Chapter 20
Chapter 20
siya Mata,shi yasa tazo kano ta Kama gidan haya har Suka hadu da Affan suke fada Kuma kusan a tare Suka zo Kama gidan ta Sha Matukar wahala a hannun Hussain kafin Allah ya yanke mata. Affan Affan Kuwa asalin Fulanin Zamfara state ne, sunansa Aliyu A. Aliyu,mahaifinsu su biyu Maza ya Haifa Yusuf shine Babba an haife shi da shekaru hudu aka samu cikin Affan,da cikin Affan Allah yayiwa babansu Aliyu rasuwa,Babar su tana haihuwa aka sakawa Affan sunan Mahaifinsa wato Aliyu shine aka boye sunan ake kiransa da Affan, su biyu Suka taso a hannun mamansu a Zamfara duk da cewar babansu bai mutu ya bar wata kadara ba face wata gona layi biyu,bayan Yusuf da Affan sun gama secondary School babu kudin ci gaba da karatu,sai Mamansu ta siyar da gonakin nasu ta hada kudin kaf ta Kira Yusuf da Affan tace kunga kudin nan nasan bazai isheku kuyi karatu ba ku biyu Kuma ina so a cikinku wani yaje yayi degree a rayuwa ya kuke gani Kai Yusuf gadon ku ne idan Kuma kowa bazai iya barwa kowa ba to sai dai mu Kama sana'a da kudin,Yusuf ya kalli Affan yace gaskiya ni bazan iya barwa Affan kudina ba,Affan Kuwa Nan take yace Yaya Yusuf ni na hakura da karatun dama kaga nine karami na bar maka kudin gado na halak malak kaje kayi karatu idan ka samu aiki daga baya ka biya min ni nayi karatun daga baya ai ba'a girma da karatu,Yusuf yayi farin ciki sosai karshe aka Nemo admission lokacin baya wahala a ABU Zaria Yusuf ya shiga ya gama degree dinsa gashi Allah ya hadashi da Abokinsa Dan gidan me kudi ya ja shi cikin Harkar kasuwancinsu na siyar da gwala gwalai har aka zo ma ana tura Yusuf kasar waje yana siyo kayan, a hankali a hankali Yusuf ya Zama me kudin gaske ya kera katafaren gida a Kaduna gida na gani na fada,ko aikin gomnati ma bai nema ba,ya manta da halaccin da Affan ya Masa ya kasa tunawa ya sashi a university,karshe da yazo zamfara da galleliyar motarsa Wai yazo daukan Mamansu zai maida ta can Kaduna kusa da shi,Mama tace Yusuf Saura Affan Yana ta Zama ba karatu burina ka biyawa Affan shima yayi karatu ya shiga University yace to zaiyi cikin ikon Allah watan mamansu Uku kacal a gidan danta ta kamu da ciwon sugar farar daya ta rasu dake Affan shima Yana gidan Yusuf din tun asali Allah yayo shi da son Gayu da tsafta ga iya daukan wanka dama Kuma gasu kyawawan gaske. Bayan mamansu ta rasu da watanni Yusuf ya fara wulakanta Affan kamar ba gidan dan Uwansa ba,karshe Affan har ya gaji ya fara sana'a haka Kawai sai ya saro irin Guava ya dinga siyarwa Yana samun kudinsa baya kula kayan Yayansa,ya koma sarar irin su safa da handkerchief yana bin titin kwalta a hannu Yana siyarwa,ya dawo ya koma koma siyar da su charger a gefen titi da Haka ya samu ya shiga University amma shi BUK ya samu a Kano ya dawo Kano Hostel a school ranar da ba school ya tafi siyar da kayansa a gefen hanya,har ya hadu da wani babban mutum yace yazo ya dinga zauna Masa a shago a kasuwar kofar wanbai Harkar Yan robobi,ya koma can Yana fama a Haka ya kammala degree ga Yayansa can kullum arzikinsa Kara gaba yake amma sisi baya bawa Affan bai ma San Ina yake rayuwa ba,Affan wata yarinya ya samu Yar talakawa Suka Fara soyayya Nabeela,Yana mugun kaunarta Kamar ransa a Kaduna take Mamanta tana da ciwon zuciya kullum Affan akan