Skip to content

Chapter 42

Chapter 42

Abban Sojoji Book One Complete Hausa Novel 1,205 words 0 views Progress saved
Download Book

da kallo bakomai ne ya faɗo mata arai ba face mahaifiyarsu haka kullum ta kece musu aduk lokacin da suke tunanin zasu rasa ta sai tace, "Idan kuka rasani ba akwai Allah ba, shine gatan kowane bawansa, shi zai tsare ku ya kare mun ku ba wanda ya isa ya taba ku batare da izninsa ba, yana sane daku, tuna wannan yasa jahad jin komai ya dawo mata sabo fal azuciyarta Jiki a mace ta kwanta itama a ƙasan cikin ƙasa a side ɗin husanna ta ɗan ruƙo hannunta a haka suka kwana, ga sauro ga sanyi ga tsoro saboda gidan ba ƙopa, tun da safe da jahad ta farka cike da tsoran kar ace husanna ta mutu, amma tana buɗe ido taga akasin hakan , samun ta tayi zaune hannunta ɗauke da kofi ta dama furar da tsohuwa ta kawo masu jiya wnda ta yarda a ƙasa, sai sha take yi hankalin ta kwance, Cike da tsananin farin ciki tace "shashasha ashe kina nan ! I thought u ave already gone, " murmushi husanna tasaki tare da cewa "Ba kin ce kar na tafi na barki ba that's why i stayed alive,' yar dariya jahad tayi kafin tace"nima yunwa nake ji dan Allah ki rage mun furan wai yaushe ma har ki ka tashi ki ka dama ta? bayan jiya ki ka ce mun mutuwa zaki yi? "Lokaci na ne baiyi ba in yayi zan tafi,' husanna ta bata hamsa tana idasa sipping porridge ɗin da takai a bakinta, dakyar jahad tasamu ta rage mata furar, itama ta sha sai da cikinsu ya ɗanyi nauyi sannan suka tuna basu yi sallar asuba ba, ga tsohuwa har time ɗin she didn't open the door, Haka suka tashi su kaje su ka dauro alwala suka tsaya a kofan ɗakin da tsohuwa take suna cewa "dan Allah ki buɗe mana ko sallaya mu ɗauka muyi sallah, kuma tun jiya muke baki haƙuri amma kin ƙi buɗe mana kopan, Jin shiru bata alamun motsi balle tayi masu magana yasa suka wuce gidan makwabtansu don su gudanar da sallar acen, haka suka ruƙe hannu cikin na juna suka fice gidansu mamee, bayan sun kammala gudanar da sallarsu, mamansu mamee ta kawo musu kosai da kunu a plate saboda ta lura da yunwa a cikinsu, nan suka samu wuri suka zauna saman ledar ɗakinsu suka hau ci, ita mameen ba bata gidan ta tafi school, After each 30 mins sai sun leƙa sun ga ko tsohuwa ta buɗe masu ƙofa but still a datse ta ke, Abun ya wuce na hankali har ƙarfe 2 na rana tayi time ɗin mamee ta dawo daga school nan ta same su jugun, sai da tayi wanka taci abinci sannan ta zauna kusa dasu saman tabarma wadda mamansu ta shimfiɗa musu saboda ciki akwai zafi, kallonsu tayi tace"meya faru ne ? laifi ku ka mata ko har tayi fushi haka? Jahad ta nuna husanna da hannunta tare da cewa "gata nan ita ce ta jefa mata waya a cikin toilet tun daga lkcn ta shike ɗaki ta datse tun daren jiya zuwa ynx" murguɗa baki husanna tayi tace"ae ni ma ba laifina bane kyankyaso ne mai fiffike ya hau mun kaina shine na firgita har wayar ta sulale cikin masan,'' ta ƙare maganan tana hura hanci, Jinjina kai mamee tayi kafin tace"gsky bana tunanin cewa tsohuwa zata iya yin wannan fushin saboda ƙaramar waya nokia harta rufe ɗaki tun yesterday night up to now bata buɗe ba, tabbas there's something behind we've to find it but firstly ya kamata mu fara trying na buɗe kopan, tana cikin wannan bayanin mamansu ta fito daga kitchen tana cewa "nima ina tsammanin hakan, saboda