Chapter 53
Chapter 53
shi mamaki take bashi yanda taci kuka,kamar bazai hakura ba yace tashi na hakura ni ki daina durkusa min haka,na hakura ya zanyi Dake tunda Ina sonki na fada Miki bana son kishin zargi idan kishi yayi yawa zargi yake sawa idan nayi niyyar kula wata har zan bari ma ki gane kin San maza kuwa,bana son zargi a rayuwata bana so karki sake min irin haka,Raudah da tana ganin Affan Kamar sai yanda tayi da shi sai taga ashe ba haka yake ba baya takuwa ko kadan Namiji ne bai son raini,tuni ta Shiga hankalinta,yace kije kiyi bacci,ta mike sum sum har ta fita ta dawo tace baka ce kana so na ba,bazan fada ba yau Banga dama ba ya furta Yana hararta,tace to ni Ina sonka yace can da yawarki,tafiya tayi dai zuciyarta ba dadi da safe bata je aiki ba Monday guda Affan bai ce Yana sonta ba tana nan tana bacin rai, Tuesday ma kin zuwa tayi tace bata da lafiya sai ta warke,Affan yaga motarta kwana biyu ba inda ta fita ko a compound basu hadu ba Kuma ko ta window bai leka ba bata leko ba zai shiga mota ya fasa yazo yayi knocking door nata ta bude ya ganta ras da ita taci kwalliya,tace Ina kwana lfy Alhmdllh kwana biyu bakya fita lafiya? Kai nake jira kace kana so na sai na fita,Affan Ido ya zaro yace kina da abin mamaki Raudah....kuka ta saki kaji ko kaji ko Beb dinma ka daina fada sai Raudah,Murmushi yayi Yana kallon ikon Allah,yace sai ance ana sonki dole shine Kika San ana sonki? tace ae ni Indai ana so na Kuma ana son zaman lafiya kullum sai ance min I love you morning, afternoon and night,I love you ya furta tace naji na yanzu Saura bashin na jiya sai da ya fada yafi sau biyar sannan tace yayi haka a dawo lafiya,ya tafi Yana dariyar Raudah. Siyama ce ta zuba wani abinci zata ci Aslam yace yayi kadan ki Karo a gidanku ba haka kike ci ba,tana shagwaba tace ai tunkafin ayi min aure Sam bana iya cin abinci bana son ci ma dole nake yiwa kaina Aslam a ransa yace to ga Kawu yace idan yaga ta rame akwai matsa dole na samo Mata multivitamin,tashi yayi yace da kin fada min tuntuni ai da na samo Miki maganin cin abinci ki dawo normal haka akeyi,Bari naje chemist tace to,yaje chemist din layin yace Multivitamin zaka bani maganin cin abinci babba,me chemist yace Kaine baka iya cin abinci? Yace ae me chemist shi ba likita bane Yar makarantar ma school of health technology ya Fara aka kore shi ai Kuwa ya dauki me karfi maganin boosting din apetite da Kuma multivitamin ya bashi me kyau me karfi yazo ya ebo ruwa ya balla ya bata ta Sha ashe muguwar yunwa yake sawa tare da shegen bacci,Minti talatin ta shafa cikinta tace ji nake Kamar an sace min kayan cikina Honey wayam ba komai,abincinsa da bai ci ba yace sai anjima ta dauke ta cinye tas,tana ci wani mugun bacci ya kamata ta mike tsam ta tafi bedroom dinsa ta kwanta bacci take ba ji ba gani har dare bata tashi ba,zuwa yayi Yana tashinta yace wannan wanne irin bacci ne magriba ta wuce fa har na dawo daga masallaci Daukanta yayi tare da direta a kasa tana tangadi ta shiga toilet da kyar tayi Alwala da Sallah a wajen ta kwanta sai bacci Aslam yaji gidan ba dadi abokiyar tasa tana ta bacci Sallar Isha ma da kyar ta iya tashi ga jikinta ya mutu,Har 11pm tana bacci Aslam sai me aiki ya sa ta Masa girki, yayi wanka tare da Shirin