Chapter 52
Chapter 52
tayi kyau gata da hips,Raudah baki ta bude tana kallo shi bai kula bama Signing ya Mata tare da Mika Mata ta karba ta dauki Hanya zata fita tabi ta gefen Raudah,da yatsa Raudah ta dan taba Duwawun matar, Affan yace mene Haka beb? Tace wannan wace? Yace Secretariat ta ce,tace kana nufin kullum sai kaga wannan? Yace mene ne Wai? Baza ka kawo Namiji ba sai mace to duwawunta kake kallo ko me,kalli fa duwawunta kullum da safe sai ka ganta Ina can na saki baki hai a bude Saurayina yana nan yana kallon duwawun Chinaza,wlh Affan idan ka kalli duwawunta bazan yafe ba,Affan yace Wai in tambayeki baki yarda dani ba,haba Raudah kishin nan naki yayi sau nawa zan fada Miki ke kadai nake da ita,bazan iya cin amanarki ba,I will never ever cheat on you Karki bari muyi auren zargi so kike kishi ya halakar dake,Ni wlh Kawai ka canja sakatariya zuwa sakatare Namiji gaskiya ban yarda ba,yace ba laifin data min baki Isa kisa na sallameta ba Kuma bani na kawota ba Liman ne ai kin san gidansa tunda munje tare kin gaishe shi je ki fada Masa ya canja ta Indai kin San haka zaki to karki sake zuwa Office Dina ya mike tare da dukan table sai data tsorata yace tashi ki tafi gida bana son zargi bana taba ko hannun mace akan kishin banza kizo ki sani gaba ki hanani sakewa ba ke kadai kike da saurayi ba sannan idan niyyar cutarki nayi ta ya Zan Bari ki gane, tashi ki tafi bazan cuceki ba Ina sonki babu wacce nake so sai ke bana ko budurwa bare neman Mata bana son zargi,Raudah mikewa tayi ta Fara hawaye yace oh my God me na miki? tace ni dai karka kalli duwawunta,yace to naji bazan kalla ba idona ma Zan rufe muje na rakaki mota a haka ya lallaba Raudah ta koma gida. Tunda ta koma gida part din Landlady ta shiga suna Hira tace karki yarda da Maza Yar uwa maciya amana ne duk yanda kike da kyau sai sun kula Mata,ki kula da Affan sosai yanda yake da kyau Mata bibiyarsa suke kisa Ido akansa idan ba Haka ba wata ta kwace Miki shi,Landlady ta dinga zuga Raudah,Raudah har da bata labarin sakatariya,tace to ki shiga ki fita a sallameta a canja masa Namiji ko mace me addini, Raudah ta Fara tunanin ya zata yi ai da yamma ta shirya sai gidan Liman Bayan taje sun gaisa da Liman tace Liman wata barna na hango a matsayinka na Malami bai kamata ace an hada mace da namiji suna kebewa ba da sunan aiki Wai sakatariya me yasa baza a Kai Namiji ba duk sakatariya sai ace dole sai mace,Liman ya kalleta yace ai an fi son mace sabo da ita zata iya Zama ko hour nawa ne sabanin Namiji sannan yare sunfi Hausawa kwazo a wajen aiki,amma tunda Naga Kamar kina da manufa kema bari Zan samu mace me addini me saka hijab kullum me zikiri a Kai Masa ita,Raudah taji sanyi a ranta ta zube kasa tana ta godiya. Washe gari Liman ya canjawa Chinaza Wurin aiki ya kaita wajen Daya manager din nasa Affan kuma sai gani yayi an turo mace wata baka amma tana da kyau ba laifi hijab dinta har kasa,ga safa hannu da kafa,suna gaisawa ta saka Nikaf dinta tana magana tana Jan carbi, Affan Yana kallonta tana motsa baki tana cewa Lailahaillah Lailahaillah tana ta fama. Bayan kwana Daya Suka Fara aiki kullum tana aikin Jan carbi idan ta kama ma a Office dinta mikewa take tsaye ta Fara dukan kirji tana zikiri Kamar zaka kashe kanta,Affan har ya