baiwar Allan nan duk yadda zaka 6ata mata rai bata nunawa, maca ce mai haƙuri gsky tsohuwa fa akwai na annabawa sai dai wani abun na daban,' Jikinsu ne yayi sanyi sosai jin wannan maganar daga bakin mamansu mamee, hankalin jahad ba ƙaramin tashi yayi ba, cikin sauri ta miƙe tana cewa"dan Allah ku tashi mu je musa ƙarfi mu buɗe kopan, nidai Allah yasa lafiya...' ta ƙare maganar tana zura silifa ɗin ta a ƙafarta, Suma suka tashi kowa ya zura takalmansu suka fice mamansu mamee kawai suka bari a gidan tana idasa sanwar rana da ta aza, Shiga cikin gidan su kayi cikin hanzari, jahad da mamee suka shiga kaiwa kopar bugu da hannunsu da ƙafafunsu, amma gam bata buɗe ba, ganin zata basu wahala yasa jahad dakatawa ta shiga kitchen ɗinsu ta ɗauko tabarya, "Matsa mamee kar na buge ki" ta faɗi hakan tana ƙoƙarin kaiwa kofan naushi, cikin sauri mamee taja da baya ta koma gefen husanna ta tsaya, Da iya ƙarfinta na ƙarshe ta shiga kaiwa kopan bugu da tabaryar nan, amma gam taƙi buɗuwa ko motsi, a wahalarce ta miƙa wa mamee tabarwar "ke ma ki gwada" hannu tasa ta karba ta shiga bugun kopan amma garam taƙi ko motsi, Sai da husanna ta bari suka sha wahala sun haɗa uban gumi sai nishi suke sannan tace" ku matsa na jaraba nima" ja da baya su kayi suka bata hanya, baya husanna tayi dama shegen ƙarfi gare ta, da gudun gaske ta tunkari kopan naushi ɗaya tayi mata kofar ta balle gaba ɗaya, gaba ɗayansu suka sauke ajiyar zuciya suna murmushin jin daɗi sai dai me !? husanna ce ta fara kutsa kai cikin ɗakin kafin jahad da mamee suka shiga su ma, gabansu ne yayi mugun faɗuwa cikin tsananin firgici jahad ta dafe ƙirji tare da cewa "Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un! Mun shiga uku!!!! Tana faɗin hakan ta yanke jiki ta faɗi sumammiya, fashewa da wani irin matsanancin kuka na tashin hankali husanna tayi tana faɗin "shikenan komai yazo ƙarshe" zube wa tayi saman guiwowinta tana kuka cikin ƙunar rai, Mamee kuwa fita tayi da gudun gaske sai gida ta sanarwa mamansu da abinda ke faruwa, ko hijabi bata tsaya dauka ba, zani ta lullu6a a kanta ta biyo ta suka shigo gidan, Hankalin ta ya tashi ganin tsohuwa baje a ƙasa bakin ta na fidda ruwan kumfa, tama ji ma da mutuwa bakomai bane yafi tayar ma mamansu mamee da hankali ba face ruwan kumfar dake malale a bakinta wannan alama ce dake nuni da cewa poison ne!!! hakan na nufin cewa bata akai tasha, meke shirin faruwa ne? menene ke faruwa? Meye zai biyo baya !? Wannan koke koken da suke yi ne yasa sauran makwabta ji, nan fa mutane suka yo buya guda sai cikin gidan, lokaci guda gidan ya cika da mutane kai hada cincirundon samarin unguwar wasu harta saman katangar gidan suna leƙe, Babban tashin hankalin ma wata mata nan da suke kira da maman baffa tayi tsalle ta dire da cewa "Dama ni banyarda da waɗannan yaran ba! Mayu ne sune suka bata guba taci! dama bamu san asalin su ba haka rana tsaka muka gansu a gidan munafukan Allah asirin ku ya tonu," wata da ga cikinsu ma ta ƙara da cewa"maganarki gaskiya ce maman baffa yara sai shegen kyau ga rashin son shiga mutane ashe su suka son me suke ƙullawa, dama ance tsintacciyar mage bata mage wlh dole mu ɗaukar mata fansa tunda ku bakusan halacci ba, ta janyo ku inuwa kun kaita

Table of Contents

Chapters

113 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113