bacci yazo Kawai ya dakko rigar bacci wata sabuwa ya cire Mata kayan jikinta garin cire kayan bacci sha'awarsa ta motsa ya fasa sa Mata kayan yaja ta suka Shige bargo tare zaiyi shagali tana ta faman bacci jiki a mace Yana Fara taba ta sai dai ta bige hannunsa tace ni bana so wlh ka kyaleni bacci,Aslam takaicin magani yasa ya kwashe su tare da watsa su a dustbin yace baza a sake shansa ba haka Kawai ya jawo min tsiya Magani dai sai da safe ya saki Siyama da safen ma ba sosai ba,zata tafi kitchen ya riketa yace kalli hannuna yanda ya dawo red sabo da dukanki,dariya tayi tace maganin nan ne gaskiya,Nima Naga alama tace baccin Dadi a Kara min,yace na zubar da dan Iska jiya ya hanani Jin dadi sai hakura nayi amma yanzu ba fashi Siyama tace ai banci abinci ba yunwa nakeji yace to gama aikin ,ta fita ya koma baccinsa,tana kitchen din amma ciye ciyenta takeyi tun kafin ta gama Kamar zata cinye abincin gidan,tana gama soye soyenta ta zauna ta karya ko jiransa baza ta iya ba sai data gama ta koma bedroom dinta wanka tayi ta shirya cikin Dan Bum short black sai wata rigarsa silk white da digo digon baki me dogon hannu ce da kwala,pcap ta saka me black da adon fari,gashinta kwance a baya tayi bala'in kyau,ta fito daga room dinta sai gashi ya fito sanye cikin Jallabiya arsh Yana kamshi, ka tashi har kayi wanka ashe,Yana can Yana aikin kallonta bai ji me tace ba sai da tace hello sannan ya dawo hayyacinsa,tace ka tsaya kana ta kallona,kinyi kyau da yawa ne shi yasa,jawota yayi jikinsa Yana shakar kamshinta Bayan ya karya ya dauketa sai dakinsa domin bazai iya hakuri ba a matse yake,Haka ya soye ya barta da jinya. Amarci suke Sha Kamar ba gobe zuwa wata uku Siyama ta murza kiba tayi wani kyau da haske kana ganinta kasan tana hutawa hankalinta a kwance yake,lokacin tace zata je gida ta gaida su Kawu,Ranar wata Sunday Suka shirya cikin sutura me tsada sunyi kyau matuka Suka fito Yana kallonta yace dole Kawu yace na iya kiwo ya bude Mata mota ta shiga sannan ya zaga ya Shiga yayi driving din su zuwa gidan su Siyama,Yana yin parking ya fito kenan ya Bude mata kofa ta fito sai ga Nusaiba ta dawo daga shago hannunta rike da leda ta siyo manja bai fi na dari ba,ta rame tayi baki sai kallon Siyama takeyi da Aslam tana zare Ido,Aslam ko kallonta baiyi ba,Nusaiba kishin Siyama take yi Bata kulata ba,Siyama ce tace Yar budurwar bazawara daga Ina,Nusaiba Tsaki ta ja tayi gaba fuuu,dariya ta bawa Siyama tace Nusaiba kawarki ce Charity fa Nusaiba ko kulasu bata Yi ba ta fada gidansu tana kuka a gaban Mama,Mama tace wanne Iskanci ne wannan wallahi Kika fasa manjan nan sai dai kuci shinkafa da waken nan babu mai wallahi kudin cefanen da ubanku ya bayar na dauke dari biyar na zuba a dashi dama da irin wannan Yar cuwa cuwar muke yin dan adashin nan namu,Nusaiba tana hawaye tace ni gwara Ina gidan mijina ko gidan Sufyan ne ya fiye min,Mama tace ki Bari kiyi idda Inshaallah hannun Aslam ma zaki koma,ai na kusa iddar Ina sane dake akwai abinda zanyi karki damu yarinya,Nusaiba sai lokacin ta danyi murmushi. Aslam kuwa gidan Kawu Suka shiga Aunty sai Murna Siyama tayi kiba an Kara kyau alamar kana gani kasan tana cikin kwanciyar hankali,Kawu ne ya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71