Skip to content

Chapter 27

Chapter 27

AURENMU Book One Complete Hausa Novel 1,226 words 0 views Progress saved
Download Book

ta sake haihuwa ta yarda aka sa sunan Babar Shehu Asmau ai Kuwa tace Husna Kawai ita fa ta waye Kuma baza ta boye ba ai ba uwarta bace haka ta Haifi yaranta karshe ma Shehu Yana son haihuwa tace ta gama tayi planing shike nan ta tsaya da haihuwa abinta, gaba Daya tafi karfin Shehu ya rasa inda zaiyi da ita,wulakanci iri iri,da kudinsa Shehu zai siyi abinci amma idan ta dafa ta hanashi sannan yaranta kadai zata bawa Kuma Suma kadan sai ta siyar da sauran taci tsire da kudin, idan taga dama zagin Shehu ma takeyi shi Kuma Shehu hakuri yake da ita Kawai Sabo da yaranta,duk sabo da yaran data tara yake kyaleta sabo da idan ya koreta ma ya zaiyi da yaransa sannan rashin uwa a zamanin nan ba karamin matsala bane ga Yara shi yasa Kawai yake hakuri,akwai Sanda ma idan Suka Yi fada to da wuri zata rufe gidan idan Shehu ya fita masallaci Sallar Isha ya Sha kwana a masallaci Ita Kuma bata ganin hakurinsa haka tunaninta Kawai Dan ta Isa ne ko masifarta ce tasa,ya rasa ya zaiyi da ita Kawai ya daina bata ficika Kuma ya daina bata abinci Wai ko zata Yi hankali,wannan talaucin yasa Mama tayi laushi ita da Nusaiba Kawai ta ya zasu ci su koshi suke yi amma gashi Aslam Yana zuwa Suka samu kudi sai wulakanci Kuma Wanda yafi na baya ma,gidanta Kuma da Shehu yace ya siyar ba siyarwa yayi ba gani yayi akan Addua yarta ta bace zata siyar da gidanta yaji tsoro ne Kar ta koma bin bokaye abin bazai Yi da kyau ba shi yasa yayi Mata wayo ya nuna ya siyar da shi,duk wani zalunci sau tari ba zakuntarta yake Yi ba Yana yi ne sabo da nemawa Kansa sauki sai gashi dai karshe sai da ta kaishi ga zaluntar yaransa da matar ma tunda ya hanasu abinci Wanda hakkinsa ne,ita Kuma Nusaiba tun tana karama zuwa tasha talla da yawan rike kudi shi ya jawo idonta ya bude da kudi da shegen son kudi Idan kaci kayan me talla ka hanata kudi zaka ga rashin mutunci shi yasa takewa Aslam haka ta Saba fada da maza a wajen talla dama mafadaciya ce Kawai dai ita ba Yar iska bace bata bari a kawo Mata iskanci amma talla Yana daya daga cikin abinda ya jawo Nusaiba tafi karfin kowa bata tsoron kowa komai girman mutum ga Kuma gadon su na uwa wajen rashin mutunci da rashin sanin ya kamata,Mama sabo da rashin karatunta shi yasa Bata damu da ilimin yaranta ba. Nusaiba wankan tarwada ce Kuma ba laifi tana da kyanta dai dai gwargwado baza ace Mata mummuna ba,itama doguwa ce sai dai siririya ce amma ba can ba sannan tana da shape dinta dai dai ita Kuma dama Indai ta samu Kayan kwalliya to Yar kwalliya ce sabanin Siyama da tun tana karama bata kwalliya ita sai dai ta sa Riga da wando Bata taba saka skert ko zani kullum da Riga da wando har ta girma take zuwa wajen gwanjo ta zabo kala kala masu Fadi manya manya hakan yasa aka sa Mata suna Charity tace Begins at home taji ta karba shike Nan sunan ya bita Indai baka ce Siyama Charity ba Babu me ganeta ko kace Siyama sai ance wacce? Sai kace Charity sannan za a gane. Charity saka Riga da wandonta ya jawo Mata bata samari da yawa sai dai dai kadan amma Nusaiba Kuwa Allah ya bata kowa sonta yake sabo da Yar kwalliyarta,Kuma Charity gata kyakyawa Fara amma Riga da wando yasa