gaji da halinta ta cika musu kunne da dukan kirki tana Abu daya tana faman cewa Sayyadina muhammadu ka kula dani Allah...Allah...Allah tana dukan kirji, ta manta ma Affan aikenta yayi ta dakko Masa file sai da ya gaji ya taho da Kansa ya isketa tana ta dukan kirjinta tsawa ya buga Mata tana Adduar bata daina ba tace Sir Allah ya maka gida me kallon bangon gabas,Allah ya baka mace me zikiri....tsawa ya Mata shut up Ina file din da nace ki dakko? tace Sayyadina manzo na shi zai agaza min na ganshi, Assalamualaika ya rasulillah.... Affan yana masifa yace ke lokacin Addua daban lokacin aiki daban,Rabbana.....Rabbana...taci gaba,Affan ya zaro Ido yace ke tafi gidanku na koreki you are fired,zata roke shi ya daka Mata wata uwar tsawa wacce tasa ta fice da gudu,nan take ya Kira Liman ya sanar Masa komai Liman ya canja masa wata macen arniya ce amma Kamar musulma haka take shigarta bata dame jikinta Kuma nutsasiya ce sai dai ita Kuma akwai bin maza Kamar karya haka take in Banda son maza babu abinda ta sani, Raudah tana bala'in sawa Affan Ido akan Shige da ficensa Yau Saturday tana gida amma shi har Saturday Yana zuwa aiki,ya bawa Raudah key din part dinsa zata gyara Masa,tana cikin palon Affan ta gama gyara dakin tana kwance a kujera sai taji knocking tana budewa taga wani Matashin yaro da wata jaka me kyau yace gashi Wai a bawa me gidan inji Farha, Raudah ta karba ta rufe kofar, budewa tayi taga wata flower ta soyayya tana zuba kamshi ga wani agogo na musamman me tsada,ga wani turare kala biyu,bakin ciki ya cikawa Raudah zuciya ta dauki turarukan ta fice can baya tasa dutse ta ragargaje su,ta dawo ta dauki agogon ma ta fita tasa dutse tare da farfasa shi,ta dawo ta jefar da ledar da kafa ta dinga tattake su sai ga Affan ya dawo ya sameta a haka Yana Tambayarta Lafiya? tace Affan wace ta kawo maka gift Affan so kake hawan jini ya kashe ni,taya zaka dinga kula wasu gashi har gift ake kawo maka, Knocking aka musu tare da turo kofar aka shigo Wanda ya kawo gift dinne ya dawo yace dama wannan sakon na dawo karba ashe ba nan tace na kawo ba gaban gidan nan ta aikeni wajen saurayinta nayi mistake,Surrender Raudah tayi kunya ta kamata ta kasa ko motsi har yaron yaga sauran ledar sa flower watse a kasa,Kawai juyawa yayi tare da ficewa, Affan ransa ya baci shima kasa Mata magana yayi ya juya ya fice abinsa ya shiga mota ya bar gidan ya bar Raudah tayi mutuwar zaune tana hawayen bakin cikin halinta na kishi da dana sani,tana so ta daina kishin ta kasa,ga Affan yayi fushi tace Ina Zan sa kaina ta dafe Kai tana hawaye ta jawo Wayarta ta Fara kiransa yaki dagawa,bugun duniya yaki daga Wayar tata tana zaune a part dinsa har 11am bai dawo gida ba gashi idan ta Kira sai ya kashe wayar ma gaba daya, a ranta tayi alkwarin ta daina wannan kishin nata,ga Affan yaki dawowa. AsmaBaffa [4/1, 5:47 AM] Sis Asma: 🛢️AUREN MU🛢️ 81-85 Official By AsmaBaffa Page naki ne FUTURE RM Kuka Raudah ke yi yaki daga Wayarta Yana can wajen abokansa sai kusan 12 na dare ya dawo Yana bude kofarsa ya ganta a palonsa,tana ganinsa ta mike tsaye yazo zai wuce ransa a bace ta zube har kasa ta durkusa tana hawaye tace dan Allah kayi hakuri ka yafe min na tuba,Affan ya kalleta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71