Skip to content

Chapter 13

Chapter 13

Farar Wuta Book One Complete Hausa Novels 1,195 words 0 views Progress saved
Download Book

da kujerar motar sannan yayi murmushi. "Kana magana kamar kana neman wani yaro ɗan karami, sau dubu nawa a rayuwata na ɗauki mota na fita da daddare Ishaq?" Yaji yadda Ishaq din ya fitar da numfashi cike da takaici. "Wai ka haukace ne gabadaya Ma'aruf? Yanzun nan fa muka dawo ƙasar nan, minti biyar kawai kayi a gida kayi wanka ka fito! Yanzu ƙarfe nawa? Tara fa ta wuce, ta yaya zaka ɗauki mota ka fita a halin da kake ciki?" Ya sanya ɗaya hannunsa ya cusa yatsuntsa cikin gashinsa yana tuno abinda ya faru bayan barinsu Office ɗin Daddyn, tsaf ya zayyanewa Ishaq abinda Daddyn ya shaida masa tun a hanya kafin su ƙarasa gida, kuma zai iya rantsewa kamar yadda maganar ta tsorata shi haka ta daki Ishaq ɗin shima, amma duk da haka ya boye ta hanyar gaya masa cewa ya kwantar da hankalinsa kawai insha Allah zasu daidaita komai a hankali, wasu maganganu da jinsu kawai yayi a lokacin da yake furtawar. Don suna shiga gida wanka kawai yayi ya shirya cikin wasu riga da wando duka kalar baki sannan ya dauki wata rigar mai hula (hood) da dogon hannu ita kalar ruwan toka ya dora akai, ya rufe kansa da hular amma duk da haka ana ganin sumar kansa data taru itama baƙa wuluk da ita kamar kayan. Lokacin da ya fito falo Ishaq ya shiga wanka shima, don haka wayarsa kawai ya dauka da muƙullin motar Ishaq ɗin yayi waje, don shi tasa motar tana can gida ba'a dawo da ita ba tun ranar da al'amarin ya faru (lokacin da ya ɗauko mutumin da yayi wa duka daga Office ya kaishi wajen Daddyn.) Ya tabbata Ishaq yaji lokacin da maigadi ya buɗe masa gate ya fita, don bai ko bar kan layinsu ba kiransa na farko ya shigo, amma bai dauka ba, sai da ya katse sannan ya lalubo nambar Sameera a cikin wayarsa ya kira. Sameera itace kusan komai na gidan nasu don itake kula da kusan harkar komai a gidan, shi yasa duk wanda zaiyi wani abu sai ya neme ta, saboda haka ya sani duk wani information in dai ya taɓa ratsawa da gidan ba lallai ne taƙi samunsa ba. Daddy ya gaya masa cewa mahaifin yarinyar da suke zancen zata shigo rayuwarsa ɗan'uwan Mami ne kuma sunansa Alhaji Sulaiman. Don haka kai tsaye bayan Sameeran ta gama murnar dawowarsa da kuma shaida masa cewar ai direban Hajiya Madinan da yayi clear dashi kafin ya fito titi zai kawo musu abinci yanzu, sai ya tambaye ta. "Waye Alhaji Sulaiman a ƴanuwan Mami?" Shirunta ya nuna alamun tambayar ta bata mamaki amma duk da haka mamakin nata baiyi tsawo ba tace. "Ko wanda yazo jiya? Ɗan'uwansu Hajiyar Mami ne, yana ɗan zuwa dai ba sosai ba." Ya cije gefen lebbensa kafin ya sake tambayarta. "Da yazo jiyan me yayi?" "Bai wani daɗe ba Yaya, Mallam Sani ma aka saka ya tafi dashi office ɗin Daddy wai zasu yi magana." Da jin haka ya tabbata shine wanda yake nema don haka kai tsaye ya sake tambayarta. "Kin san gidansa?" "A'a, amma Mami tace a Gadon ƙaya yake wai wajen layin transformer." Ya gyada kansa. "Kin san sunan ƴaƴan sa?" "Eh, Babbar dai kawai na sani sunanta Amina." Ya riga ya gama samun abinda yake so don haka ya gyada kansa kawai yana gode mata sannan ya kashe wayar, kwatancen daya kawo shi har kofar gidan kenan a yanzu. "Ina Gadon ƙaya." Ya bawa Ishaq amsa ta cikin wayar. "Gadon ƙaya? Wajen wa? Me zaka yi?" "Ni da kai mun sani cewa abinda Daddy ke shirin ba ƙaramin