Chapter 61
Chapter 61
zubar da jini mijin bai samu damar saduwa da ita ba suna ta fama su kadai. Kawu da Shehu watansu kusan biyu a kasar waje ana kaisu yawan bude Ido Suka koma Saudiya a karshe Suka sauke farali can suka hadu da Aslam da Siyama, daga nan gida Suka dawo Suka bar su Aslam a can,Shehu yayi bulbul yayi kyan gani gashi suna ta waya da Landlady ita ta Dade da dawowa Nigeria sun gama shirya aurensu ,sai daga baya yaji ma ashe tana da kudi Shehu bayan sun huta da sati biyu ya samu Mama cikin dare suna kwance ya tashe ta yace tashi zamuyi wata magana,Mama ta mike tana Jan tsaki wacce magana ce wannan sai cikin dare mutum yana baccinsa Fadi ni naji mene? yace dama fada Miki zanyi Zan Kara aure wani watan idan Allah ya kaimu za a daura min aure,ban gane ba wanne aure? Wanda Kika sani dai shi Zan Kara ma'ana Zan Kara Mata ku Zama ku biyu,banyi dan naci zarafinki ba,ahayye eheheheeeeee heeeeeeyy Mama tayi shewa tace dama ka dade kana cin amanata ban sani ba kwarto a wanne dakin zaka sakata daki uku ne daki daya namu daki daya na Mata daki daya na maza to Ina waje? Shehu yace Aslam ne zai min auren nan fa kwandala bazan kashe ba shine zai min komai yace, yace idan so nake ma zai bani gida na saka Amarya,nace a'a gwara na hada Kan Yara na gida na Zan kawo ta tunda gidan zaiyi part guda yace zai gina min part daban a cikin gidan nan a wancen part din dana katange ban gina ba,Mama ta fashe da kuka da ihu cikin dare tace amma Allah ya tsinewa Aslam Albarka bazai ga annabi ba,Su Nusaiba sunji ihun Mama Suka firfito,Mama cikin tsakar daren ta fito tsakiyar unguwa tana zunduma ihu da kuruwa sai da makwafta suka fito Shehu yace kowa ya koma gidansa akan Zan Kara aure take wannan haukan,aka dinga tir da halin Mama,da kyar su Nusaiba Suka lallabo ta ta dawo gida tace wallahi yau bazan kwana a daki ba a tsakar gida Zan kwana tun suna lallashi har Suka gaji Suka koma daki ita Kuma Mama a tsaye gari ya waye Mata tana faman zunduma ihu,Shehu bakin ciki Kamar ya kashe shi ta gama tozarta shi,Kamar Wasa da safe sai ga motar yashi tana ta saukewa a kofar gidan Shehu aikin Aslam ne,Mama tace Nusaiba ku fita ku barbaje yashin nan a kasa duk ku tirje shi,sauran yaran Suka ki zuwa Nusaiba ce take taya uwarta kishi ta fito Kamar sabon kamu tana eban yashin tana watsarwa a cikin kwata,Allah ya kawo Shehu ya kamata ya nada Mata shegen duka Kamar zata mutu,Shehu Yana shiga gida Mama taci kwalar Shehu tace idan kayi min kishiya shegiya nake algungumi azzalumi Allah ya isa shine ka samo me kudi zaka auro bazan yafe ba sabo da mu talakawa ne wallahi sai ka sake ni ka sakeni,a gaban yaranta tayiwa Shehu haka Shehu hannunta ya cire daga jikinsa ta karfi yace ki tafi gidan ubanki na sake ki saki daya,Mama Hannu ta daura a Kai tana ihu shine ka sakeni Allah ya Isa kuka take ta tattara nata ya nata cikin fushi ta tasa keyar Nusaiba kadai Suka tafi Kauye garin su Mama su biyu,shi kuwa Shehu yace Allah raka taki gona aka ci gaba da gini. Aslam tsabar muguntarsa ya samu part din Amarya aka kera shi Kamar gidan wani hamshakin me kudi 3room and Palo aka Mata sai kitchen dinta da komai,babu inda za ayi gate wani makwafcin Shehu zai tashi daga unguwar yayi sabon gida Aslam