Skip to content

Chapter 13

Chapter 13

AURENMU Book One Complete Hausa Novel 1,250 words 0 views Progress saved
Download Book

iya ci,hankalinsa a tashe Charity ta kula da Haka amma matar tasa Nusaiba bata ma gane shi ba Kawai a bata kudi ita Kam, Yana zaune a garden yayi tagumi Yana ta waya Charity taje har Inda yake,sai da ya Gama Wayar tace sir Ina da Yar tambaya ne,yace go ahead Ina jinki,Nusaiba ce tazo wajen sanye cikin bum short da Yar wata t-shirt yace amma kin San me gadi zai iya ganinki da wannan shigar ko? Nusaiba tace naji tana tabe baki,Charity tace Naga kwana biyu kullum cikin damuwa kake ko abinci baka ci,Nusaiba tayiwa Charity wani banzan kallo up and down tace ke a wa Kuma da wannan tambayar,Aslam bai kula Nusaiba ba yace matsala na samu da kayan Dana shigo dasu gashi bashin bank na karba Kuma kayan sun salwanta ba ma custum ne Suka Kama ba jirgin ruwa ne yayi hatsari Suka nitse,yanzu komai nawa banki ne zasu karbe har gidan da nake ciki motocina da komai Ina Miki zancen yanzu Banda komai nan da sati ma bank zasu zo sabo da dana karba wata Daya nace Zan maida kudin kin San Kuma bashin banki,Innalillahi wa Innailayhirraju'un cewar Siyama tace kayi ganganci kaima daka karbi bashin bank gaba Daya ka tura aka turo da Kaya da kudin,yace duk kadarar da na mallaka Ina fada Miki baza ta biya bashin bank din ba,Wata shewa Nusaiba tayi tace wa zaka rainawa hankali Kawai kace akan jiya nace ka bani dubu dari Zan canja waya sabo da mammako baza ka iya bani ba shi yasa ka kirkiri karya Wai kayanka sun nutse a ruwa just like that,heee Aslam tsabar son kudi ne yasa sai ka min karya Allah ya kyauta idan ba karya kake ba to tabbas kazo gidanmu da karya Ashe motoci da kudin daka nuna Mana ashe duk na karya ne dama ance samarin yanzu aron mota da gida suke bayan kwana biyu su karanta maka matsala shike nan ka shiga talauci tana Gama fada ta juya ta koma ciki abinta,shi ta daina daga Masa hankali ma ba ta ita yake ba yanzu ta kudinsa yake Yi,Ya kalli Siyama da damuwa yace baza ki gane ba Siyama amma Dan kasuwa shi Ina karanta Masa zai Gane,Siyama tace na fahimta ma wlh ubangiji Allah ya mayar maka da mafi Alkhairi Allah yasa ka samu Wanda Suka fi Wanda kayi asara Allah Kuma ya Kare gaba wlh da ace Ina da kudi da na taimaka nima,kallonta yayi yace karki damu na gode A ranar ya sallami me gadi yace Isa baka min komai ba ga salary dinka na wata biyu ka tafi gida Zan nemeka,Isa yace Sir fatan ba wani laifi nayi ba dan Allah karka kore ni yace ba laifin komai idan na samu yanda nake so Zan kiraka a waya,Isa ba a son ransa ba ya tafi,ya Kira Daya me aikin itama Bara'atu ya sallameta yace nan gaba zai kirata itama tana takaici ta tafi. Washe gari Siyama ya samu tana girki ya Bata dubu sittin cash yace gashi na wannan watan da watan gaba kije gida domin nan da sati ma'aikatan banki zasu iya zuwa su kore mu daga gidan Nan,Charity tace bazan karbi ko kwandala ba Sir na bar maka ka rike Kuma bazan bar gidan Nan ba sai ranar da Yan bank Suka zo Zan biku naga gidan da kace zaka Kama haya idan naga gidan sai na koma gida Zan dinga zuwa lokaci lokaci Ina dubaku kayi hakuri da kawata kaddara ce da Jarabawar rayuwa ka Zama me tawakali kasa Allah a ranka Inshaallah shi zai taimakeka,Murmushi yayi cikin dacin zuciya yace ba