Chapter 62
Chapter 62
wanke da shara a dauke ki aiki kin tsaya kin zuba Mana Ido, Raudah tace ai wallahi gwara aiki ya kashe Ni idan ba namiji zaka dauka ba Indai macece bana so zanyi komai da kaina,Nusaiba juyawa tayi tana tuna rayuwarta a gidan Aslam,da kyawun Aslam da yanda yake nuna Mata so da kauna,kuka ta saki tana tafiya kasa shiga gidansu tayi ta zauna a kofar gida bakin kofar su tana ta kuka,tausayi ta bawa Raudah taje wajenta tace baiwar Allah kuyi hakuri wlh bamu fada dan mu wulakantaki ba mun San darajar dan Adam kune bakwa kau da kai ga mazajen wasu kiyi hakuri idan abinda mijina yace ya Miki zafi,Nusaiba tace ba wannan ne ya dameni ba,nadama nayi a rayuwata na tafka kuskure,to Allah ya Mana me kyau cewar Raudah tana juyawa motocin Aslam biyu Suka Yi parking daya motar securities ne daya kuma shine a bayan motar tare da Siyama,Fitowa yayi a hankali wanka iya wanka ga kyau,zagawa yayi tare da budewa Siyama mota ya riko hannunta ta fito da dan karamin cikinta a gaba ya Fara Fitowa ta Sha Abaya ta zuba kyau Kamar ba Yar kasar nan ba,sunyi kiba da kyau sun Kara wani fresh,da gani kasan sun dan huta a kasar waje, Nusaiba ta bisu da kallo kawai,Aslam Yana ganin Affan ya koma gaban Siyama ya kareta Wai Kar ya ganta tsohuwar budurwarsa Kar so ya dawo sabo,Affan dariya abin ya bashi,ke Kuma Raudah da kin ga mace sai boye Miji a tsiri nunawa lallai ita fa matarsa ce,Aslam zai wuce tsabar kishi harda nunawa bai San Affan ba,Affan ya Mika Masa Hannu da kyar ya karba Suka gaisa Siyama ta dawo gaba tace Affan kaine a unguwar tamu,yace Amarya Muka kawowa Alhaji Shehu kawar matata ce,Siyama ta kalli Raudah tace Sannu Ina yini,Aslam harda Jin haushi dan me zata gaisar da Raudah ai Raudah ce ta kamata ta gaida Siyama,Raudah ta amsa da fara'a Suka gaisa ta gaida Aslam ya amsa,Affan yace Nasha Kaye a wajenka mene abin bata rai,tunda ka lashe zabe Kai fa kace ba gaba,Murmushi Aslam yayi ba shiri ya dai tsaya sun gaisa sosai harda bawa Affan katinsa yace gashi idan kana so Watarana mu gaisa,Affan ma ya zaro katinsa yace ga nawa Wai ya nunawa Aslam shima fa babban yaro ne da aikin yinsa,Raudah sai kallon cikin Siyama takeyi dama itama ta samu nata da Affan,gidan su Siyama zasu shiga Wanda dole sai ka wuce ta kofar gidan su Nusaiba,Nusaiba tana tsaye tana ta faman kallon Aslam Kamar mayya,Aslam ya gane itace harda shafa cikin Siyama suna tafiya,Siyama tayi dariya tace dan Allah ka kyale babyn nan haka kullum hannunka na kai,Siyama tace Nusaiba kece dama ko magana haba Nusaiba,Nusaiba an sakko tace Charity sannunki tana tabe baki ,Hannun charity ya rike Suka Shiga gida me kyau Nusaiba bata gane gidan su Siyama bane yanda Kawu ya gyara gidan yayi kyau ya canja sosai,haka ta Shige gidansu ta iske kannenta duk basa nan sun tafi sashen amarya,Shehu Yana dakinsa yaji sallamarta,Fitowa yayi yaga Nusaiba a gabansa ta zube gudun Kar ya koreta ta fashe da kuka ta rike kafar Shehu tana dan Allah Abba ka yafe min na tuba wlh bazan sake biyewa Mama ba,Shehu yace Nusaiba ki ma biye Mata ni ba ruwana kece a wahale,Ka yafe min Abba yace dama ni bana Fushi dake na yafe Miki, Yar da na Haifa ai kullum Addua Zan Miki Allah ya shiryeki ,Nusaiba taji Dadi sai ta share waje ta samu wajen Zama duk da haka bata leka wajen Amarya ba abinci taci duk Yan uwan Shehu sun tafi itace ta gyara gidan