Skip to content

Chapter 29

Chapter 29

AURENMU Book One Complete Hausa Novel 1,247 words 0 views Progress saved
Download Book

kudi dubu biyar yace gashi ki sa Kati bai San ko waya Bata da ita ba,Aslam ya kura musu Ido gashi Yana yiwa Sabeer masifa muje dalla malam Siyama kin karbar kudin tayi Affan yace mene haka Kuma bana so nayi kyauta a maida min,Siyama juyawa tayi Kawai ta Shige gida duk ta firgice ta tsorata, Affan baki ya tabe yaja motarsa ya wuce,Aslam tuni sun tafi. Siyama tana komawa gida tace kawu ya tafi Aunty na dawo Suka ce to sai bayan Isha Kya bamu labari tace to tare da fadawa dakinta ta kwanta akan katifarta ta fashe da kuka Wai Aslam ya ganta tana zance har da cewa na shiga Uku na shiga dubu tana rusa uban kuka Kamar wacce aka Mata mugun duka,Aunty ce taji kukanta ta fado dakin da gudu tana cewa me Zan gani Siyama lafiya? Saurayin ne yaci Miki mutunci ko me? Marinki yayi? Siyama tace shike nan tawa ta Kare na gama yawo ta sake sakin kuka tana shesheka tace Aslam ne Aslam,Aunty tace mutuwa yayi? Siyama tace Aunty Aslam Aunty wash...shike nan Aunty Aslam ya kamani ya ganni Ina zance Innalillahi, Subhannallahi,Ashahdu Allah ilaha illallah ta Dora Hannu aka tace Aslam kuru kuru ya ganni,Aunty Tsaki ta ja tace ke dalla rufe Mana baki mahaukaciya amma dai sonsa kike dama ko? Charity tace Mijin Nusaiban haba Aunty mijin kawata kuma abin kunya ne ai,Aunty tace to rufe Mana baki sakarya, Kawai ki Fara Mana kuka sabo da rashin aikin yi,Siyama tagumi ta zuba tana goge hawaye ta kasa tashi Sam sabo da jimami. Aslam kuwa suna tafiya Sabeer yace zamuje park din? da masifa ya furta ka kaini gida Malam Babu Maganar park din banza kaini gida gwara nayi tunani me kyau na huta,ka fasa zuw...bazan je ba karka dameni ya furta da masifa,Sabeer yace kaga nifa bani naje zance wajen Yarinyar Nan ba bare kace,to ni nace maka naji haushinta ne Ina ruwana ta kula maza dubu ma Ina ruwana,Sabeer dariya kawai yayi Yana tukinsa yace tana da saurayinta kana ganinsa dai sharr da shi gwara ka auri Nabeela, Allah ya kiyaye na auri sakin wawa Nima fa sakin wawan nayiwa wata nasan me tayiwa mijinta ya saketa ba duk bazawara ce ta kirki ba gwara wacce ma mijinta ya mutu amma Wanda ake sakowa na tsorata da su wa yasan me Suka aikata aka sake su,Sabeer yace wallahi akwai Wanda laifin mazajensu ne,Aslam yace ae naji naji bana so bata min ba ni da wata kafarta a gwame,nufinka idan ta sa min riga da wando haka Zan na ganin Ball leg dinta sun kantare,Sabeer dariya Kamar me yace yaushe kaga kafafunta maye yanzu har ka San tana da Ball leg? Kwarai kuwa ko zaka ce karya ne? Sabeer yace tabbas wlh ba musu lallai mutumin auren Nusaiba ya sake gogar dakai da ko kallon Mata baka yi,Aslam yace dan Allah ka kyaleni bana son surutun me gwamammiyar kafa dai bana Yi karka sake min zancenta ana Neman macen kirki kana kawo min bage,Sabeer yace sorry na Siyama yana dariya,ance maka son Siyama nake Yi wai nifa ban shirya aure ba ku sani ma ya furta Yana turo jajayen lips dinsa yace kaini wajen Mum ma gwara na ga uwata na huta da duk wata ya mace. Wajen Mum suka tafi can Suka zauna har dare Mum har ta Fara damun Aslam cewar ka Nemo Mata ta gari Aslam gashi ma Kai naga Kamar baka da niyya Wanda hakan hatsari ne ga duk namijin da ya taba aure bai dace ya zauna ba Mata