancin kuka, zaro ido su kayi ganin tsohuwar na sharar kwalla, kuka fa sosai hada jan majina tana faɗin "saboda na fara tsufa kke gudu na ko? ban ta6a tunanin ƴa'ƴan abusufyan zasu guje ni ba, wlh sai na kirasa a waya nasanar masa tashin kunyar da kukayi wa goggonsa wlh baxai ƙyale ku ba...' tayi maganar tana shesshekar kuka abun kamar a mafarki su hosana da jahad suke kallon lamarin, Jin kukan goggo yasa saude fitowa daga kitchen hankali a tashe karaso wa tayi tana faɗin "Subhanallahi goggonmu me nake gani haka kamar kuka a idonki,' Ƙara fashe wa da kuka gaggon katsina tayi tare da cewa " saudatu dan Allah waɗannan ba ƴa'ƴan abusufyan bane? tayi maganar tana nuna su Hosana da hannunta, Sakin baki Saude tayi galala cikin mamakin rigimar goggon katsina, girgixa kai tayi tare da cewa " wlh narasa meke damunki goggo ! Sarai fa kinsan cewa Uncle abusufyan bai ta6a aure ba ko? wai yaushe ma yayi budurwar ballantana ma aure har akai ga ƴa'ƴa, anya goggo kina shan maganinki akai akai'? Miƙewa tsaye goggon tayi idonta cike taf da kwalla fuskarta a damuje tasa idonta cikin na saude tace" saudatu hada ke za'a ƙaryatani ko? ke ma kallon zararriya kike mun ko? saudatu da hankali na wlh, waɗannan yaran ƴa'ƴan abunsufyan ne, Jini na ne ina ji ajiki na, dan Allah kudaina mun yawo da hankali wlh zuciyata zata iya bugawa in mutu a wurinnan," Goggo tayi maganar cikin ƙunar rai da jin ɗaci aranta saboda ita harga Allah ta tabbatarwa kanta cewa tagwayen nan ƴa'ƴan abusufyan ne, mutun da bai ta6a aure ba, hasalima ma ba a nigeria yake zaune ba gaba ɗaya, Shiru saude tayi tana kallon goggo dake ta faman kuka kamar ƙaramar yarinya aranta tace "tabbas goggo fa hauka ya tashi gadan gadan, don haka a kunnan babban likita dole nasanar mishi a bincika kwakwalwarta in ba haka ba kawai daga ganin yara sai kice wai ƴa'ƴan Uncle sufyan ne, yau yau ɗinnan fa yaran nan suka fara zuwa gidan nan tab lallai akwai matsala awurin nan........", muryar goggonce ta katse ta da cewa "Saudatu kinyi shuru baki ce komai ba? ƴa'ƴan abusufyan ne ko? Yarfa hannu saude tayi saboda tama rasa amsar da zata bata, Jinjina kai goggon katsina tayi tare da mayar da idonta kansu hosana da jahad waɗanda jikinsu keta faman kerma saboda tsoran tsohuwar don sun lura tana da ta6in hankali, Rai a6ace tace "Wlh ku ƴa'ƴan abusufyan ne !! Ni zakuyiwa karya don kutmar ubanku !! Kunci buhun ubanku ƴan kan uba !!! , Hankali atashe su hosana ke kallonta,

Table of Contents

Chapters

113 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113