Chapter 15
Chapter 15
ta fada Saman bed bata san da mutum ba ta manta jikinta ya mutu Affan Yana bacci yaji jiki me laushi ya fado Kansa Tashi yayi da sauri yaga itace tana shigewa jikinsa da sauri ya dirga kasa daga bed din har zai kwanta a kasa ya tuna shi fa guy ne baya kazanta Tsaki ya ja yabi ta window ya koma dakinsa yace aikin banza warin balaga takeyi ma Yana karkade jikinsa harda shinshina inda ta fado Masa a jiki yace kaji ko warinta ya manne min a jiki irin wannan warin sai na balaga yanzu ma ta Fara balaga na rainata ma banza ta gyara min daki kwadayayya ta cinye min kazata ya furta tare da fadawa saman bed dinsa ya kwanta Kiran Sallah yaji an kwala yace ta cuceni ban karasa baccina ba ya tashi ya daura Alwala ya wuce masallaci yana doro da carbi a hannunsa Kalar jallabiyarsa kullum ko masallaci zai je carbinsa ma toomatch yake da carbi da kayansa carbinsa sunfi kala hamsim ko wanne Kaya da Kalar carbinsa ana taku dai dai ya shiga masallacin unguwar, Liman ya sanshi Yana shigowa zaka ji kamshinsa Yana bawa liman dariya sai dai Yana birge mutane duk gayunsa Sallah a jam'i kullum ba fashi ko wacce Sallah har sun Saba da liman da duk wani me zuwa masallacin. Sai da aka idar da Sallah Affan ya daga hannu sama Yana Addua Allah ka azurtani,Allah ka bani kudi....kudi ya Allah na halak...Liman yace samari barka da asuba Affan yace Morning liman how are you? Dariya liman yayi yace Alhmdllh, Affan ya mike tsaye yace lafiya dai liman muyi Maganar a tsaye sabo da rigata zata yamutse ka ganta ta Sha guga bana so ta yamutse na tafi hanya a haka,liman ya zaro Ido yace asuba ce fa yaro da sauran duhu wa zai ganka,Sabo da jin dadin kaina ai ni Zan kalli kaina cewar Affan,Liman ya jinjina kai Yace baka da aure ne? Affan yace wuuu Ni aure rufa min asiri da yanzu Ina nan hankali a tashe Ni da cikakken bacci munyi hannun riga,Liman Murmushi yayi yace kaga Kuma da zaka Yi auren sai kafi haka nutsuwa,Affan yace to nifa gaskiya bana son aure yanzu mace ta dameni da kudin cefane kaina ma da kyar nake rikewa,Liman yayi dariya yace baka da budurwa saurayi kamarka kyakyawa da Kai haka kowa ya ganka yaga Namiji irin Kalar da Mata ke yayi,Affan ya shafa sajensa yace ba ruwana haka Kawai soyayya yanzu sai da kudi inje in tari budurwa bani da abin bata ta ci min mutunci,Liman me kudi ne na gaske yace kaje ka kula ko wace Indai da aure kake sonta Ni Kuma ko nawa zaka Bata Yar hidimar Mata dai Zan dinga baka har muga abinda Allah zaiyi, Affan yace to yaji samun kudi yace dama Ina da budurwa Ina sonta fada mukayi akan kudin anko tana so na za ayi biki na kasa siya Mata anko kunya tasa da kaina na fece,Liman yace tayi aure ko bata Yi ba? Bata Yi aure ba jirana takeyi Kawai Liman yace ka koma ka Bata hakuri ku daidaita Yar hidimar Mata dai Zan dinga baka har a tsaida Maganar aure ya kamata ace kana da aure bai dace mutum me addini irinka ba ka zauna haka Kuma muna limamai mu zuba muku Ido bayan Allah ya hore Mana yanda zamu tallafeku, Affan yayi godiya ya fice Yana murna a ransa wurin samun kudi ya samu shi Kam Yana cewa Allah na gode ma ka amsa Addua ta sai ta fada Kan liman. Kwanan Nusaiba biyu a daki a kulle Aslam ya kulleta yace sai ta fito Masa da motarsa abinci ma