Skip to content

Chapter 8

Chapter 8

AURENMU Book One Complete Hausa Novel 1,239 words 0 views Progress saved
Download Book

bare ma su roki me gadi ya basu aro. Mun jawa kanmu mun Sha kokonmu amma Muka ki godewa Allah cewar Charity a haka me aiki ta sake kawo musu lafiyayyen abinci haka suka sake cika cikinsu amma idan suka tuna gida sai kuka har bacci ya kwashe su. Washe Gari Suka Yi Sallah suka fito suna tunanin ganin wani ba kowa sai me aiki tana girki sunyi sunyi akan ta fadawa oga zasu tafi Amma tace ya Mata warning baza ta je ba,Wasa Wasa har Suka kwashe kwana uku a gidan basu ga ko Kare ba tun suna cin abinci suna murna har bacin rai da tsoro ya hanasu ci,ga abincin suna gani amma sun kasa ci ba kwanciyar hankali. Gidan su Nusaiba tun suna tunanin yawan banza ta tafi har Suka dawo kuka da addua,Shehu sabo da Yana cikin bacin rai har da basu kudin cefane,Mama ta dafa shinkafa da wake da Mai da yaji,Ihsan tace ga shinkafa yau zamu ci amma abin haushin Aunty bata nan suna bakin ciki suna murna ta wani bangaren zasu ci shinkafa,mutanen layin sai jaje ake musu ana tayasu da addua Allah ya bayyana su Nusaiba,Shehu akan baya so ya kashe kudinsa yace ba inda Zan Kai Sadaka a tayani da addua da kaina Zan roki Allah watakil ma nafi malaman matsayi a wajen Allah muyi addua da kanmu,Mama tana hawaye komai na sana'arta ya tsaya yarta ta bace tace ai ba malamai aka ce ka bi ba cewa akayi ka bada a masallaci a tayamu da addua sai kayiwa Almajirai Sadaka,Shehu yace ai ke baki San Allah ba tunaninku mata kullum a bi malamai idan baza kiyi Addua da kanki ba ki barshi,Mama cikin jarinta ta dauki dari biyar ta bawa Ameer danta tace ungo kaje masallacin juma'a kaga yau Juma'a ka siyi ruwa na du kudin ka rabawa Alummar annabi Allah ya bayyana Mana su Nusaiba,Ameer ya karba da sauri ya tafi zai siyi ruwa ya rabawa Alummar annabi Sadaqa,Mama tana da filinta na gado ta ajiye abinta,sabo da tayi Sadaka Allah ya bayyana Mata yarta tace zata siyar da filin,Shehu Sadakar dari biyu ya kasa Amma tana daga filinta zata siyar yace zai siya ya lallaba Mama zai siyi fili,filin a Kauye yake Bai wuce dubu dari biyu ba amma Shehu yace filin Bai wuce dubu dari da talatin ba Mama bata San Kan komai ba yace ya siya zai bada kudi ya lallaba ya karbe takardu tayi signing da komai shima haka ba shedu bata fadawa kowa ba Shehu ya hana kudi tana ta binsa karshe ma Sai labari taji ya siyar da filin dubu dari uku Kuma ko ficika bai bata ba,idan tayi yaji ta tafi ta barwa wa yaranta ga yarta har sati guda shuru,Mama ta kwana takeyi tana kuka tana kaiwa Allah kukanta. Charity idonsu duk ya kumbura sabo da kuka basu ga kowa ba Kuma an hanasu fita,Oga zai iya sati biyu a gida ba tare da ya leko ko compound ba Haka yake shi,Sun wanke kayansu ya bushe sun maida shi jikiksu bayan sunyi wanka,Palo Suka dawo Suka zauna babu Wacce tayiwa Yar uwarta magana sunyi jugum jugum a Palo,Tv tana yi Amma ko kallonta basu Yi,kamshi suka ji ya mamaye palon,wani me uban kyau Suka gani yana sakkowa daga steps sanye yake cikin wani silk doguwar Riga Kuma armless gefe da gefe an tsagata Silver color takalminsa ma haka sumarsa ta Sha gyara na musamman fadar kyawunsa bata baki ne komai nasa na daban ne,sheki Kawai yake da