ba ka dinga dubawa kaji,to Aslam yace kawai. Affan kuwa akan idon Raudat ya shigo da motarsa gidan tana tsaye ta juya baya ita da Landlady suna hira ya wuce da mota abinsa Yana yin parking ya fito Raudat tana kallon inda yake fitowa,part dinsa ya Shiga da sauri,Raudat ta sauke ajiyar zuciya ta Shige part dinta ita ma,ai tana Shiga ciki taji suna tafawa da Sayyeed suna magana Affan yace Kai Kuma wannan tarkacen flask din da tire Ina ka samo su? Sayyeed yace ai baka sani ba budurwa nayi Raudat ce ta dinga Miko min ta window ashe windown ku daya, Affan yayi dariya yace Kai dalla ba sonka takeyi ba mutunci ne da ita Haka take da kirki ita tana ma da mijinta matar wani ce aiki ya kawota weekend take komawa gidanta, Sayyeed ya zaci da gaske ne yace eyya na hakura gwara da ka fada min,ai Kuwa tana da kirki kalli girki ya shiga budewa Affan Yana kallo,yace ta hutar Dani dama da tunaninka na dawo na nema maka abinci,Raudat tana jinsu suka hau Hira Sayyeed har yayi wanka Affan yace ko zamu fasa gari ne?Raudat ta Riga su fitowa ta tsaya kamar zata Shiga motarta,Affan ya fito tare da Sayyeed,Affan yace Hajiya Aunty fita zakiyi ne? Tace ae Ina son fita amma bana son driving din na gaji,Affan yace muje to Mana na kaiki ni Naga yanda Kika karrama abokina na gode fa,Hmm ba komai cewar Raudat zata Shiga Bayan motar Affan yace shigo gaba Sayyeed sai ya Shiga baya shi,Sayyeed ya Bude baki matar wani Kuma Affan yace Kawai dai Sayyeed ya Shiga Bayan mota,Affan ya tashi mota Suka wuce Raudat bata San inda zata je ba,Affan yace Ina za a kaiki? tunawa tayi da wata kawarta da suke aiki waje daya wata Hafsat ta nuna Masa gidan har ya kaita kofar gidan Hafsa yace yaushe za a zo a daukeki? Raudat tace sai 10pm,Affan ya zaro Ido yace haka Kawai ki zauna a gidan wata matar tana da aure fa har goman dare ki takura musu idan mijinta Yana son yayi Yar harka fa gaskiya bai dace ba,Raudat tana dariya tace to karfe nawa Zaka dawo? Yace gaskiya 8pm Haba kina mace a dinga sakaki dake bazai yuwu ba,To sai ka dawo cewar Raudat yace yawwa 8pm ki shirya har ta juya yace Aunty ta juyo da sauri yace ba ruwanki da mijinta sawunki a likkafa ki dauke idonki dan mazan yanzu ba mutunci gare su ba wlh sai yace Yana sonki ato ki kula Kar azo kawa ta nada Miki duka a gidanta irinku Aunty sai kusa mijin wata ya kifa yaci ta ka,Dariya Raudat keyi yace gaskiya nake fada Miki ki Kama kanki ba ruwanki da mazan wasu,Raudat tace to sai dai ka dawo ta juya ta Shige tana dariya,Affan sai da ya daina ganinta sannan yace da Sayyeed Kai katon gardi dawo gaba Kuma wallahi karka sake muna kwance ko yatsanka ya taba min fatata nasan baka iya kwanciya ba na tsani jikin Namiji ya taba Ni da ace dai macece aha wannan is okay Sayyeed ya koma gaba yace nasan halinka ni a Palo ma Zan kwana Kuma kaji tsoron Allah kana kula matar wani,Affan yace ai mun Saba da ita, Sayyeed yace naga alama dalla karka Raina min hankali let's go,Suka tafi yawonsu. Tun kafin 8pm Suka koma gida da kayan ciye ciyensu ya bar Sayyeed ya sake zuba wankan 3qtr da riga me gajeren hannu farare ya tafi dakko Raudat,8pm dot yayi horn dit dit Raudat taji ta shirya tare da yiwa Hafsat Sallama,Hafsat ta rakota tare da mijinta har mota ta Mika

Table of Contents

Chapters

71 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71