Chapter 2
Chapter 2
damu muna tare fa sai lokacin Mustapha ya saki ransa suka ci gaba da labarin duniya. Affan gida yazo da Niyyar shiga sai ga wani Mallam yasha babbar riga da rawani ya tsaida Affan yace Saurayi Innalillahi wa Innailayhirraju'un, masifa ta tunkaro ka,Mallam yaga Affan Kalar Naira ya dau wanka Kalar me kudi yace kana da makiya Alhaji wasu suna nan zasu sace maka mota,Affan ya bude baki yasan karya yake shi da baida mota,yace sannan makiyanka Yan uwanka ne sun Kai sunanka za a maka asiri kwana nan zaka rasa milliyoyin kudi a cikin dukiyarka,Affan ya sheke da dariya a ransa Shi da bai da ko sisi yanzu ma bashin dubu uku ya samo da kyar,a fili gigicewa yayi yace yanzu Mallam ya zanyi kenan? Me ya kamata ayi? Mallam farin ciki ya kamashi ya samu gara zai cuce shi,yace dubu dari zaka kawo ayi aiki me zafi a kansu,Farooq yace an gama bani Address din gidan naka yanzu banda kudi a hannuna,Nan take Mallam jiki na rawa yace ya bada address Affan ya wuce gida,Yana cikin palonsa dake estate din kowa bangarensa Palo da 2 Bedroom ne a hadadden Estate a haka ma Sai me kudi ko ma'aikata ke Kama gida a ciki da gate dinsu da komai kowa da part dinsa,Yana ta kora lemo da bread babu kayan abinci. Raudat ce tayi parking motarta ta iske Hajiya Mairo a compound kusa da part dinta turaruka ta Bata kyauta masu kyau,Mairo tana ta murna mugun shiri sukeyi da Raudat har abinci ma idan Mairo taga dama a part din Raudat take ci itama Raudat tana ci a wajen Mairo duk gidan tasu tazo daya suna morar juna,Raudat tace landlady wancan Kuwa ya biya kudin haya? baki Hajiya Mairo ta tabe tace yo mutumin banza Ina zai iya kullum sai wanka bako sisi na gaji da halinsa a gidan nan nawa kwana nan Zan kore shi,Raudat kasa kasa tace mene amfaninsa face kora ko dubu Hamsim bazai iya hadawa ba bare dubu dari biyu,Suna haka sai ga Affan ya fito ya dau uban wanka cikin kana nan Kaya Yana taku dai dai Yana takama ko kallonsu baiyi ba ya fice suka bishi da kallo cike da mamakin yanda yake da mugun gadara baida aiki sai wanka kullum cikin kamshi amma babu ko kobo. Wani kanti yaje inda suke siyayya kusa da gidansu Suka tafa da me kantin yace a wannan wanka haka Affan Ina zaka je ne? Affan yace tafiya zanyi Ina so zanje Abuja ne akwai wani business da nake ya zuba karya yace gashi ma kaga Atm dina yaki aiki,me kanti sabo da yasan Affan Yana Masa ciniki Yana ganinsa cikin kyakyawar shiga ya zaci me kudi ne yace gaskiya kana tafiye tafiye Oga ko yaushe a Hanya, Affan yace ya za ayi Harkar Business ai in kana Business ba zama yanzu ma bank Zan koma Ina so zanyi siyayya kudi yaki fita dan Allah zan karbi kaya idan na dawo daga tafiya sai na kawo ma kudin, nan take me shago yace ba damuwa komai normal ebi abinda kake so,Affan ya kwashi manyan manyan madarar gari su gwagwanin Milo kayan tea sosai ya hada sannan ya kwashi su tumatir din gongoni,shinkafa yasa ya auna Masa kwano biyar,wake,taliya, macaroni komai ya har su Mai da kwai sai da ya hada akayi Total aka rubuta a list din Yan bashi ya fita,Yana kaiwa gida ya zauna ya shirya girki me rai da lafiya yaci ya koshi sannan ya fito sai gidan Mallam Wanda ya karbi Address. Affan ba kudin mota a kafa ya dinga tafiya