walwali,kwarjininsa ya kamasu Suka kasa magana har ya samu kujera ya zauna irin Zama na isassu na masu Hannu da shuni kana gani kasan Hutu ya ratsa shi. Gyaran murya yayi kadan lokacin Charity tace Ina yini cike da Ladabi Nusaiba Kuwa ta kafe shi da Ido tana kallonsa sai da Charity ta dan bigi hannunta sannan tace Ina kwana au na manta Ina yini? A takaice ya amsa ya kalli Nusaiba yace ke kina kama da Baban Mum da gani jikarsa ce ko?,da sauri Nusaiba tace ae,ya kalli Charity yace ke da alama Yar Hajjo ce ta gangare ko? Charity tace ae,yace sorry Allah yaji kanta,Charity tace Ameen harda kuka dan a barsu su tafi tace ka tuna min da babana Yana can shi daya gwara na koma, Oga yace har Kun gaji baza ku tafi yanzu ba ya Dace ku huta sosai ya furta tare da mikewa ya fice suna ji ya shiga mota, Nusaiba suka sake fashewa da kuka,tunda ya fita bai dawo ba sai tsakar dare sunyi bacci lokacin harda siyo musu kayan makulashe da safe suna tashi suka gani a bakin kofar su Leda guda, Charity tace wlh da wannan kayan dadin gwara muna gidan Iyayenmu,Nusaiba ta kalleta tace hmm ai ni abin ya isheni gashi Muna fadar gaskiya za a kamamu sai gidan kaso masu kudi zasu Yi tunanin ma da abinda ya kawo mu,ai Kar mu sake mu fada Kuma Kinga Yana kamamu sai Iyayenmu sunji abinda muke yi,Nusaiba tace badluck, har suka gaji suka fito suna zaga gidan ko Ina sai da suka gani sun Sha kallo amma Sam abin baya birge su burunsu su koma gida,Palo suka koma sai gashi a zaune Yana kallon film sannan Yana latsa wayarsa. Zama suka Yi can nesa da shi yace hope Kuna Jin dadin birni ya furta Yana kallon Nusaiba, Charity tace sosai ma Alhmdllh amma gida muke so mu tafi yau Iyayenmu zasu Mana fada,Ogan yace ai Indai kunce a nan kuke ba matsala kadaici ya min yawa kuyi zamanku kwa dan ebe min kewa ko ba komai na dinga Jin motsin mutane, Nusaiba ce ta kalli Charity suka hada Ido idanuwansu ya ciko da kwalla zasu Yi kuka ya tashi ya haura sama shi dama ya gaji da Shuru shi kadai a gida ga Yan uwa sunzo yaji motsin mutane ko da na yan satikai ne, Yana fita Charity tace kamar fa wannan mutumin kwakwalwarsa a takashinsa take ta kowa a kansa aka Masa brain amma Banda shi tasa a takashi aka Masa ita baya tunanin Iyayen nu chab Aisha ce ta shiga motarta tana tukawa a layin har makwafta suka tsiri zuwa suna gaida su Sabo da aga ta siyi mota ko Ina da key a hannunta tana karkadawa,Sunday Yana gida Aisha anci gayu ta fito tace Maggi fa ya Kare sannan ba kayan miya ko yaji Banda shi bare nayi Mana shinkafa da wake,Farooq yace Wai ku Mata me yasa baku da hankali ne sau Nawa Ina fada miki idan Abu ya kusa karewa ki sanar min amma kinki ji sai komai ya Kare kat Zaki zo ki fada min to yanzu kin San wata yayi nisa ba kudi sai mu yini haka ya furta Yana Jan tsaki,Aisha tace Farooq kafa isheni tsakani da Allah na gaji Kai ba haihuwa kake ba how many years? 5yrs da auren mu maimakon ka lallaba ni sabo da nice ke hakuri Ina taimaka maka wajen Zama da Kai ba haihuwa Alfarma fa nake maka,for how long Zan dinga jira ba haihuwa ta juya ta saka Hijab ta fice ba ko neman izini haka tasa kudinta tayi cefane ta dafa abincinta ita kadai taci na Rana ta boye

Table of Contents

Chapters

71 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71