ba a zuwa ma wasu ma zaton su Yar Igbo ce in ka ganta haka,Nusaiba Kuwa iyayinta kadai da gwalli Yana jawo Mata samari amma bata taba samun me kudi ba sai Aslam shi yasa Kawai ta aure shi Dan kudin ita Indai Namiji me kyau ne baya birgeta tafi son kudi duk kyansa bata bukata Siyama Kuwa Samarinta Basu da yawa amma duk na kirki ne masu sonta tsakani da Allah Kuma masu rufin asiri ne kowanne ba na banza lokacin bata son zancen ma aure harkarta takeyi tunda Dangin Hunaif Suka Mata sharrin Yar lesbian ce ta daina kula kowanne Namiji harkarta Kawai takeyi,kowa kallon wata Yar duniya yakewa Siyama ana yiwa Nusaiba kallon mutuniyar kirki,Haka Kawai ma Siyama bata Yi komai ba za a dinga Mata kazafi a layin ana gulmarta musamman samarin layin sun sata a gaba. wannan kenan Yau Affan yayi Niyyar zuwa gidan su Siyama,Liman ya bashi number Dauda kawun Siyama yace idan yaje ya Kira shine kawun Yarinyar, Affan wata sabuwar Shadda ya bare gal dinki me kyau na manyan samari masu tashe da ji da kansu, Yana furta Siyama...Wai Siyama yo ai naga Sima ma karewa, shiri ya Fara ya sa wani short tight ya matse shi sosai ya kalli Kansa yace yawwa Yana kallon Sandar girma wacce ya matse ta da wando yace ke sarkin rashin hakuri baza ki kunyatani ba ke sarkin son aiki ke dai ayi aiki ko to Kuwa baza ki samu ba kije kisa naji kunya a wajen yarinya yanzu kuwa da na matse ki ai ko motsi bakya Yi ba sarkin aiki lokaci baiyi ba ki Kara hakuri,Boxers ya sake dorawa a Kai sannan yasa wandon shaddarsa ya shafa turaruka kala kala sannan ya saka rigar shaddar wata ita ba milk ba ita arsh ba haka take,hula ya dakko a ledarta sabuwa Kalar shaddar ya feshe hular da turare me kamshi sannan ya sake taje sumarsa tare da wani dan dasa hular a gaban goshi yanda samarin zamani ke yi, Suma gata Nan a baya da yawa tari guda,sajensa zuwa gemunsa ya gyara ya shafa musu Mai me kamshi da spray dinsu ya feshe ya fesawa shaddar Kalar na kaya,sabon takalmi ya dakko shima jaraba kalar shaddar sabo da shi ya zura a kafarsa na Yan gayu yayi bala'in kyau abinka da me kyau da haske domin shi Affan Kalar skin dinsa Kalar ta Yan Latin ce Kamar irin Dan Brazil haka skin dinsa take,hancinsa dogo ne babu wacce zata ganshi ace bai birge ta ba, Fitowa yayi tare da kulle part dinsa ya juyo Yana waya da Abokinsa Sayyeed dan kd yace Ina Kano na kusa karasowa gidanka nan da 30mnt,Affan yace Zan bar maka key a wajen wata idan kazo gidan kace wace Raudat zata baka key sai ka bude ka shiga kafin na dawo,Sayyeed ya amsa da to an gama Yana kashe wayar ya dago Suka Yi Ido biyu da Raudat ta dawo daga wajen aiki ta gaji sosai yau sunyi meeting ogansu yaci mutuncinsu ya bata Mata rai,Amma tana ganin Affan komai ya canja ta manta da bacin ranta gaba Daya farin ciki ya kamata Bata taba ganin ya Mata kyau ba irin yau kallonta yake yi bata sani ba botin din rigarta ya bude daga kirji ana hango shatin boobs dinta,tana aikin kallonsa shi Kuma Yana kallon kirjinta sai kace maye har sai da ta lura tayi maza ta gyara mayafinta da sauri ya dauke Kai kamar bai gani ba ya basar yace Hajiya Aunty Sannu dan Allah ga key dina ki ajiye a wajenki abokina zaizo zai karba a wajenki karki

Table of Contents

Chapters

71 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71