damuwa,Mamansa ya Kira a waya itama da kudinsa take gadara duk da cewa a wajen Yayarta take zaune a turai,Zuciyar Mum dinsa ta kusa bugawa da taji irin bala'in daya tunkaro danta musamman da ya fada Mata halin Nusaiba abinda take Masa,itama Mum hakuri take bashi akan halin Mata tace sai yayi hakuri dole,tana so ta taho Nigeria yace Kar tazo idan tazo ma wahala zata Sha gwara tayi zamanta Kawai ta tayashi da Addua,Mum har kuka tayi danta ya samu karayar arziki taje tana bawa Yar uwarta labari. Tun daga Sanda Nusaiba ta tabbatar Aslam ya talauce kudinta na accnt da shi take kwasa ta fita yawon shakatawarta ya sallami driver dinsa ma duk da cewar ma'aikatan bank din Basu zo ba tukun a taxi take fita tunda bata iya mota ba,Siyama ce ke Masa girki,yau ma tun safe bai karya ba ya fita akan matsalar data fada masa. Sai Yamma baici komai ba ya dawo ya iske Siyama tana Shirya Dining sallama yayi ta amsa tare da furta Sannu da zuwa,Nusaiba fa? Ya tambaya tace bacci takeyi Kai ya jinjina ko a jikinta ita, wanka yayi ya canja kaya wani yard hadadde ya fito da takardu zai sake fita Siyama tace dan Allah ka tsaya kaci abinci tukun,wa ya bani lokacin cin abinci ya furta,tace ka dai Yi hakuri ka dauki komai a nutse,Dining din ya karasa ya zauna Yana Kiran Abokinsa Sabeer Wanda tunda matsalar ta faru tare suke shige da ficensu,Jullof rice ta zuba Masa taji Hadi sai dai ba nama tace Naman fridge din ya Kare jiya Nusaiba ta kwashe ta soyesu duka suna dakinta a soye,yace kyaleta ya fara cin abincin yaji ba nama amma yayi mugun dadi yace Wai ke da Nusaiba waye ya girmi wani ne? Dariya Charity tayi tace Santi ne ko me? Yace na Dade Ina so na tambaya sai na manta yau dai na tuna,Na girmeta Mana ai Nusaiba bama sa'a ta bace Kawai dai school ne ya hadamu kasan makaranta ba lallai ace shekarunku Daya ba ni na girmeta da wurin shekaru uku Yayarta ce ni Charity Allah yayota da son girma Yan watanni ta bawa Nusaiba amma sai tayi ta cewa shekaru ta bawa Nusaiba,Nusaiba ce ta fito ita ba alamar Wasa a fuskarta tace to munafuka na hakura da aikinki ki tattara kayanki ki tafi gidan ubanki,sai wani shishigewa mijina kike Yi karuwa,Charity tace Ina zani ba inda Zan tafi Zama daram,gidanki ne Naga nina kawoki ko,to bazan tafi ba cewar Siyama har ya gama cin abinci suna fada ya mike ya fice,Yana barin gidan Nusaiba ta Kira wani mutum tace ya fita kazo ka dauki motar,Wanda ta Kira bai Dade ba yazo ya shiga katuwar motar Aslam me tsada ya fita da motar,Hijab ta saka tabi Wanda ya dauki motar,wurin siyar da motoci Suka karasa aka Yi cikin mota Wanda ya siya yace ki dawo gobe ki karbi kudi tace to ta tsaya a gefen titi zata shiga mota sai ga wani matashi a dankareriyar mota da alama Yana da kudi yace ranki ya dade barka da Yamma,Nusaiba ta kalleshi ta ja tsaki,yace Dan Allah idan baza ki damu ba ki shigo na rage Miki Hanya,Bata kulashi ba sai da ya fito daga motar wani baki ne Dan mummuna da shi yaci gayu Yana kamshi yace dan Allah ki shiga na rage Miki Hanya sai muyi magana,motar ta bude tare da shigewa Gaban motar ta zauna ya shiga shima yace ko na kaiki wurin cin abinci zamu fi sakewa a nan,tace to ya ja mota zuwa wani hadadden Joint Suka zauna yasa aka kawo Mata

Table of Contents

Chapters

71 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71