Chapter 59
Chapter 59
suna nishadi kamar saurayi da budurwa ka gansu gwanin birgewa,Suna ta nishadi yana tsokanarta,wata Yar budurwa ce tazo wucewa Raudah da sauri ta koma ta bayansa tare da rufe Masa idanu da tafukan hannayenta dariya sukeyi musamman Affan, sai wurin magriba Suka dawo gida. Siyama kwance suke da Aslam a makeken bed dinsu sun gama soyewa suna hutawa ta juya tare da hugging din Aslam tace My Sugar dan Allah ka biya min makaranta na koma Nima nayi karatu,marairaicewa tayi da shagwaba please ko ba degree ba ko NCE ne dan Allah kaji, Aslam yace ni bana son fitarki aje a gurbata min Mata Muna zaman mu lafiya,Siyama tace Ina da hankali fa Inshaallah babu abinda zai faru wace ma ta Isa ta zuga ni na yarda ilimi Yana da dadi kaga Zan sake wayewa sex dinnan ma Sai kaga albarkacin makaranta da gogewa nazo Ina maka style har na tintsira gudi gudi,dariya Affan yayi ba shiri yace ba wayon da Zaki min Yar nan,Siyama ta sake cewa to yaran mu fa ko Dan yaranmu da zamu haifa zai musu Rana,Yan dagwai dagwai dinmu jikokin Mum, Yan fararen yaranmu masu Yan kunnuwa Affan yace naji amma sai kin samu ciki Zaki fara yarona tun a ciki ya dinga Jin turanci,Siyama tace Indai ciki ne Ina da shi fa,watanmu biyar da aure Ina da ciki,Aslam yace haka ake cikin,da gaske fa nake idan baka yarda ba muje asibiti gobe,ta ya Kika sani? tace Sanda na dinga zazzabi rannan na siyo wannan tsinken na pt na gwada Allah ya nuna Ina da ciki,shine baki fada min ba? gobe Zan kaiki asibiti ai,gari na wayewa Suka shirya sai asibiti bayan an Mata gwaji nagartacce aka tabbatar tana da ciki na wata uku dai dai,Aslam sai Murna harda kissing dinta a kumatu Suka dawo gida murna taki karewa,Siyama tace ai mu irin jinin haihuwa ne ana taba mu muke samun ciki,dariya yayi sai Murna yake zubawa daga nan ya Fara musu Shirin barin kasar. Su kawu,Aunty da Shehu sai Wanda Affan yasa zai rakasu ko Ina suna filin jirgi,Landlady ma tazo zata tafi Umrah tana filin jirgi a nan Suka hadu da su Shehu,Shehu yaga dai dai shi yaji Landlady ta masa harda cewa sannu,tace yawwa sannunku,sai ga Shehu ya zage Yana yiwa Landlady tambayoyi kema Makkah Zaki? tace ae Umrah zanyi yace ke Kuwa ki karasa ladanki Mana kiyi aikin hajjin gaba daya amma kiyi Umrah Kawai ki dawo sabo da rashin rabo,Landlady tayi Murmushi bai san me kudi bace,Shehu ya zake suna ta hira da Landlady,Shehu harda cewa daga nan mu Paris zamu wuce sai Dubai, Landlady ta zaro Ido ta zaci wani shegen me kudi ne Shehu ta saki jiki harda bawa Shehu labarinta kaf amma bata nuna Masa me kudi bace, tun a nan Suka kulla soyayyarsu in sun dawo zasu Yi aure, Landlady a ranta tace gwara ko talaka ne Indai na samu me so na Nima nayi auren nan na huta kullum sai dai na rungumi pillow na gaji,Shehu Yana ta murna ya samu matar aure shi kam. AsmaBaffa [4/1, 5:47 AM] Sis Asma: 🛢️AUREN MU🛢️ 91-95 Official By AsmaBaffa Page naki ne Bk Affan yau zai koma aikinsa cikin shiri ya fito tare da Raudah tana shagwaba ta rakashi har mota tana kumburo baki irin na Yan Shagwabar nan da sangarta,Affan ya zaro kudi Yan dubu dubu na dubu goma ya Mika Mata ta karba tana cewa na mene? yace baki nayi ki kashe,duk da tana da kudi bata da wata matsala sai da taji dadi yace sabo da wasu