tsaf tare da kannenta tayi wanka,Shehu Kuwa ana yin Sallar Isha ya wuce bangaren Amarya landlady anci gayu ta hade cikin rigar baccinta pink ta Sha kyau na musamman,Shehu duk an gigice anga sabon jini,kajin da ya siya Mata sai da ya siyawa yaransa ya basu nasu na Amarya Kuma daban,Nusaiba yaushe rabon da taga nama tana Kauye sai yanzu,kannenta su Ameer sai dariya suke kyalkyala mata. Landlady wayayya ce wacce tasan ta Kan maza ga iya shagwaba da kisisina Shehu tun a wajen kwanciyar aure yasan sai yanzu yayi aure da haukarsa Kawai yake yi,washe gari kasa Fitowa yayi ko kafar gida Yana ta soyayya, Landlady girkinta tayi Nusaiba itace tayi nasu girkin ita da kannenta,da yamma Kuwa sai ga Shehu a kitchen ya ajiye hula a gefe Yana taya amarya wanke wanke,Yana gamawa yazo Yana yanka Mata Alayyahu,yau ma Shehu kwanan farin ciki yayi sun gurji juna shi da Landlady gaba daya Shehu ya susuce ya samu mace Yar gyara wacce tasan kanta,Satin Landlady daya ta Fara girki da su Nusaiba duk da haka Nusaiba bata taba shiga gidan ba sai da ta gaji taga kannenta sai shatara ta arziki Aunty Amarya take musu amma banda ita,haka da Yamma tayi wanka ta shirya ta Shiga bangaren Amarya a ranta tace gaskiya Aslam bashi da mutunci mutumin nan ba karamin makiri bane shine yayiwa Amarya wannan mu Kuma ko oho Nusaiba harda goge kwalla ta shiga Palo ac da kamshi Kawai ke tashi,Abbansu taji a kitchen suna ta Wasa da dariya da Amarya suna girki a hankali tayi Sanda Kamar barauniya ta leka kitchen din ta hango Landlady akan cinyar Shehu suna kissing,da sauri ta dawo baya tana rufe Ido ta zauna tana mamaki tace oh duniya ashe Abba dan duniya ne haka,Amarya ce tace naji Kamar yarmu na sallama ta mike ta fito tasan Nusaiba a hoto,Nusaiba tana ganin Amarya shegu kudi ba karya sai ta Mata kwarjini har kasa ta rusuna tace Ina yini Aunty,Aunty ta amsa da fara'a tace sai yau Zaki zo min kema kishi kike taya mamanki ko banga laifinki ba,Nusaiba mayyar masu kudi tace ba haka bane tana sadda Kai Kamar ba Nusaiba ba ,Shehu ne ya fito,Nusaiba tace Sannu Abba tana Zama a kujera ya amsa da fara'a sai rawar kafa yake sabo da anzo gaida Amaryarsa,bedroom ya shige Landlady tace Nusaiba jeki kular min da abincin can bari naje,Nusaiba ta Shige kitchen Itakuma Amarya ta wuce ciki tare da Shehu suna soyewarsu aka bar Nusaiba da aiki,Wasa Wasa sai gashi Amarya bata aikin kirki a gidan nan gaba Daya kusan Nusaiba ce ta Zama Yar boyi boyi ita take Kai kanta tayi ta dirzar aiki ba tare da an sakata ba sabo da Landlady tana da kudi. AsmaBaffa [4/1, 5:47 AM] Sis Asma: 🛢️AUREN MU🛢️ 96-98 Official By AsmaBaffa Page naki ne FUTURE RM Nusaiba gajiya tayi da rashin mahaifiyarsu ta tattara kannenta suka koma gaban Abbansu tare da durkusawa,Shehu yace Yaya aka Yi ne? Nusaiba tace zuwa Muka Yi mu roke ka dan Allah Abba ka dawo da Mama gida badan halinta ba ko don mu,Amarya Landlady tana ji,Shehu yace babu ruwanku Kar na sake ji Kun min maganarta Indai maganarta Zaku kawo min to karku zo inda nake,ku tashi ku bani waje ya musu tsawa suka mike sum sum Suka bar wajen,Nusaiba babu abinda take da buri face ta samu mijjn aure ko ba me kudi ba amma ta rasa me sonta yanzu duk irin farin jininta yanzu babu ko wani ya fara tunanin zuwa a unguwar za a fada Masa gaskiya halin Nusaiba da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71