Skip to content

Chapter 69

Chapter 69

Farar Wuta Book One Complete Hausa Novels 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

komai banda kyawunta don ita ɗin kyakkyawa ce, amma a yanzu ya samu wannan amsar da ya daɗe yana nema, don yadda zuciyarsa ke sake ɗaukan hoton ƙafafun Amina tana masa kyakkyawar ajiya, a wani yanayi ne da wataƙila ko bayan ransa ba zai manta ba. Ta ƙaraso kamar mara gaskiya ta wuce shi ta nufi wajen wani ɗan ƙaramin table da ma'aikatan wajen suka kawo musu abinci kamar yadda ya basu umarni. Kuma sai a sannan tayi magana, tun bayan da suka idar da sallar isha da ya bata wayarsa ta sake kiran mahaifiyarta ta shaida mata cewa basu bar garin ba sai gobe tukunna. "Wanne abincin zan zubo maka?" Yaji ta tambaya daga bayansa inda taje ta tsaya, sai kawai ya ture komai a ransa ya taso ya taho inda take, ta juya bayan nata kamar yadda ya zata tana ƙoƙarin buɗe plates ɗin masu wasu irin manyan-manyan murafe kamar na abincin sarakai, a hankali ƙafafunsa suka tako ta kan carpet ɗin dake shimfide a wajen ya ƙaraso ya tsaya dab da bayan nata idanunsa na nazarin ɗan karamin jikinta dama siraran hannunta, bayan haka tsawonta ma gabadaya iya kafaɗarsa ne, ya san yana da tsawo don shi da Jamal ana cewa duk tsawon Hajiya Maimuna suka yi, amma bai taɓa tsayawa yayi nazarin yadda yafi wani tsawo irin haka ba sai akanta, don ko Ruƙayya ya sani ne cewa da kaɗan yafi ta. Kuma wataƙila shirun da yayi ne yasa ta juyowa a hankali hannunta rike da murfin da ta ɗauko guda ɗaya, idonsa ya sake kaiwa kan kafafunta a yanzu data juyo, sai yanzu ya lura cewa akan farcen kafafun nata akwai kalar baki alamun lallen da bai gama fita ba, kuma yadda farcen ya rabu kala biyu fari da baki yasa shi kasa daina kallonsu. Amina ta sunkuya kalli ƙafafunta da yake kallo tana son ta nemo abinda ke wajen amma bata ga komai ba, yadda yake tsaye dab da ita kaɗai ya isa yasa zuciyarta rabewa gida biyu, amma tunda bata rabe tun a lokacin data fahimci cewa yau zata kwana daya daki daya dashi ba, bata jin a yanzun ma zata yi. Ta sake haɗiye wani abu karo na ba adadi a maƙogwaronta tana son kore ɗimbin tunanin dake kanta kafin ta sake yin magana. "Zaka ci abincin?" Muryarta ta fito ne kamar tana son tuna masa cewa ba'a kafarta fuskarta take ba, kuma hakan yayi aiki don a lokaci guda ya ɗago da idonsa ya kalle ta. "Naci abincinki, kin manta?" Ta yaya zata manta, da wannan busashshiyar doya da ƙwan data soya tun safe yayi buɗa baki, tea ɗin wajen kawai yasha ya cinye doyar gabaɗaya, a lokacin tana waya dasu Amma, tana daga karshen ɗakin kallon yadda yake buɗe-bude a cikin labtop ɗinsa yana cin doyar, wani abu da ya kara nutsar da zuciyarta a cikin kirjinta tana jin dama abinda tayi yafi doyar kaɗai, sannan kuma wani abu da ya fara buɗewa kalaman Amma dake sa hannunta rawa kofa a zuciyarta. Sai ta girgiza kanta a yanzu tana ƙoƙarin cigaba da kallonsa. "Ai wannan ba zai isa ba, idan mutum yayi azumi gwara yaci abinci da yawa." Ya gyaɗa kansa shima yana kallonta. "Na sani, amma raina ne ya fara ɓaci yanzu, bana jin zan iya cin abincin." Kawai sai ta samu kanta da tambayar. "Me ya faru?" Kuma fitowar tambayar yasa taji kamar ta fara yin nisa da taraddadin dake zuciyarta. Hannunsa ɗaya taga ya zura cikin gashin kansa kamar abinda zai faɗa zai yi masa wahala kafin wucewar sakan biyu yace. "Ina da abubuwa da yawa