mazan tunaninsu Kawai ci da Sha zasu bawa mace basu iya bawa mace dan kudi ko Yaya ne gwargwadon samunsa Watarana haka sabo da ba iya abinci da sutura bane matsalarta,in ka bata kudi maybe a danginta akwai Wanda take so ta yiwa kyauta ko ta kyautatawa kawaye ko Yan Uwa bare uwa uba iyayenta kuma,zata kyautata muamularta da Yan Uwa da abokan arziki amma mazan da yawa basa ganewa, Raudah tana shagwaba tace to ai Ina da kudi Kuma ma Ni ka dawo da wuri yafi min muhimmanci,nasan kina da su ai amma kudinki daban nawa daban wannan naki ne kiyi abinda Kika ga dama da abinki, tace to na gode Allah ya Kara budi yasa kafi haka,karfe nawa zaka dawo? 5pm ya furta Yana kallonta,dire diren kafafu ta fara tana kukan tabara yayi nisa gaskiya ni ka rage, kina aiki fa My life kin San Kuma ka'ida kiyi hakuri tare fa muke bacci kin San da Ina gida ba aiki dole Ina gida, Alright ta furta Allah ya tsare a nemo mana halali Banda haram, Inshaallah ya furta Yana cewa am gonna miss you,me too yace come here..dan kanta ta shigar cikin motar yayi kissing dinta tace ko na zo nayi driving naka? Kina amaryar Zan bar matata ta fita, dariya Suka Yi tare da dagawa juna Hannu ta Masa bye sannan ya tashi motarsa tare da barin gidan,bayan yaje Office ya kirata yafi sau biyar, sai Yamma ta sake gyara gidan tasan bai son kazanta ko ya take, girki ta shirya Masa lafiyayye ta cakare tana zumudin ganin angonta. Siyama Kamar bata da ciki ana gobe Mum zata tafi tazo gidan Aslam,Siyama tana sama taji door bell da sauri ta fito,sanye take cikin wasu Pakistan masu kyau Riga da wando da mayafinsu farare tas sunji adon golden,Wandon me Kama da skert ne idan baka sani ba zaka rantse skert ne,dankwalin daurawa tayi a kanta amma Jin muryar Mum sai ta Yafa mayafin sannan tazo tare da bude kofar, fara'arta ta fadada tace Sannu da zuwa Mum tana Jin kunya kunya Mum ta shigo ta zauna kujera ta zuba lace me tsada, Siyama a kasa ta durkusa tare gaida Mum cike da girgimawa ko itace ta haife ta sai haka,ta mike ta cikawa Mum gabanta da kayan ci da Sha, Mum sai Murna da farin ciki danta yayi dace tace oh bakya gajiya Yar nan da hidima Allah dai yayi muku Albarka,Siyama ta amsa da Ameen tana zubawa Mum lemon a cup ta Mika Mata sannan tace bari na Masa magana ta haura sama da sauri,Mum tana ta washe baki Sabo da farin ciki,Siyama tana Shiga ta Samu Aslam yana aiki a system daga shi sai boxers,bayansa ta zaga ta duka tare da rungume shi ta baya hannayenta ta sarkafo ta wuyansa ta Masa rada a kunne Mum tana nan fa tazo tana Palo ka tashi ko nace ta shigo Nan? Ko kince ta shigo ai baza ta shugo turakata ba,to tashi tana jira fa dan Allah,yace wannan rawar kafa da kike Yi haka ko Ni bakya min haka ni ya kamata ma na Fara kishi da Mum kinfi sonta da ni,Mikewa tayi tace to ita ta haifa min Kai ai da bata haifa ba na Samu,Jallabiya ta dakko Masa ya saka sannan yace muje,tace kaje Kai kunya nake ji ta ganmu tare,bana son gulma sau nawa Muka je wajenta tare,Ni dai kaje tace,baki ya tabe ya fice ya samu Mum tana eban gara,Mum baki ta bude ta kasa rufewa tace me Zan gani haka Aslam wato sumarka da kake tarawa me shegen yawa bata Isa ba shine kaje aka zana maka kitso a kanka
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71