sai da yaci bakar wahala kafin ya Isa gidan Mallam Yana zuwa yaga gidan Mallam hadden gaske sama da kasa,bai Sha wahala ba aka kaishi har part din Mallam,Mallam Yana zaune shi da wani Yana fada Masa karya dan ya karbe Masa kudi,Bayan ya sallameshi Suka gaisa da Affan, Affan yace Mallam ka firgita ni shi yasa nazo da wuri kaganni sauri nakeyi zanyi tafiya yanzu ba kudi a hannuna Kuma tafiyar wani kudade Zan karbo shi yasa nazo yanzu ka bani dubu Hamsim kafin na dawo sai na baka dubu dari biyu ma kaci harda riba,Mallam Yana Jin Haka ya haukace zai samu kudi ba bata lokaci ya irgo kudi dubu Hamsim ya bawa Affan ,yayi godiya tare da cewa sai ya dawo ya fice,Yana fita yazo ya biya me shago kudin kayan abincinsa tas harda samun canji ya shiga harkarsa. Mallam Shuru Shuru Babu Affan ba labarinsa bai San Kuma inda zai ganshi ba,Affan yaci wanka cikin wani yadi me kyau Yana taku dai dai sai ga Raudat ta taso daga aiki ta tsaya kusa da shi tare da sauke glass tace Affan shigo na rage ma hanya Naga Kamar gida zaka je,cike da rashin mutunci yace ke kin Isa ki taimakeni,akan wannan banzar motar taki har kin Isa ki rage min Hanya ya juya da Niyyar tafiya Katsam sai yaga Mallam shi da wani suna ta magana juyawa yayi da sauri ya bude motar Raudat ya Shiga gaba taja mota suka tafi Babu Wanda ya kula wani,sai da Suka Yi nisa tace da kace baza ka shiga ba me yasa ka canja? Cikin bala'i yace to sabo da na Shiga motarki shine Zaki Raina min hankali motar ki din banza motarki din wofi,Parking Raudat tayi tace amma baka San mutunci ba fitar min a mota,Tsaki yaja ya Bude kofa ya fice tare da furta banzar mota bayan ma ba da kudin halak Kika siya ba maza ne Suka siya Miki Karuwar banza da kudin karauwanci Kika mallaki mota tunaninki bamu sani ba Alhaji Sanata ko dan majalisa ya siya Miki ya daki motar da kafa yaci gaba da tafiya cikin gadara,Raudat ce ta leko ta window tace mutumin da ya kasa biyan kudin gida talaka da Kai baza ka taba iya siyen mota irin tawa ba Never, wace zata kulaka a haka Kai a dole kyakyawa kana daukan wanka ba abinka ka iya sai siyen Kaya kana nan kayan ma duk na gwanjo ne ta fisgi mota taja gaba,yace stupid girl Wai ita me mota Allah ya kiyaye na shiga motar haram. Raudat yau da takaicin Affan ta dawo tana zuwa bayan taci abinci ta fito ta faki Ido kowa ta taka tsani tayi disconnecting wutar gidan Affan ta danna switch dinsa ta sakko ta koma gidanta,Yana dawowa ya kunna ko Ina duf babu wuta ya rasa dalili gashi gudun Landlady yake tana ganinsa zata ce ya biya ta kudin haya,shima Fitowa yayi Raudat tana ganinsa ta window tana ta kyalkyala dariya Yana dubawa yasan itace sai ya kunna nasa ya kashe nata wutar itama sai gata ta fito da masifa Affan kana neman masifa abinda kakeyi ka takura min a gidan nan Zan dauki mataki a kanka, Affan yace amma ke banza ce wawiya Naga alama so kike nace Ina sonki to wannan bazai Yi tasiri ba,nafi karfinki kije ki samu dai dai dake, me zanci da Kai me zaka iya siyawa matarka kudin gida ma ka kasa biya me zaka iya,Hajiya Mairo me gidan itace ta shigo da dalleliyar motarta ta fito tace Wai ku meke damunku ne baku da aiki sai fada a gidan nan me ya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71