ya siyawa Shehu gidan aka bajeshi tare da hade shi a bangaren Amarya aka mata gate me cin mota biyu abinta ko Ina yasha tiles da Interlock kyau Kam ba a magana gidan ya keru,ita Kuwa bangaren Mama Yana nan sai paint aka mata Kawai shi ma me paint ne yaji kansu ya musu komai siminti ne,Mama Kuwa da Nusaiba tunda Suka koma Kauye garau garau ma da kyar suke samu ga kazanta,daga dankali sai kunu sai tuwo,dambu,danwake shima kadan ake basu,Basu taba sanin da a Rahma suke ba sai da Suka zo Kauye ashe a gidan Shehu ba karamin dadi suke ji ba,sun rame sunyi baki,tsakanin Nusaiba da Mama sai fada suke Yi babu mutunci a tsakaninsu Yau suna zaune a wani dakin kasa Wanda shine makwancinsu sai tabarma wata yarinya ce ta shigo ta ajiye musu kunu a wani dan karamin kofi Wai shine abincin ranansu ai Nusaiba tace wallahi duk da bani da kudin mota gida zan koma wajen mahaifina,Mama ashariya ta dannawa Nusaiba tace sai kin dawo marar mutunci marar biyayya ga uwarta,tace ae naji tafiya zanyi wallahi yau bazan kwana a garin nan ba,Fitowa tayi ta shiga dakin wata tsohuwa a gidan me siyar da daddawar miya,Nusaiba tasan inda matar ke Adana kudinta sai ta dinga Jan Me daddawa da surutu suna ta hira har lokacin Sallah yayi tsohuwar ta mike ta fice zata Yi Alwala tana shiga bandaki Nusaiba ta bude wajen ajiyar ta kwashe dubu uku tasan zai isheta kudin mota har da rara,ranar kuma an daura auren Shehu da Amaryarsa Landlady kayan daki na gayu da tsada Landlady ta zuba a gidan kana gani kasan ba karya,a ranar da yamma Kuma ta tare ba kowa a gidan sai Raudah Wanda ma har Affan yazo Daukanta zasu tafi gida sai ga Nusaiba da Kaya niki niki a Ghana must go ta dawo. Affan ya dau wankan sugar yana tsaye a jikin mota yana jiran Raudansa Nusaiba sai kallonsa takeyi har da goge Fuska ko zai kyasa yace Yana sonta,Jakarta ta rike a hannu a Dan gayence Wai Kar ta kwafsa,zata wuce ta gaban Affan tace sannu lokacin Rauda ta fito taji Nusaiba tana cewa bawan Allah wani gidan kake nema ne? Affan ya kalleta sama da kasa yace ke lafiya Ina ruwanki dani karki jawo min matata yau ta hanani bacci mijin tace ne ni nan da kika ganni bani da amfani wajen Yan matan waje gwara kija tsummar ratuwarki ki Kara gaba gwandala ta baza kici ba,Nusaiba dariya tayi irin ta samu Hanya tace hmm amma matar taka ta birgeni haka ake son mace,Affan yace ae ai ta Isa ne kin san wasu ai basu Kai su mallaki miji ba sabo da Basu iya allonsu ba basu da hali na gari shi yasa ake yawan sakin Mata basu iya Zama da miji ba,Nusaiba sai taji Kamar da ita yake,yace Amaryar Shehu Muka kawo ai Shehu yayi dacen mace yanzu zai samu kwanciyar hankali ance uwar gidansa ballagaza ce ita da yarta Basu San me suke ba ance ma ko a unguwa an tsane su,Nusaiba Kamar ta fashe da kuka bawan Allah ya tsaya sai caba Mata magana yake,ita bata San ma Affan bai San ko Shehun ba sai dazu ya ganshi Suka gaisa labari Suka ji a layin ana fada, Raudah ce ta karaso tana hararar Nusaiba ko kunya Raudah babu akan kishi ganin layin ba kowa sai iya su harda shafa gemun Affan ana Masa shagwaba tace muje ta juyo ta kalli Nusaiba tana Mata up and down,Affan yace baiwar Allah ko Zaki Mana wanke
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71