a gabana, so mutane na using wannan opportunity ɗin suna cuta ta, Annual report din MMB- 6 aka aiko min yanzu, kuɗin da suka ce sun kashe a shekarar nan Amina ko ni bani dasu yanzu." Ba maganganun ne suka daki zuciyar Amina ba, sautin muryarsa ne yadda ya fito cike da wani rauni da idan za'ayi musu da ɗimbin mutane zasu kwana suna rantsewa cewa ba daga muryar Ma'aruf wannan raunin yake ba, ba shiri taji ta hadiye wani abu a makogwaronta kafin tace. "Meye MMB-6?" Wataƙila idan ta fara sani meye shi din zata fahimci abinda maganar tasa take nufi. "Asibiti na ne da yake Abuja." Sai ta sake gyaɗa kanta tana jin kamar maganar tafi karfinta, amma kuma kai tsaye sai tace. "Ance idan hankali ya ɓata hankali ake sawa ya nemo shi, yanzu ko ranka ya ɓaci babu abinda zai canja, kamata yayi ka samu nutsuwa mai kyau, sai kayi amfani da hakan ka gano koma wane irin akasi ne aka samu." Maganganun suka tafi har ƙarshen zuciyar Ma'aruf, suna fito da irin kwanciyar hankalin da yake ji a duk lokacin da ya gayawa Mami damuwarsa kuma ta bashi ɗaya daga cikin shawarwarin ta, Amina bata sani bane amma itace mutum ta farko daya dangance shi bayan Ishaq da suka san da zancen asibitin nan. Abu ne da ko Mamin bata sani ba, kuma shi yasa dama yake damuwa duk sanda aka samu matsala akansa don ya san babu wanda zai iya bashi shawara mai kyau akan hakan tunda ko Ishaq baya yiwa zancensa. Kuma haka kurum ya zaɓi boyewa kowa sanin da zaman asibitin don so yake yi da gaske ya binne duk wata halayyarsa ta baya tare dasu kamar yadda yayi wa kansa alƙawari. Zama likita yana daya daga cikin burinsa na farko a duniya, don haka nacin da zuciyarsa ke masa shi yasa shi tsallakewa zuwa garin Abuja ya gina ƙaton asibitin guda inda ya danka amanarsa a hannun wani likita mai suna Sadiq, shi yake jagorantar komai na asinitin don hatta tarin likitocin dake musu aiki shi yake biyansu, shekaru biyar kenan da kafa asibitin, kuma tun bayan shekaru biyun farko aka fara samun matsala a annual report din da suke bashi duk ƙarshen shekara, ya zama kudin da suke cewa duna amfani dashi duk shekara ya fara fin karfin tunaninsa. Sai gashi yanzu minti ɗaya kawai gaban Amina duk dauriyarsa ya kasa riƙe wannan sirrin ya fallasa mata komai, amma kuma da ta bashi sai tasa bai ji yayi nadamar sanar da itan ba, hasalima zuciyarsa gode masa ta dinga yi don aƙalla abinda ta faɗa ɗin ya sama mata wani sauƙin. Sai kawai ya gyaɗa kansa yace. "Thank you." Sannan ya zagayo ta gefen table ɗin yace. "Me zaki zuba mana?" Tambayar tasa ta juyowa itama tana jin nauyin abinda ya faɗa, plates din ya shiga budewa gabadaya yana tara murafansu a hannusa ɗaya. "Wanne kafi so a ciki?" Ta samu kanta da tambaya babu wani dalili. Ya girgiza kansa shima. "Ni zan ci ko meye kika zuba, favourite abinda nake so baya cikin wadannan." Ya fada yana kokarin ajiye murafan a gefe, sannan kai tsaye ya shiga gaya mata irin abincin da yake so wanda kusan duka na gargajiya ne, sanda yace mata har da ɗanwake sai da ta tsaya tana kallonsa, don ita a tunaninta mutane kamarsa basa ɗaukar abincin gargajiya da muhimmanci. Ya tambaye ta abinda take so itama kuma sai ta samu kanta da ture komai a ranta ta shiga gaya masa, kuma da kowacce kalma data faɗa tana ji kamar tana karkaɗe ragowar taraddadin dake ranta

Table of Contents

Chapters

73 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73