hadari bane Ishaq, don haka zuwa nayi na warware komai tun kafin lokaci yaja da abinda ba zai taba faruwa ba." "What?" Ƙarara mamaki da kuma fargaba suka fito daga muryar Ishaq ɗin, kuma Ma'aruf zai rantse ya shiga girgiza kansa lokacin da yake faɗin. "Kar kayi haka Ma'aruf dan Allah, ka juyo ka dawo. Zuwa wajen mutumin nan ba shine zai kwance komai ba..." "Ba wajensa nazo ba don dashi da Daddy duk abu ɗaya ne. Ita nazo gani Ishaq, saboda a yanzu maganar ta koma ni da ita kawai." "Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un... Ma'aruf me zaka yi?" Salatin ya saka shi sake yin murmushi yana cije lebbensa. "Nuna mata zanyi irin ramin da ake shirin jefa ta, nuna mata zanyi da gaske bani da hankali." "B, tsaya kaji..." Dib. Ya katse kiran ya ma kashe wayar gabaɗaya. Idonsa ya sake kallon ƙofar gidan yayin da zuciyarsa ke zana masa dukkan hotunan abinda zai faru kafin ya kashe motar ya fito. Ya sake janyo hular rigar yana ƙara rufe fuskarsa daidai lokacin da wasu yara biyu mace da namiji suka zo shiga gidan idanunsu akan shi da kuma motarsa. Da sauri ya yafito namijin alamun yazo. Ya kuwa taho yayin da macen ta tsaya tana kallon su hannunta rike da wani abu da take ta lasa. "Bigboy ya sunanka?" Amon muryarsa mai zurfi da taushi ya tambaya sanda yaron ya ƙaraso. "Adam." Ya gyada kansa yana murmushi lokacin da ya zaro wata sabuwar ɗari biyar daga aljihunsa yana miƙo nasa. "Idan ka shiga gidan nan Adam kace wai Amina tazo." "Toh." Ya amsa da nasa murmushin shima sannan ya juya, idanunsa ko kaɗan bama su ga kuɗin da yake bashi ba. Da murmushin da bai san dalilinsa ba Ma'aruf ya maida kudinsa cikin aljihu yana kallon tafiyarsu zuwa ciki, ƴar yarinyar har sai da sake juyowa ta kalle shi lokacin da Adam ɗin yaja hannunta zuwa ciki. A hankali ya dawo da fuskarsa kan katangar gidan, idanunsa na hasko masa dukkan abinda zai faru nan da mintunan dake shirin tahowa! *** Me zai faru?? Me zai faru?? . . . Me Ma'aruf zaiyi?? #Aysha Shafi'ee. #FikraWriters #FararWuta. BABI NA HUDU. ~~~~~ "Kiyi hakuri Amina, amma sun shaida min cewa yaron yana da matsalar taɓin hankali!" A daidai sanda ya rufe bakinsa, a daidai lokacin aka haska wata walƙiya har da tsawa a cikin ɗakin! Kuma bayan walƙiyar ta ɗauke a idanun Amina, Baba ya cigaba da maganarsa. "Wannan maganar ita ta sanya a safiyar yau dana shaidawa Kawu mallam dukkan abinda ya faru ya tara meeting din da ya sanya yinin mu a gidan, don har su Kawu Ibrahim da Kawu Hamza sun zo a yau..." Ba shiri tasirin sunayen ya sanya Amina ta sake ɗago da idanunta ta kalli mahaifin nata, yayyen Baba hudu ne kuma shine ƙaraminsu, Daga Kawu mallam sai Kawu Abubakar da suke kira da 'Baban kurna' sai kuma Kawu Ibrahim da Kawu Hamzan da dukkansu biyun suke zaune a garin Abuja tare da iyalansu, don haka bata san adadin mamakin da zata iya kiyastawa ba na cewar saboda maganarta Kawu mallam ya taso su a yau tun daga can suka zo, ganin yadda Babn ke kallonta yana son fassara yanayinta yasa ta maida idanunta ƙasa a hankali yayin da hannunta na dama ya kamo karshen skirt dinta da ƙarfi. "Amina a jiya babu irin boren da mahaifiyarki bata yi min ba akan maganar nan, dukkan ku shaida ne cewa Halima mace ce mai biyayya gare ni, don tun daga ƙuruciyarku har yanzu babu ranar da ɗayanku zai ce kunji kanmu

Table of Contents

Chapters

73 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73