Dan kadan yake Dan zubawa ya Mika mata,tana ta kuka ta dinga Kiran Mama a waya,ba shiri Mama ta sauka a kofar gidan Charity tana bakin kofar da aka kulle Nusaiba tace ki fito Masa da motarsa a zauna lafiya,Nusaiba tace sai naci uwarki shegiya munafuka,Aslam Yana gidan yaji ana bubbuga gate yaje ya bude yaga mama ce ta shigo tana karewa gidan kallo tace Ina kudinka? Ina motocinka makaryacin banza dama karya kaje kake Mana ka jefa yata a masifar talauci,Aslam yace kije ki fadawa yarki ta fito min da motata,Mama ta kalle shi tace butulu wato babu mutunci ba girmamawa Aslam bai kulata ba suka shiga ciki yasa key ya Bude dakin Daya kulle Nusaiba Yana tsaye ya tare Hanya Mama ta shiga tana shiga ya maida kofa ya datse ya kulle su tare a dakin yace ku fito min da motata na fada muku,Mama ta zaro ido tace dama haka yake baida mutunci,Nusaiba tana hawaye tace wlh Mama zai kashe mu Yana da bindiga,Mama tace kwantar da hankalinki yanzu Ina motar? tace na siyar da ita ko kudin ma ban karba ba ya kulle ni,a jikin kofar Mama ta tsaya tace dan Allah surukina ka Bude mu sai muje a karbo maka motarka,Aslam ya kalli Charity dake sanye da Riga da skert na Atamfa wasu kodaddu yace wlh mutanen nan sun maidani wani banza,tunaninsu Banda hankali, charity tace yo ai Basu san da hankalinka bane basu san Kai cikakken Namiji bane sai yanzu,Aslam yace dan Allah? Charity tace Allah,yanzu ni cikakken Namiji ne? Ae sosai yanzu na tabbatar Amma da ka zauna Kamar solobuyo,Murmushi Aslam yayi yace Ni kaina sai najini wani na sake girma yanzu, Charity tace ah ai sai yanzu ni kaina na ganka kato,yace haba,? Tace Allah da karami nake ganinka, dariya sukayi Siyama tace Kara sa key na uku a fito da mota,Aslam ya bubbuga kofa gam gam hankalin su Nusaiba ya sake tashi yace a fito da mota,abinda zai muku zakuyi mamaki idan baku fito da mota ba cewar Charity tana taya Aslam Kamar kanwarsa. Sai zuwa Safiya Aslam ya Bude kofa zai Basu abinci Nusaiba ta kwada Masa tsinin takalmi choge Nan take ya dafe Kai ya Fadi kasa a sume ga Charity bata kusa da gudu Nusaiba da Mama Suka fice daga gidan suka tafi wurin siyar da motoci zasu karbi kudi babu Wanda ya karbi mota ba alamarsa Suka tambayar duniya akace ba a sanshi ba Ashe Dan damfara ne barawon mota Kuma ya gudu da mota,Nusaiba sai da ta Fadi har kasa sabo da kudin ta gama kasafin su,ba kunya suka tashi Suka koma gidan Aslam,lokacin Charity ta shigo ta kwala ihu ganinsa a kwance jini na zuba ta Kansa da gudu ta fita ta samo wasu maza biyu Suka taimaka Mata aka sashi a mota taxi zuwa asibiti,Allah yasa Babu matsalar kirki dressing Suka Masa bayan ya farfado suka dawo gida Kansa nade da bandage Charity tana Masa Sannu sannan tana bashi hakuri har Maman Nusaiba ta shigo da gudu tana kuka tace Nusaiba ce ta Sume,Siyama ta rude ta fita taga Nusaiba a sume tayi suman karya sun hada wayo,Aslam ya fito shima da Kansa ya dauki Nusaiba Kamar bai gano su ba ya shigar da ita bedroom ya kulle ya sake sa key yace sai ta fito min da motata,Mama da tana murna Aslam ya yarda da karyar su, yace Mama tun kafin na dakko bindiga ki bar min gida,Mama da gudu ta fice daga gidan,Charity tace dan Allah kayi hakuri
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71