taimaka musu yake duk abinda ya samo a wajen Maman budurwarsa yake karewa wajen nema Mata lafiya,Neman kudi yake Yana samu amma Maman budurwa kullum a asibiti can yake Kai kudin,magunguna shine ke siya, Basu da abincin ci shi zai siya musu a Haka jarinsa ya tarwatse babu ko sisi,Watarana Affan yaje zance Sabo da Nabeela ya koma Kaduna,ta rako shi gefen titi kenan Suka hadu da Yayansa Yusuf zai wuce a mota ya tsaya,Affan yace Yaya Suka gaisa ya nuna Masa Nabeela yace itace budurwata yace Nabeela ga yayana uwarmu Daya uban mu daya tace oh suka gaisa Yusuf sai kallonta yake gaba Daya Nabeela ta tafi da imaninsa,bayan Affan ya shiga Napep ya tafi sai ya dawo da motarsa ya Sha Gaban Nabeela yace ta shigo ya rage Mata hanya,Bata kawo komai ba ta shiga motarsa Suka tafi har gidansu har take fada Masa rashin lafiyar mamanta ya shiga gidan Suka gaisa tashi Daya ya basu dubu dari biyu,zuwa sati Yusuf ya koma gidan su Nabeela yace ta shirya zai fitar da mamanta kasar waje India nemo Mata lafiya Suka dinga murna Affan ma tuni Suka daina ta tasa idan yazo ma bata taba fada Masa Yayansa Yana zuwa ba ko dan kudi ya bata sai Taki karba tace Alhmdllh karka damu yanzu Allah ya hore mana, bata fada Masa zasu je India ba Kawai Yusuf ya musu visa da komai Suka je can ai Kuwa Maman ta warke ta samu lafiya Suka dawo garau da ita,Sabo da irin kudin da Yusuf ke kashe musu Yana cewa zai turo manya Suka ce ba matsala,ya turo da danginsa na zamfara Kuwa aka tsaida ranar aure, Affan Yana ta zuwa zance bai taba sani ba yaji dai Yayansa zaiyi aure,ranar data Kama daurin auren Nabeela da Yusuf sai Allah ya kawo Affan yazo zance da safe Dan lokacin ma a gidan wani Abokinsa yake zaune ai Kuwa ya iske abin mamaki Yayansa ya aure Masa budurwa har an daura aure ma ana ta hotuna,Nabeela ta fito Suka hada Ido da Affan ta fashe da kukan munafunci,Affan mutuwar tsaye yayi Kawai hawaye na tsiyaya a idanunsa tunda ya tabbatar Kawai ya juya ya bar gidan. Yusuf Yana ta Neman Affan yasan yayi laifi, Affan Kuwa yafi sati biyu Yana cutar so,Abokinsa sayyeed shine ke ta tausarsa har ya dan Fara hakuri ya Sha wahala ya rame sosai ya fita hayyacinsa Yana mugun kaunar Nabeela,lokacin Nabeela ma tuna abinda tayi na cin Amana ya hanata sukuni a gidan miji,Yusuf ya kasa Gane kanta dole ya Nemo Affan yazo har dakin Abokinsa ya samu Affan yace Affan sai dai fa kayi hakuri,na kashe kudi...Affan yace dakata Mallam ni kasan me na musu jarina kaf na karar bani da shi na iya taimakon su Kai Kuma kana da arziki idan kayi ma baka birge ba domin nasan da Kaine a halin da nake ciki na talauci baza ka iya sadaukar da arzikinka garesu ba,Indai akan macece kaje na hakura na bar maka har abada Kai jinina ne amma idan kayi da kyau ma ka sani idan ma baka Yi da kyau ba ka sani kanka Kuma Allah Yana kallonka,Suna haka Nabeela Katsam sai gata itama ta fito daga gidan auren nata tana cewa Dan Allah Affan ka yafe min,Affan ya kalleta yace bazan taba yafe Miki ba Nabeela kinfi Yusuf Laifi tunda da baki bashi kofa ba keda mamanki da Haka bata faru ba na tsaneki a rayuwata nayi nadamar saninki a rayuwata mayaudariya makaryaciya suna kallo ya hada kayansa ya dakko kudinsa da ya Dade Yana tarawa a asusu ya fice
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71